Aminiya:
2025-09-17@23:30:33 GMT

Me ya sa ake musayar yawu tsakanin APC da PDP?

Published: 9th, February 2025 GMT

Duk da cewa akwai sauran lokaci kafin babban zaben 2027, ana ci gaba da musayar yawu kan shirye-shiryen manyan ‘yan siyasa da ke hamayya da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, inda suke tarurruka tare da tuntuɓar juna kan yadda za su kayar da Jam’iyyar APC mai mulki a Zaɓen 2027.

Fadar Shugaban kasa ta mayar da martani kan kalaman da wasu daga cikin ‘ya’yan jam’iyyun adawa da na cikin gidanta suke yi, inda suka zarge ta da sauka daga kan turbar da jam’iyyar take.

Katsina ta zama cibiyar haɗin kan ƙabilun ƙasa a Arewa — Gwamna Radda Ta kashe saurayinta saboda ya gaisa da tsohuwar abokiyar karatunsa

Fadar Shugaban kasa na mayar da martani ne bayan wani taro da jagororin hamayya da wasu daga cikin ‘yan Jam’iyyar APC da ke adawa da gwamnatin suka gudanar a Abuja.

Jam’iyyar ta APC dai ta ce hakan ba komai ba ne illa yunƙurin da masu adawa da gwamnatin ta Bola Ahmed Tinubu ke yi na kawar da hankalin Tinubu daga hidimar da yake wa al’ummar kasar nan.

Sai dai Jam’iyyar adawa ta PDP ta ce, borin kunya ce gwamnatin APC ke yi, saboda manuniya ta nuna cewar al’ummar kasar nan sun gaji da mulkinta.

Malam Abdul’aziz Abdul’aziz na ɗaya daga cikin masu magana da yawun Shugaban kasar ya bayyana cewa, ganin irin rawar da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ke takawa wajen gyara kurakuran da Jam’iyyar PDP ta yi ne tsawon shekara 16 da suka ɗauka.

“Suna mulki ne ya sa suke kaɗa gangar siyasa tun kafin lokacin ya zo.

“Su wadanda suke irin wadannan zarge-zargen ai su ne mutanen da suke ɗauke hankalin gwamnati daga kan abin da ya kamata ta yi”, in ji Abdul’aziz.

Shi kuwa mataimakin mai magana da yawun Jam’iyyar PDP, Alhaji Ibrahim Abdullahi ya ce, martanin na fadar shugaban ba komai ba ne illa shure-shure da baya hana mutuwa, wanda duk ya iske shinkafa a Naira 6,000 da PDP ta faɗi zabe, yanzu kuma yake sayen shinkafar nan kan Naira 100,000, lallai akwai ayar tambaya da ake cewa wai ana gyara a cewar Ibrahim.

Fadar shugaban ta ce, taron da suka gudanar ba komai ba ne illa na wadanda ba sa fatan ci gaban kasar nan da kuma son tunzura al’umma da barazana da kuma bayyana ra’ayoyin da za su durƙusar da dimokuradiyya.

Jam’iyyun hamayya na fama da rikice-rikicen cikin gida, lamarin da masana kan harkokin siyasa ke bayyanawa da cewa zai iya kawo musu tarnaƙi wajen haɗewar da suke niyyar yi.

A shekarar 2023 ce dai Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu ya yi nasarar doke Alhaji Atiku Abubakar na Jam’iyyar PDP a Zaɓen Shugaban kasa, inda aka samu wasu gwamnonin PDP da ake zargin sun yi wa Jam’iyyar APC aiki.

Yanzu dai hankali ya karkata ne wajen ganin irin wainar da za a toya a babban taron Jam’iyyar PDP, wadda ke kan gaba a sahun jam’iyyun adawa.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jam iyyar PDP

এছাড়াও পড়ুন:

An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin

Hukumar jin daɗin jama’a ta Jihar Kwara tare da haɗin gwiwar Hukumar Gyaran Hali ta Najeriya sun kama wasu mabarata a titunan Ilorin, ciki har da wasu da aka samu da kuɗaɗen ƙasashen waje.

Daga cikin waɗanda aka kama akwai wani mabaraci mai suna Musa Mahmud daga Jihar Kano, wanda aka samu da takardar daloli.

Musa Mahmud ya shaida wa manema labarai cewa wani ne ya ba shi takardar Dala a Abuja.

Jami’ai sun bayyana damuwa kan yadda masu bara ke riƙe da kuɗaɗen da ba su dace da yanayin rayuwarsu ba.

Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki Cire tallafin man fetur shi ne abin da ya dace —Sarki Sanusi II

“Za mu bincika asalin waɗannan kuɗaɗen da kuma dalilin da ya sa suke da su,” in ji Adebayo Okunola, shugaban cibiyar gyaran hali a Jihar Kwara.

Jami’an gwamnati sun kwashe kusan mutane 40 daga wuraren da suka haɗa da Tipper Garage, Offa Garage, Tank da Geri Alimi Roundabout.

Jami’an sun ce bakwai daga cikin waɗanda aka kama an taɓa kama su a baya, amma sun koma tituna bayan an sako su.

Kwamishinar jin daɗin jama’a ta jihar, Dakta Mariam Imam, ta ce adadin masu bara da aka kama ya ragu sosai idan aka kwatanta da na baya, inda ta ce suna sauya dabaru don su guje wa kama.

Ta roƙi jama’a da su daina ba wa masu bara kuɗi kai tsaye, su maida gudummawarsu ta hanyar wuraren  ibada da gidajen marayu.

Jami’an gyaran hali sun ce za a tilasta wa waɗanda aka kama su yi aikin tsaftace tituna a matsayin horo da kuma darasi.

Wasu daga cikin masu barar sun roƙi gwamnati da ta tausaya musu, ba su da wata hanyar rayuwa sai bara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa