Aminiya:
2025-11-03@04:09:48 GMT

Gwamnatin Kano ta dakatar da wani fim mai suna Zarmalulu

Published: 9th, February 2025 GMT

Gwamnatin Kano ta dakatar da wani fim da take zargin ya saɓa ka’ida tare da gayyatar dukkannin wanda suka fito a cikinsa domin sauraron ba’asi.

Hukumar tace fina-finai da dab’i ta Kano ce ta dakatar da fim ɗin mai suna Zarmalulu bayan ƙorafin da aka miƙa mata.

Taron Qur’ani: Tsakanin magoya baya da masu kushe Me ya sa ake musayar yawu tsakanin APC da PDP?

Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar a ranar Asabar, ta ce ana zargin waɗanda suka shirya fim ɗin sun sanya masa suna na baɗala.

“Biyo bayan ƙorafin da Hukumar ta karɓa daga wasu masu kishin Jihar Kano akan wannan fim ɗin, Shugaban Hukumar, Abba El-Mustapha ya bayyana damuwarsa kan lamarin tare da dakatar da fim ɗin.

“Haka kuma, Abba El-Mustapha ya gayyaci dukkannin wanda suka fito a shirin domin jin ba’asi na yin amfani da ita wannan kalma.”

Bayanai sun ce fim ɗin mai suna “Zarmalulu” ana zarginsa da rashin ma’ana sannan an yi masa laƙabi da wani suna mai kama da na baɗala.

Hukumar ta buƙaci duk waɗanda suka yi ruwa da tsaki a fim ɗin da su bayyana a gaban kwamatin bincike da ta kafa.

Hukumar tace fina-finan na da hurumin dakatar da dukkannin wani fim da bata gamsu da yadda aka shirya shi ba tare da ladaftar da duk wani da ta samu da yin abinda bai kamata a cikin kowane fim ba ko kuma a wajen fim ɗin matsawar ɗan Masana’antar Kannywood ne.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hukumar Tace Fina Finai Jihar Kano kannywood Zarmalulu

এছাড়াও পড়ুন:

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara November 2, 2025 Wasanni Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar? November 2, 2025 Wasanni Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025? November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare