Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [1]
Published: 9th, March 2025 GMT
SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1 BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 1
Sharhi:
Shehun malami Ibnu Juzai (Allah ya yi masa rahama) yana bayani a nan game da ma’anar Tafsiri, wanda ke nufin fassara da ƙarin bayani kan ma’anonin ayoyin Alƙur’ani. A bisa wannan magana, ana iya fahimtar cewa:
1. Tafsiri yana nufin bayani da sharhi na Alƙur’ani – Wato fassara da bayanin ma’anar ayoyi domin su fi zama a fili ga masu karatu da sauraro, don su fahimci saƙon da ke cikinsu.
2. Tafsiri yana bayyana ma’anar ayoyi dalla-dalla – Manufarsa ita ce kawar da ruɗani da kuma hana kuskuren fahimta.
3. Hanyoyin bayani a tafsiri suna da matakai daban-daban:
Ta lafazin ayar kai tsaye (بِنَصِّهِ) – Wato bayani a fili kamar yadda ayar take, ba tare da ƙarin sharhi ba.
Ta hanyar alama da ishara (إِشَارَتِهِ) – Wato fahimtar ma’anar da ke ƙunshe a tsarin ayar, sigar kalmomi, ko wasu dalilan shari’a da suke cikinta.
Ta fahimtar abin da ayar ke iya nufi (مُحْتَمَلِهِ) – Wannan yana buƙatar zurfin nazari, domin fahimtar ma’anar da za a iya ɗaukowa daga ayar bisa dalilai masu goyon baya.
Daga wannan bayani, ana iya fahimta cewa tafsiri ba wai kawai fassara ne kai tsaye ba, har da zurfafa fahimta ta hanyoyi daban-daban, tare da la’akari da sauran dalilan shari’a. Wannan yana taimakawa wajen fahimtar saƙon da Allah yake isarwa ta cikin Alƙur’ani cikin ingantacciyar hanya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye
Kungiyar gwagwarmaya ta Hamas ta yi Allah wadai da sabbin gine-ginen mastugunnan yahudawa yan share wuri zauna guda 764 da isra’ila take ginawa a gabar yammacin kogin jodan , kuma ta bayyana shi a matsayin wani shiri na mayar da yankin ya koma na yahudawa.
Wannan matakin yana nuna irin yadda isra’ila ta ke ci gaba da fadada gine-ginenta a yankun da aka dauki dogon lokaci ana takaddama akai, kuma babbar barazana ce ga yankunan dake ciki yankunan falasdinawa a gabar yammacin kogin Jodan,
Siyasar ci gaba da Gine gine na isra’ila ya kara sauri a yan shekarun nan duk da nuna rashin amincewa da kwamitin tsaro na majalisar dinkin duniya ya nuna, kuma ya bukaci ta dakatar da dukkan gine-ginen da take yi domin ya sabama dokokin kasa da kasa,
Kungiyoyin falasdinawa sun yi gargadin cewa ci gaba da kwace filaye da nufin samar da cikakken iko ga Isra’ila da kuma korar yan asalin kasar,
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Tana Daukar Bakwancin Taron BRICS Na Binciken Kimiya Da Kuma Ci Gaban Ilmi December 10, 2025 Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya December 10, 2025 ‘Yan Ta’adda Sun Kai Hare-Hare Kan Sojojin Pakistan Sun Kuma Kashe 6 Daga Cikinsu December 10, 2025 Najeriya: Majalisar Dattawa Ta Bawa Tunubu Damar Kai Sojoji Zuwa Kasar Benin December 10, 2025 Ministan Makamashi: Iran Tana Da Sanayya Ta Ilimi Na Samar Da Hadari Domin Yin Ruwan Sama December 10, 2025 Kasar China Ta Zartar Da Hukuncin Kisa Akan Wani Babban Jami’in Banki December 10, 2025 Ganawa A Tsakanin Mataimakan Ministocin Waje Na Kasashen Saudiyya, China Da Minista Arakci Na Iran December 10, 2025 Antoni Gutress Ya Yi Allawadai Da Kutsen Da “Isra’ila” Ta Yi A Cibiyar Unrwa December 10, 2025 Iran da Saudiyya sun sake jaddada fadada dangantakarsu December 9, 2025 Faransa ta ce da hannunta aka dakile juyin mulki a Benin December 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci