Leadership News Hausa:
2025-03-16@00:12:46 GMT

Adadin Mata Mamallaka Sana’o’i Na Ta Karuwa A Kasar Sin

Published: 8th, March 2025 GMT

Adadin Mata Mamallaka Sana’o’i Na Ta Karuwa A Kasar Sin

Yanzu haka adadin matan kasar Sin mamallaka sana’o’i na ta karuwa sannu a hankali, inda ya zuwa yanzu mata ke taka muhimmiyar rawa wajen samar da ci gaba mai inganci a kasar.

Wasu alkaluma daga hukumar lura da hada hadar kasuwanni ta kasar sun nuna cewa, ya zuwa karshen shekarar bara, adadin kamfanoni da matan kasar Sin suka zuba jari sun haura miliyan 23, adadin da ya kai kaso 41.

6 bisa dari cikin jimillar kamfanonin kasar masu zaman kan su.

Alkaluman sun nuna adadin hada-hadar kamfanoni masu jarin matan kasar Sin na ta karuwa, da kimanin kaso 9.8 bisa dari a duk shekara tun daga shekarar 2012, a gabar da karin mata ke kafawa, da zuba jari a kamfanoni daban daban. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Wata mata ta faɗa ruwa ta mutu a Legas

An tabbatar da mutuwar wata mata da har yanzu ba a bayyana sunan ta ba bayan ta yi tsalle ta faɗa kogin Legas daga gadar Third Mainland a Jihar Legas.

Majiyar PUNCH ta ruwaito hakan ne daga wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Legas, Benjamin Hundeyin ya fitar a ranar Juma’a cewa lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 4 na yamma kusa da bakin ruwan kogin da ke hanyar jami’ar Legas.

Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo Lakurawa: Gwamnan Kebbi ya nemi a kafa sansanin soji a jihar

“Tawagar ’yan sandan ruwa da ke aiki a wurin sun gano ta gaɓar ruwan da ke hanyar jami’ar Legas kuma likitocin jami’ar UNILAG sun tabbatar da mutuwarta a gaban rundunar  ’yan sanda daga sashin Sabo,” kamar yadda sanarwar a wani ɓangare ta bayyana.

Hundeyin ya ci gaba da cewa, an kai gawar zuwa ɗakin ajiye gawarwaki na Asibitin cututtuka masu yaɗuwa da ke yankin Yaba a jihar domin adanawa.

Ya ƙara da cewa “Yan sanda a halin yanzu suna binciken al’amuran da suka shafi mutuwar matar.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon Firaministan Lebanon: Rashin Fahimta Da Shakku Daga Waje Ba Za Su Iya Dakatar Da Ci Gaban Kasar Sin Ba
  • Nageriya ta Maida Martani Kan Zargin Kissin Kiristoce A Kasar,Wanada Gwamnatin Amurka Ta Yi Mata
  • Birnin Beijing Ya Shirya Yiwa ‘Yan Mata Rigakafin Cutar HPV Kyauta
  • Wata mata ta faɗa ruwa ta mutu a Legas
  • Yadda Nijeriya Ta Zarce Yawan Man Da OPEC Ta Ware Mata – Bincike
  • Sama da ‘Yan Mata 74,000 Suka Amfana Shirin AGILE Cash A Kano
  • Ranar Mata Ta Duniya: Kalubalen Da Mata Ke Fuskanta A Siyasar Nijeriya
  • Somalia: Adadin wadanda suka mutu a harin Al-Shabaab ya haura 10
  • Fiye Da Yara Mata 74,000 Sun Amfana Da Shirin Tallafin Kudi Na AGILE A Kano
  • Uwargidan Tinubu Ta Bai Wa Mata Manoma Tallafin Naira Miliyan 26 A Nasarawa