Iran Ta Kira Taron Gaggawa Na Ministocin OIC, Kan Shirin Trump Na Kwace Gaza
Published: 9th, February 2025 GMT
Iran ta bukaci taron gaggawa na ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar hadin kan kasashen Musulmi ta OIC, game da shirin shugaba Donald Trump na Amurka na kwace Gaza da kuma korar al’ummar Zirin.
Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran, yana mai jaddada cewa haramtaccen shirin” na shugaban kasar Amurka kan Gaza ya gamu da kakkausan ra’ayi daga kasashe daban-daban, inda ya yi kira da a gudanar da taron gaggawa na ministocin kungiyar ta OIC domin tattaunawa da yanke shawara kan wannan batu.
A wata tattaunawa daban daban ta wayar tarho da wasu takwarorinsa a yammacin jiya Asabar ministan harkokin wajen na Iran Sayyid Abbas Araghchi da takwaransa na kasar Masar Badr Abdel-Aty, Abbas Araghchi ya yi Allah wadai da shirin hadin gwiwa tsakanin Amurka da Isra’ila na tilastawa mutanen Gaza gudun hijira a yankin da aka yi wa kawanya.
Mista Araghchi ya ce dole ne dukkan al’ummar musulmi su tashi tsaye wajen dakile wannan makirci.
Araghchi yakuma tattauna da babban sakataren kungiyar hadin kan kasashen musulmi OIC Hussein Ibrahim Taha ta wayar tarho.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya yi kira da a gudanar da wani taro na musamman na kungiyar domin daukar kwararan matakai masu inganci na kare hakkin Falasdinawa.
Ya kuma bayyana babban nauyin da ke wuyan kasashen musulmi na tallafawa Falasdinawa da ake zalunta, musamman hakkinsu na cin gashin kansu.
“Shirin tilastawa Falasdinawa kaura daga Gaza ba wa kawai babban laifi ba ne da ke da alaka da ‘kisan kare dangi,’ barazana ne ga tsaron yankin da kuma duniya baki daya,” in ji shi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
Shugaban kungiyar hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’imKasim ya bayyana cewa, kungiyarsa tare da Sojojin kasar da kuma mutanen kasar ne zasu tabbatar da ci gaban kasar Lebanon a wannan halin da ake ciki.
Tashar talabijin ta Al-Mayadeen ta nakalto sheikh Na’im kasim yana fadar haka a wani jawabin da ya gabatar a jiya Litinin, jawabinda kafafen yada labarai da damaa suka watsa kai tsaye.
Sheikh Qasim kasar Lebanon zata ci gaba da zama mai karfi idan gwamnatin kasar ta dakatar da hare-haren da HKI take ci gaba da kawowa a kan kasar, da kwato dukkan yankunan kasar da aka mamaye, har’ila yau da kuma ci gaba da hadin kai tsakanin masu gwagwarmaya, sojoji da kuma mutanen kasar.
Shugaban kungiyar ya jadda bukatar sake gina wuraren da HKI ta rusa a yankunan daban daban a kasar, ya ce gwamnatin kasar ta yi alkawalin zata sake gina wuraren da HKI ta rusa a yakin da hizbullah a baya-bayan nan.
Kuma ya ce rashin yin haka nuna bambanci ne a tsakanin mutanen kasar. Ya ce dangane da wadanda aka rusa gidajensu kungiyar ta bada kudaden haya ga 50,755 , sannan ta gyura wasu 332 da aka lalata, wanda duk aikin gwamnati ne ta yi hakan. Don haka akwai bukatar gwamnati ta aikata wajibin da ya hau kanta.