Adadin Mata Mamallaka Sana’o’i Na Ta Karuwa A Kasar Sin
Published: 8th, March 2025 GMT
Yanzu haka adadin matan kasar Sin mamallaka sana’o’i na ta karuwa sannu a hankali, inda ya zuwa yanzu mata ke taka muhimmiyar rawa wajen samar da ci gaba mai inganci a kasar.
Wasu alkaluma daga hukumar lura da hada hadar kasuwanni ta kasar sun nuna cewa, ya zuwa karshen shekarar bara, adadin kamfanoni da matan kasar Sin suka zuba jari sun haura miliyan 23, adadin da ya kai kaso 41.
Alkaluman sun nuna adadin hada-hadar kamfanoni masu jarin matan kasar Sin na ta karuwa, da kimanin kaso 9.8 bisa dari a duk shekara tun daga shekarar 2012, a gabar da karin mata ke kafawa, da zuba jari a kamfanoni daban daban. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Aragchi: Amurka Tana Iya Farfado Da Tattaunawa Kan Shirin Makamashin Nukliyar Kasar Idan Tanaso
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa tattaunawa tsakanin Amurka da JMI sun lalace ne saboda zagon kasar HKI da farwa kasar da yaki. Yace gwamnatin Amurka idan tana so zata farfado da shi.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a wani rubutun da yi wa jaridar ‘Financial Times ta Amurka. Inda y ace : Har yanzun JMI tana bukatar hanyar Diblomasiyya, amma kuma hakkinta ne mu yi shakku a kan ninyar Amurka niyyar Amurka a tattaunawa da ita. Idan Amurka da gaske take ta nuna cewa ta warware wannan matsalar to tana iya yin haka da adalci.
Sai dai, inji ministan, yakamata Amurka ta san cewa al-amura sun sauya kuma bayan wannan yaki na kwanaki 12 da HKI da ita suka kaiwa cibiyoyin makamashin nukliyar har guda uku ta kuma kashe manya-manyan Janaral na sojojinmmu sannan ta kashe masana fasahar nukliyammu da kuma wasu Iraniyawa.
Aragchi ya ce: Iran ba zata mika kai kamar yadda Amurka take riyawa ba. Iran kasashe wacce tayi shekaru dubbai a duniya, kuma ta kutsa yake-yake da dama a baya ta kuma sami nasara. Sannan yace: Muna son zaman lafiya a ko yauce, amma mune muke iya tabbatar da ita ko mu hanata tabbata.
Yace: A halin yanzun kuma ba zamu taba amincewa da kissam mutanemmu ba.