Iran Ta Kira Taron Gaggawa Na Ministocin OIC, Kan Shirin Trump Na Kwace Gaza
Published: 9th, February 2025 GMT
Iran ta bukaci taron gaggawa na ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar hadin kan kasashen Musulmi ta OIC, game da shirin shugaba Donald Trump na Amurka na kwace Gaza da kuma korar al’ummar Zirin.
Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran, yana mai jaddada cewa haramtaccen shirin” na shugaban kasar Amurka kan Gaza ya gamu da kakkausan ra’ayi daga kasashe daban-daban, inda ya yi kira da a gudanar da taron gaggawa na ministocin kungiyar ta OIC domin tattaunawa da yanke shawara kan wannan batu.
A wata tattaunawa daban daban ta wayar tarho da wasu takwarorinsa a yammacin jiya Asabar ministan harkokin wajen na Iran Sayyid Abbas Araghchi da takwaransa na kasar Masar Badr Abdel-Aty, Abbas Araghchi ya yi Allah wadai da shirin hadin gwiwa tsakanin Amurka da Isra’ila na tilastawa mutanen Gaza gudun hijira a yankin da aka yi wa kawanya.
Mista Araghchi ya ce dole ne dukkan al’ummar musulmi su tashi tsaye wajen dakile wannan makirci.
Araghchi yakuma tattauna da babban sakataren kungiyar hadin kan kasashen musulmi OIC Hussein Ibrahim Taha ta wayar tarho.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya yi kira da a gudanar da wani taro na musamman na kungiyar domin daukar kwararan matakai masu inganci na kare hakkin Falasdinawa.
Ya kuma bayyana babban nauyin da ke wuyan kasashen musulmi na tallafawa Falasdinawa da ake zalunta, musamman hakkinsu na cin gashin kansu.
“Shirin tilastawa Falasdinawa kaura daga Gaza ba wa kawai babban laifi ba ne da ke da alaka da ‘kisan kare dangi,’ barazana ne ga tsaron yankin da kuma duniya baki daya,” in ji shi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu
Iran da Rasha sun tattauna kan inganta hadin gwiwar kafofin yada labarai da yaki da labaran karya
Jakadan kasar Iran a birnin Moscow Kazem Jalali ya gana da mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha Maria Zakharova a jiya Talata inda suka yi musayar ra’ayi kan bunkasa hadin gwiwar kafofin yada labarai.
Bangarorin biyu sun tattauna batutuwan baya-bayan nan da suka hada da yiwuwar gudanar da harkokin yada labarai, da nazarin yiwuwar bunkasa hadin gwiwar kafofin watsa labaru, da hanyoyin yin tasiri a kafofin watsa labaru, da matakan hadin gwiwa don kara fahimtar ra’ayin jama’a a kasashen biyu.
Bangarorin biyu sun yi tsokaci kan yadda kafafen yada labarai ke yada jita-jita da nufin yin zagon kasa ga dangantakar kasashen Iran da Rasha tare da tattauna hanyoyin yaki da labaran karya da yada labarai marasa tushe ko madogara.
A farkon taron, jakadan Iran ya yi tsokaci kan karairayi da kafafen yada labaran yammacin duniya ke yadawa, musamman Axios, dangane da alakar da ke tsakanin kasashen biyu, ya kuma mika godiyarsa ga ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha kan wannan batu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba July 30, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami July 30, 2025 Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci July 30, 2025 Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya July 29, 2025 Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon July 29, 2025 EU Tace Zata Dakatar Da HKI Daga Cibiyar Bincikenta Saboda Gaza July 29, 2025 Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar July 29, 2025 Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki July 29, 2025 Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci