Aminiya:
2025-05-01@03:10:14 GMT

Me ya sa ake musayar yawu tsakanin APC da PDP?

Published: 9th, February 2025 GMT

Duk da cewa akwai sauran lokaci kafin babban zaben 2027, ana ci gaba da musayar yawu kan shirye-shiryen manyan ‘yan siyasa da ke hamayya da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, inda suke tarurruka tare da tuntuɓar juna kan yadda za su kayar da Jam’iyyar APC mai mulki a Zaɓen 2027.

Fadar Shugaban kasa ta mayar da martani kan kalaman da wasu daga cikin ‘ya’yan jam’iyyun adawa da na cikin gidanta suke yi, inda suka zarge ta da sauka daga kan turbar da jam’iyyar take.

Katsina ta zama cibiyar haɗin kan ƙabilun ƙasa a Arewa — Gwamna Radda Ta kashe saurayinta saboda ya gaisa da tsohuwar abokiyar karatunsa

Fadar Shugaban kasa na mayar da martani ne bayan wani taro da jagororin hamayya da wasu daga cikin ‘yan Jam’iyyar APC da ke adawa da gwamnatin suka gudanar a Abuja.

Jam’iyyar ta APC dai ta ce hakan ba komai ba ne illa yunƙurin da masu adawa da gwamnatin ta Bola Ahmed Tinubu ke yi na kawar da hankalin Tinubu daga hidimar da yake wa al’ummar kasar nan.

Sai dai Jam’iyyar adawa ta PDP ta ce, borin kunya ce gwamnatin APC ke yi, saboda manuniya ta nuna cewar al’ummar kasar nan sun gaji da mulkinta.

Malam Abdul’aziz Abdul’aziz na ɗaya daga cikin masu magana da yawun Shugaban kasar ya bayyana cewa, ganin irin rawar da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ke takawa wajen gyara kurakuran da Jam’iyyar PDP ta yi ne tsawon shekara 16 da suka ɗauka.

“Suna mulki ne ya sa suke kaɗa gangar siyasa tun kafin lokacin ya zo.

“Su wadanda suke irin wadannan zarge-zargen ai su ne mutanen da suke ɗauke hankalin gwamnati daga kan abin da ya kamata ta yi”, in ji Abdul’aziz.

Shi kuwa mataimakin mai magana da yawun Jam’iyyar PDP, Alhaji Ibrahim Abdullahi ya ce, martanin na fadar shugaban ba komai ba ne illa shure-shure da baya hana mutuwa, wanda duk ya iske shinkafa a Naira 6,000 da PDP ta faɗi zabe, yanzu kuma yake sayen shinkafar nan kan Naira 100,000, lallai akwai ayar tambaya da ake cewa wai ana gyara a cewar Ibrahim.

Fadar shugaban ta ce, taron da suka gudanar ba komai ba ne illa na wadanda ba sa fatan ci gaban kasar nan da kuma son tunzura al’umma da barazana da kuma bayyana ra’ayoyin da za su durƙusar da dimokuradiyya.

Jam’iyyun hamayya na fama da rikice-rikicen cikin gida, lamarin da masana kan harkokin siyasa ke bayyanawa da cewa zai iya kawo musu tarnaƙi wajen haɗewar da suke niyyar yi.

A shekarar 2023 ce dai Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu ya yi nasarar doke Alhaji Atiku Abubakar na Jam’iyyar PDP a Zaɓen Shugaban kasa, inda aka samu wasu gwamnonin PDP da ake zargin sun yi wa Jam’iyyar APC aiki.

Yanzu dai hankali ya karkata ne wajen ganin irin wainar da za a toya a babban taron Jam’iyyar PDP, wadda ke kan gaba a sahun jam’iyyun adawa.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jam iyyar PDP

এছাড়াও পড়ুন:

Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu

Tsoffin ma’aikatan Hukumar Shirya Jarabawar (NECO), da suka yi ritaya na neman a biya su haƙƙoƙinsu da suke bin bashi.

Shugaban ƙungiyar tsofffin ma’aikatan, Dokta Abdullahi Rotimi Williams ne ya bayyana hakan a bikin ƙaddamar da hedikwatar kungiyar a Minna, babban birnin Neja.

Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya

Shugaban ya kuma koka kan yadda gwamnatin Nijeriya ta maida ritaya abin fargaba a wurin ma’aikata saboda tarin ƙalubalen da ke biyo bayan hakan, musamman maƙalewar haƙƙoƙinsu.

“Da yawa tsoron ritaya ake yi yanzu. Don haka wannan ƙungiyar za ta taimaka wajen rage waɗannan matsalolin.

“Babban ƙalubalen da muke fuskanta shi ne na lafiya. Don haka ina roƙon shugaban hukumar da ya tabbatar cewa daga yanzu an kammala shirye-shiryen da suka kamata kafin ma’aikacin NECO ya yi ritaya.”

Ya kuma ce duk da jagororin hukumar na yanzu sun biya wasu daga cikin haƙƙoƙin nasu, ba a kai ga biyan alawus ɗin ƙarin girma ba, da na tafiye-tafiye ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
  • Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano