Aminiya:
2025-09-18@00:36:05 GMT

NRC ta dakatar da jigilar jirgin ƙasan Kaduna zuwa Abuja

Published: 26th, August 2025 GMT

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen ƙasa ta Nijeriya (NRC) ta dakatar da sufurin jirgin ƙasan da ke jigila a tsakanin Abuja zuwa Kaduna.

NRC ta sanar da ɗaukar wannan matakin ne har sai an kammala bincike kan hatsarin jirgin da ya auku a wannan Talatar.

An yi kiciɓus da gawar ’yar shekara 14 a cikin gida a Kano Hisbah ta haramta al’adun gargajiya yayin bukukuwan aure a Bauchi

Shugaban hukumar, Kayode Opeifa, ne ya sanar da haka jim kaɗan bayan faruwar lamarin.

Ya bayyana cewa tuni tawagar masu bincike da suka haɗa da ma’aikatan NRC, hukumar binciken sufuri ta ƙasa (NSIB) da sauran hukumomin tsaro, sun isa wurin domin gudanar da bincike.

Opeifa ya yi watsi da maganganun da ake yi cewa jiragen ba su da inganci, yana mai cewa an fara mayar da kuɗin tikiti ga dukkan fasinjojin da abin ya shafa.

Ya ƙara da cewa hukumar ta karɓi fasinjojin da aka sauke a tashar Asham da kuma tashar Idu a Abuja, tare da tabbatar da cewa za a sanar da jama’a duk wani sabon mataki na gaba.

Aminiya ta ruwaito cewa a safiyar wannan Talatar ce jirgin ƙasan ɗauke da fasinjoji da ya taso daga babban birnin Najeriya zuwa Kaduna ya tuntsure yana tafe.

Rahotanni na cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11 na safe a ƙauyen Asham da ke hanyar Abuja zuwa Kaduna bayan tasowar jirgin ƙasan da misalin ƙarfe 9:45 daga Abuja.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jirgin Ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da janye dokar ta-baci a Jihar Rivers daga ƙarfe 12 na daren 17 ga watan Satumban 2025.

Shugaban Ƙasar, a wata sanarwa da ya sanya wa hannu, ya ce dokar ta-bacin da ta dakatar da Gwamna, Mataimakiyarsa, da ‘yan majalisar dokokin jihar na tsawon watanni shida ta cimma manufarta na dawo da zaman lafiya a jihar.

Tinubu ya bayyana cewa ya yi amfani da Sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin 1999 ne a watan Maris na 2025 sakamakon durƙushewar mulki a Jihar Rivers.

A cewarsa, rashin jituwa tsakanin Gwamna Siminalayi Fubara da Majalisar Dokokin Jihar, da kuma lalata muhimman kadarorin gwamnati sun jefa jihar cikin rikici.

“Lamarin ya kai ga Babbar Kotun Ƙoli ta bayyana a ɗaya daga cikin hukuncinta cewa babu gwamnati a Jihar Rivers.” In ji Shugaban Ƙasa.

Ya gode wa Majalisar Ƙasa bisa amincewa da wannan sanarwa, tare da yabawa Sarakuna da jama’ar jihar bisa haɗin kan da suka bayar.

Tinubu ya kuma yaba wa  masu adawa da suka kalubalanci wannan mataki a kotu, yana cewa wannan shi ma wani ɓangare ne na dimokuraɗiyya.

Da yake magana kan sabuwar fahimta tsakanin manyan ‘yan siyasa a jihar, Shugaban Ƙasa ya ce babu dalilin ƙara tsawaita dokar ta-bacin.

Ya bayyana cewa Gwamna Siminalayi Fubara, da Mataimakiyarsa Ngozi Nma Odu, da Shugaban Majalisar Dokoki Martins Amaewhule da dukkan mambobin majalisar jihar za su koma bakin aiki daga 18 ga Satumban 2025.

Tinubu ya yi kira ga shugabannin siyasa a faɗin Najeriya da su ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai domin isar da fa’idodin dimokuraɗiyya ga al’umma.

 

Daga Bello Wakili

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Ma’aikatar Shari’ar Iran Ta Sanar Da Rataye Dan Leken Asirin Hukumar Mossad Ta Isra’ila
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila