Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na sharhin bayan labarai, wanda zai yi magana a kan “Yadda JMI Ta Bunkasa Sana’argine-gine da da kamfanoni tare da amfani da fasahar cikin gida’ wanda ni tahir amin zan karanta.

Tun bayan nasarar juyin juya halin musulunci a nan kasar Iran a shekara 1979, daya daga cikin bangarorin da aka sami gagarumin ci gaba a cikinsa shi ne, bunkasa sana’ar gine –gine da kuma samar da masana’antu, wanda ya kai ga kasar ta kai ga wadata a wannan bangaren, wani abu daga kasashen waje, sai abunda ba za’a rasaba.

Har’ila yau wannan ya wadanar da mutane da dama a kasar.

Kafin haka idan mun dubi kasar Iran kafin juyin juya halin musulunci a kasar, zamu ga cewa kusan duk wani al-amari ya shafi gine-gine na hanya gadoji asbito ci, da gidaje . Haka ma masana’antu sun dogara kacokap kan kasashen waje musamman Amurka.

A cikin rabin karni na 20TH bayan an sami arzikin man fetur a kasar Iran, ci bayan da kasar ta yi ya sa da dogara da kasashen waje musamman Amurka do samar da hanyoyi da layukan dogo da gadaje da madatsun ruwa da gine-ginen zamani a manya manyan biranen kasar. Muna iya cewa dukkan manya-manyan ayyuka kamfanonin kasashen waje ne suke gana su, ba’abinda ira niyawa zasu iya yi sai ayyukan karfi da wasu wadanda basu da muhimmanci sosai.

A tsakanin shekara 1960-70, kamfanonin Amurka ne suka mamaye mafi yawan ayyukan ginegine a kasar Iran. Sannan a lokacin yakin cacan baki Amurka ce da mamaye dukkan harkokin tsaron kasar Iran. Da kuma kamfanonin haka da sarrafa man fetur.

A lokacinda farashin danyen man fetur ya tashi Amurka ta yi kokarin ginin dukkan kudaden sun koma kasar Amurka. Barin talakawan Iran hannu banza, duk tare da kudaden da suka shiga hannun gwamnatin kasar.

Abubuwan da kwararru na cikin gida suka yi ya kara fallasa barnan da kamfanonin kasashen waje suka yi a kasar. Sannan takunkuman Amurka sun sanya wasu ayyukan ma gaba daya an daina su sabo kayakin aikin daga waje ake zuwa da su.

Don haka a cikin wannan halin kwararru na cikin gida suna kammala rukunin gidaje na Ecbatona a birnin Tehran wanda wani kamfanin amurka ya fara ginashi bai kare ba aka yi juyin juya hali ya bar aikin rabi da rabi.

Sannan bayan yaki na shekaru 8 gwamnatin Rafsanaja ta samar da shirin sake gina kasar wanda ya kawo sauyi mai yawa a bangaren gine-gine a ko wani bangaren a kasar. Wadanda suka hada da manya-manyan tituna rukunan gidaje, layukan dogo sabbin tasoshin jiragen sama da jiragen ruwa, madatsun ruwa da kayakin lantarku da sauransu.

Daga cikin matakan da sabuwar gwamnatin JMI ta dauka don warware matsalilin gidaje, a iran. Akwai basusuka masu sauki, kula da farashin kayaki, da rage farashin wasu kayaki musamman abinda don talaka ya samu, sannan rarraba filaye don gina gidaje da farashin mai rahusa.

Kodaitar da manya-manyan kamfanoni su karfafa kananan kamfanoni, ko daddaikun mutane da sauransu.

An yada shi’arin cewa , al-amuran kasar Iran ba zai sake komawa cikin hannun yan waje ba,.

Tare da wannan sai kamfanonin cikin gida suka kammala manya manyan ayyuka wadanda kamfanonin kasashen waje suka fara yi, basu karasa ba, sai suka fara sabbin gine-gine, wadanda suka sauya fuskar biranen Iran musamman a birnin Tehran.

Shekaru 46 da suka gabata, mafi yawan kasar Iran kauyuka ne, mafi yawan mutane suna rayuwa a kauyuka, amma a halin mafi yawan kasar Iran rayuwar birane suke, wanda ya tashi daga kashi 48 zuwa 77 %.

Daga lokaci zuwa yanzun an samar da birane kimani 1,300, daga 373 kacal kafin nasarar Juyin juya halin musulunci.

Kuma ana amfani da kayakin gini masu karfi ganin kasar tana fama da yawan girgizan kasa. Don haka a halin yanzu girgizan kasa mai ma’auninriche 5-7 ba zasu yi barna mai yawa ba, saboda ingancin gine gine.

Banda wannan Iran ta kai matsayinda a wasu bangarori ta shiga cikin kasashe 10 masu samar da misali ceminta da karafa a duniya. Sannan tana sayar da su ga kasashen waje. A bangare kayakin kawa sai kasar Chaina da indiya ce suke gabanta. Masu sauraro karshen sharhin bayan labaran Kenan.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a manya manyan kasashen waje

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu

Iran da Rasha sun tattauna kan inganta hadin gwiwar kafofin yada labarai da yaki da labaran karya

Jakadan kasar Iran a birnin Moscow Kazem Jalali ya gana da mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha Maria Zakharova a jiya Talata inda suka yi musayar ra’ayi kan bunkasa hadin gwiwar kafofin yada labarai.

Bangarorin biyu sun tattauna batutuwan baya-bayan nan da suka hada da yiwuwar gudanar da harkokin yada labarai, da nazarin yiwuwar bunkasa hadin gwiwar kafofin watsa labaru, da hanyoyin yin tasiri a kafofin watsa labaru, da matakan hadin gwiwa don kara fahimtar ra’ayin jama’a a kasashen biyu.

Bangarorin biyu sun yi tsokaci kan yadda kafafen yada labarai ke yada jita-jita da nufin yin zagon kasa ga dangantakar kasashen Iran da Rasha tare da tattauna hanyoyin yaki da labaran karya da yada labarai marasa tushe ko madogara.

A farkon taron, jakadan Iran ya yi tsokaci kan karairayi da kafafen yada labaran yammacin duniya ke yadawa, musamman Axios, dangane da alakar da ke tsakanin kasashen biyu, ya kuma mika godiyarsa ga ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha kan wannan batu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba July 30, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami July 30, 2025 Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci July 30, 2025 Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya July 29, 2025 Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon July 29, 2025 EU Tace Zata Dakatar Da HKI Daga Cibiyar Bincikenta Saboda Gaza July 29, 2025 Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar July 29, 2025 Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki July 29, 2025  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
  • Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
  • Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka
  • Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan