Fizishkiyan: Kasashen Musulmi Za Su Iya Sake Gina Yankin Gaza
Published: 9th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya yi kira da a kafa kawancen duniya da dukkanin kasashen musulmi za su shiga ciki, domin taimakawa mutanen Gaza, da sake gina yanki, tare da cewa, kasashen musulmi kadai za su iya sake gina yankin na Gaza tare da dawo da rayuwa a cikinsa.
A ganawar da ya yi da mambobin majalisar jagoranci ta kungiyar Hamas, anan Tehran ya yi jinjina ga shahidan kawancen gwagwarmaya, ya kuma yi murna akan nasarar da ‘yan gwgawarmaya su ka samu akan ‘yan sahayoniya.
Shugaban kasar ta Iran ya kara da cewa; Nasarorin da mutanen na Gaza su ka samu, sun hana makiya ‘yan sahayoniya cimma manufofin da su ka shata, duk da cewa adadin shahidan da aka samu suna da yawa.
Haka nan kuma ya ce; Abinda ya faru, ya cancanci a yi jinjina a gare shi, tare da kuma da taya dukkanin mayaka da dukkanin mutanen Gaza murnar samun nasara.
A nasu gefen, ‘yan majalisar jagorancin na kungiyar Hamas, sun gode wa jamhuriyar Musulunci ta Iran da dukkanin ‘yan gwgawarmaya, da kuma taya su murnar nasarar da aka samu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
Wasu Hare-haren da gwamnatin Isra’ila ta kai ya haddasa gobara a wasu matatun mai a lardin Bushehr da ke kudancin kasar Iran.
Gobarar ta tashi ne a wurin a ranar Asabar bayan da wasu kananan jiragen yakin Isra’ila guda biyu suka kai hare-hare a kan kayayyakin sarrafa iskar gas da ke yankin kudancin Pars.
Hare-haren sun yi haddassa fashe fashe a matatar iskar gas ta Fajr-e Jam, daya daga cikin mafi girma a Iran, da kuma wata karamar matatar mai a mataki na 14 na tashar iskar gas ta Kudu Pars.
Har yanzu ba a fitar da kiyasin barnar a hukumance ba.
Bayan gobarar, ma’aikatar mai ta Iran ta fitar da wata sanarwa inda ta tabbatar da harin.
Sanarwar ta ce, nan da nan aka kaddamar da aikin shawo kan gobarar da dakile ta.”
Matatar man ta Pars ta kudu ita ce tashar iskar gas mafi girma a duniya, wacce ke kan iyakar teku tsakanin Iran da Qatar.
Ta kunshi sama da kashi 70% na bukatun iskar gas na Iran.