Aminiya:
2025-07-31@10:10:56 GMT

2027: Kwankwaso da Aregbesola sun gana kan makomar siyasar Najeriya

Published: 9th, February 2025 GMT

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya gana da tsohon ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, a birnin Legas.

Kwankwaso ya bayyana a shafinsa na X cewa sun tattauna kan batutuwan da suka shafi siyasa da makomar dimokuradiyya a Najeriya.

Aisha Binani ce ta lashe zaɓen Adamawa, ina da ƙwararan hujjoji – Ari Ɗan sanda ya rataye kansa har lahira a Neja

Wannan ganawa na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyun adawa ke kira ga haɗin kai domin fuskantar zaɓen 2027.

A watan Oktoban 2024, jam’iyyar APC a Jihar Osun ya dakatar da Aregbesola bisa zargin cin amanar jam’iyya da sukar shugabannin jam’iyyar, ciki har da Shugaba Bola Tinubu da tsohon gwamnan Osun, Bisi Akande.

Aregbesola, wanda ya kasance gwamnan Osun daga 2010 zuwa 2018, ya fuskanci rikici da magajinsa, Adegboyega Oyetola, tun bayan zaɓen 2018.

Wannan rikici ya haifar da rabuwar kai a cikin jam’iyyar APC a Osun, inda wasu magoya bayan Aregbesola suka kafa ƙungiyar Omoluabi Progressives, wanda jam’iyyar ta yi zargin cewa tana aiki ne a matsayin waniɓangare mai adawa da ita.

Duk da waɗannan ƙalubale, Aregbesola ya ci gaba da kasancewa mai faɗa a ji a siyasar Najeriya.

Ganawarsa da Kwankwaso na iya nuna yunƙurin ƙulla sabbin alaƙa da haɗin gwiwa tsakanin shugabannin siyasar domin inganta dimokuradiyya a Najeriya.

Har zuwa yanzu, ba a samu cikakken bayani kan abin da suka tattauna ba, amma ganawar ba za ta rasa nasaba da yunƙurin da wasu ke yi na haɗa kan ’yan adawa domin tunkarar babban zaben 2027.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Aregbesola dimokuradiyya Ganawa Kwankwaso Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Mata a Arewacin Najeriya na fuskantar kalubale da dama a fannin karantar kimiyya.

Akwai darussan da a mafi yawan lokuta ba mata kadai ba, har da mazan na kaurace musu.

NAJERIYA A YAU: Matakan Da Muke Dauka Don Karfafawa ’Yan Najeriya Kwarin Gwiwar Kada Kuri’a —INEC DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta

Shirin Najeriya a Yau ya yi nazari  ne kan dalilan da suka sa matan Arewacin Najeriya ke tsoron karantar ilimin kimiyya.

Domin sauke cikakken shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC
  • NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
  • Shugaban Ivory Coast Ouattara zai sake takara wa’adi na huɗu
  • Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Kungiyar Gwamnonin Jihohi Ta Jajintawa Jihar Adamawa Bisa Ambaliyar Ruwa A Yola