HausaTv:
2025-09-17@21:51:09 GMT

Iran Ta Ce A Shirye Take Ta Tallafa Wa Burkina Faso A Yaki Da Ta’addanci

Published: 9th, February 2025 GMT

Iran ta ce a shirye take ta tallafa wa Burkina faso a yakin da take da ta’addanci.

Wannan bayyanin ya foto ne bayan wata ganawa tsakanin Firaministan Burkina Faso Rimtalba Jean Emmanuel Ouédraogo da jakadan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Burkina Faso, Mista Mojtaba Faghihi a Ouagadougou.

Taron dai ya baiwa mutanen biyu damar sake yin nazari kan hadin gwiwar dake tsakanin kasashensu.

A cikin wannan yanayi, Iran ta bayyana aniyar ta na tallafawa Burkina Faso, a kokarinta na dakile matsalar rashin tsaro.

Tehran, ta bakin jakadanta, ta kuma bayyana sha’awarta kan sauran fannonin hadin gwiwa, kamar su noma, masana’antu, likitanci da al’adu.

Ya ce Iran a shirye take ta ba da dukkan goyon bayan da ya dace ga Burkina Faso, yana mai jaddada a shirye Tehran ta ke na mara wa Ouagadougou baya a yakin da take yi da ta’addanci.

Wannan furuci na zuwa ne a wani yanayi da Burkina Faso ke fuskantar matsalar rashin tsaro, tana neman karkata dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare.

Firaministan Burkina Faso ya yi marhabin da wannan shiri, yana mai jaddada matsayin kasarsa da kokarin Iran wajen yaki da ta’addanci.

 Ya kuma bayyana goyon bayansa ga fadada hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu. Wannan taron ya ba da damar tattaunawa kan yadda za a yi hadin gwiwa a bangarori da dama da suka hada da noma, masana’antu, likitanci da al’adu, wanda ke nuna muradin karfafa alaka tsakanin kasashen biyu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin
  • Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
  • Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Runduwar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai
  • Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu