Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [1]
Published: 9th, March 2025 GMT
SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1 BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 1
Sharhi:
Shehun malami Ibnu Juzai (Allah ya yi masa rahama) yana bayani a nan game da ma’anar Tafsiri, wanda ke nufin fassara da ƙarin bayani kan ma’anonin ayoyin Alƙur’ani. A bisa wannan magana, ana iya fahimtar cewa:
1. Tafsiri yana nufin bayani da sharhi na Alƙur’ani – Wato fassara da bayanin ma’anar ayoyi domin su fi zama a fili ga masu karatu da sauraro, don su fahimci saƙon da ke cikinsu.
2. Tafsiri yana bayyana ma’anar ayoyi dalla-dalla – Manufarsa ita ce kawar da ruɗani da kuma hana kuskuren fahimta.
3. Hanyoyin bayani a tafsiri suna da matakai daban-daban:
Ta lafazin ayar kai tsaye (بِنَصِّهِ) – Wato bayani a fili kamar yadda ayar take, ba tare da ƙarin sharhi ba.
Ta hanyar alama da ishara (إِشَارَتِهِ) – Wato fahimtar ma’anar da ke ƙunshe a tsarin ayar, sigar kalmomi, ko wasu dalilan shari’a da suke cikinta.
Ta fahimtar abin da ayar ke iya nufi (مُحْتَمَلِهِ) – Wannan yana buƙatar zurfin nazari, domin fahimtar ma’anar da za a iya ɗaukowa daga ayar bisa dalilai masu goyon baya.
Daga wannan bayani, ana iya fahimta cewa tafsiri ba wai kawai fassara ne kai tsaye ba, har da zurfafa fahimta ta hanyoyi daban-daban, tare da la’akari da sauran dalilan shari’a. Wannan yana taimakawa wajen fahimtar saƙon da Allah yake isarwa ta cikin Alƙur’ani cikin ingantacciyar hanya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki
এছাড়াও পড়ুন:
Mutum biyu sun mutu a harbin bindiga a Jami’ar Brown ta Amurka
Jami’ar Brown a Amurka ta ba da rahoton mutuwar mutum biyu, tare da jikkatar guda tara dake cikin tsanani a harbin da aka yi a makarantar.
An ruwaito cewa mutane da yawa sun jikkata a harbin da aka yi kusa da harabar Ivy League da ke Rhode Island.
Hukumomi yankin sun bukaci jama’a da su ci gaba da kasancewa a kulle yayin da maharin ya tsere.
“Zan iya tabbatar da cewa akwai mutane biyu da suka mutu da yammacin yau, kuma akwai wasu mutane takwas da ke cikin mawuyacin hali, kodayake basu cikin damuwa sosai,” in ji Magajin Garin Brett Smiley, a wani taron manema labarai.
“Muna amfani da duk wata hanya da za mu iya don gano maharin in ji Mataimakin Shugaban ‘Yan Sanda Timothy O’Hara.
Wannan harbin shi ne na baya-bayan nan a cikin jerin hare-haren makarantu a Amurka, inda yunkurin takaita damar malllakar makamai cikin sauki ke fuskantar kalubalen siyasa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugabannin kasashen (ECOWAS) na taro a Abuja December 14, 2025 Kasashen AES zasu kafa bankin dogaro da kai December 14, 2025 Sheikh Na’im Kassim: Idan Duniya Baki Daya Za Ta Taru, Ba Wanda Zai Iya Kwace Makaman Hizbullah December 13, 2025 DRC: Kungiyar M23 Ta Kwace Iko Da Wani Gari Mai Muhimmanci December 13, 2025 Syria: Sojojin “Isra’ila” Sun Kutsa Cikin Yankin Qunaidhara December 13, 2025 Kalibaf: Iran Da Habasha Suna Bunkasa Alakokin Siyasa Da Tattalin Arziki December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 171 December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 170 December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 169 December 13, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Kudancin Labanon A Ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta December 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci