Iran Ta Ce A Shirye Take Ta Tallafa Wa Burkina Faso A Yaki Da Ta’addanci
Published: 9th, February 2025 GMT
Iran ta ce a shirye take ta tallafa wa Burkina faso a yakin da take da ta’addanci.
Wannan bayyanin ya foto ne bayan wata ganawa tsakanin Firaministan Burkina Faso Rimtalba Jean Emmanuel Ouédraogo da jakadan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Burkina Faso, Mista Mojtaba Faghihi a Ouagadougou.
Taron dai ya baiwa mutanen biyu damar sake yin nazari kan hadin gwiwar dake tsakanin kasashensu.
A cikin wannan yanayi, Iran ta bayyana aniyar ta na tallafawa Burkina Faso, a kokarinta na dakile matsalar rashin tsaro.
Tehran, ta bakin jakadanta, ta kuma bayyana sha’awarta kan sauran fannonin hadin gwiwa, kamar su noma, masana’antu, likitanci da al’adu.
Ya ce Iran a shirye take ta ba da dukkan goyon bayan da ya dace ga Burkina Faso, yana mai jaddada a shirye Tehran ta ke na mara wa Ouagadougou baya a yakin da take yi da ta’addanci.
Wannan furuci na zuwa ne a wani yanayi da Burkina Faso ke fuskantar matsalar rashin tsaro, tana neman karkata dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare.
Firaministan Burkina Faso ya yi marhabin da wannan shiri, yana mai jaddada matsayin kasarsa da kokarin Iran wajen yaki da ta’addanci.
Ya kuma bayyana goyon bayansa ga fadada hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu. Wannan taron ya ba da damar tattaunawa kan yadda za a yi hadin gwiwa a bangarori da dama da suka hada da noma, masana’antu, likitanci da al’adu, wanda ke nuna muradin karfafa alaka tsakanin kasashen biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran
Rahotanni da muka samu sun nuna cew wasu yan ta’adda sun kashe wasu dakarun sa kai guda biyu a kudu masu gabashin iran a yankin sisitan Baluchistan.
Jami’In huda da jama’a na dakarun kare juyi yayi karin harke game da harin da aka kai, yace an kashe mutane ne yayin da suke kokarin ketare da jami’an tsaro suna tafiya akan babbar hanyar da ta hada birnin kashsh dake lardin da kuma babban birnin zahidan
An bayyana cewa wanda abin ya shafa sun hada da Esma’il shavarzi da kuma mukhtar shahouze da kuma wadanda suka samu mummuan rauni a lokacin kai harin
Lardin sistan baluchestan na da iyaka da kasar Pakistan da ya dade yana fuskantar tashe tashen hankula kan fararen hula da kuma jami’an tsaro
Hukumomin yankin sun sha bin asalin tushen irin wadannan hare-hare zuwa cibiyoyin leken asirin na kasashen waje dake nuna goyon bayan yan’ taa’dda dake irin wadannan ayyukan a yankin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania November 1, 2025 Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada November 1, 2025 Shugaban Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini November 1, 2025 Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci