An bude atisayen soja kan teku bisa hadin gwiwar wasu kasashe a birnin Karachi na kasar Pakistan, a ranar 7 ga wata.

Asitayen sojan da kasar Pakistan ta tsara ya samu halartar jiragen ruwan soja daga kasashe sama da guda 10, wadanda suka hada da Sin, da Indonesiya, da Japan, da Italiya, da Malasiya, da kuma Amurka da dai sauransu.

Haka kuma, sauran kasashe sama da guda 40 sun tura masu sa ido wajen atisayen.

An raba atisayen sojan zuwa matakai guda biyu. Mataki na farko shi ne tsakanin ranaku 7 zuwa 9 ga watan Fabrairu, inda za a yi atisayen soja kan tashar jiragen ruwa, da tattaunawa kan atisayen, da tattaunawa kan ayyukan musamman tsakanin bangarori daban daban da dai sauran ayyuka. Sa’an nan, a tsakanin ranaku 10 zuwa 11 ga watan Fabrairu, za a fara mataki na gaba, wato atisayen soja kan teku, inda za a gudanar da atisaye a kan teku, da aikin binciken jiragen ruwan soja na kasa da kasa. Kana, mahalartar atisayen za su gudanar da ayyukan samar da kayayyaki da abubuwan da sojojin ruwa ke bukata, da kuma hadin gwiwa wajen yaki da ‘yan fashin teku da dai sauran ayyuka. (Mai Fassara: Maryam Yang)

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: atisayen soja kan

এছাড়াও পড়ুন:

Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje

Lamarin ya ci gaba da raguwa har zuwa 2024, inda yawan kudaden da ake kashewa a yawon ketare ya fadi da kaso 14 a matakin shekara-shekara zuwa dala biliyan 2.66.

Hakan na nuni da cewa ‘yan Nijeriya sun rage kashe kudaden da suke kashewa kan safarar jiragen sama da dala biliyan 1.12 ko kuma kashi 30 cikin dari a cikin shekaru biyun.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya