Aminiya:
2025-11-03@07:35:11 GMT

NRC ta dakatar da jigilar jirgin ƙasan Kaduna zuwa Abuja

Published: 26th, August 2025 GMT

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen ƙasa ta Nijeriya (NRC) ta dakatar da sufurin jirgin ƙasan da ke jigila a tsakanin Abuja zuwa Kaduna.

NRC ta sanar da ɗaukar wannan matakin ne har sai an kammala bincike kan hatsarin jirgin da ya auku a wannan Talatar.

An yi kiciɓus da gawar ’yar shekara 14 a cikin gida a Kano Hisbah ta haramta al’adun gargajiya yayin bukukuwan aure a Bauchi

Shugaban hukumar, Kayode Opeifa, ne ya sanar da haka jim kaɗan bayan faruwar lamarin.

Ya bayyana cewa tuni tawagar masu bincike da suka haɗa da ma’aikatan NRC, hukumar binciken sufuri ta ƙasa (NSIB) da sauran hukumomin tsaro, sun isa wurin domin gudanar da bincike.

Opeifa ya yi watsi da maganganun da ake yi cewa jiragen ba su da inganci, yana mai cewa an fara mayar da kuɗin tikiti ga dukkan fasinjojin da abin ya shafa.

Ya ƙara da cewa hukumar ta karɓi fasinjojin da aka sauke a tashar Asham da kuma tashar Idu a Abuja, tare da tabbatar da cewa za a sanar da jama’a duk wani sabon mataki na gaba.

Aminiya ta ruwaito cewa a safiyar wannan Talatar ce jirgin ƙasan ɗauke da fasinjoji da ya taso daga babban birnin Najeriya zuwa Kaduna ya tuntsure yana tafe.

Rahotanni na cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11 na safe a ƙauyen Asham da ke hanyar Abuja zuwa Kaduna bayan tasowar jirgin ƙasan da misalin ƙarfe 9:45 daga Abuja.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jirgin Ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi

Fitaccen Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Gumi, ya shawarci Shugaba Bola Tinubu da ya ɗauki mataki mai tsauri a kan Shugaban Amurka, Donald Trump, game da barazanar da ya yi na amfani da ƙarfin soja a kan Najeriya.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Lahadi, malamin ya bayyana cewa irin wannan magana ta Trump cin mutunci ce ga ’yancin Najeriya.

Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka

Don haka malamin ya yi kira da a ɗauki matakin diflomasiyya cikin gaggawa.

“Trump ya yi barazana ga ƙasa mai cin gashin kanta da harin soja, wannan girmamawa ne ga ƙasarmu,” in ji Gumi.

Sheikh Gumi, ya nemi Gwamnatin Tarayya ta kira Jakadan Amurka domin neman bayani da kuma a janye wannan barazanar, inda ya yi gargaɗin cewa idan ba a yi haka ba, to Najeriya ta yanke hulɗa da Amurka.

“Shugaba Tinubu ya kamata ya kira Jakadan Amurka idan ba su janye barazanar ba, to mu yanke hulɗa da wannan gwamnati mara mutunci,” in ji shi.

Gumi, ya kuma jaddada cewa Najeriya tana da damar bunƙasa tattalin arziƙinta ba tare da dogaro da Amurka ba.

“Akwai hanyoyi da dama da za mu iya faɗaɗa tattalin arziƙinmu da ƙarfafa haɗin kan soji ba tare da dogaro da su ba,” in ji Gumi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda matata ta ɓace a Abuja aka tsince ta a Sakkwato
  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa