A’a ba ni da aure amma in sha Allah ina sa ran yi.

 

Malama Khadija kina da wata sana’a ne ko kuma karatu kike yi?

Eh ina da Diploma a Cibil Law, sai Degree a Islamic Studies,.kuma ni cikakkiyar ‘yar kasuwa ce,.na Fara sana’a a 2016

 

Wane irin kasuwanci kike yi ma ana dame-dame kike sayarwa?

Mhm, gaskiya ina kasuwanci da yawa kamar sarrafa dinki, kayan dandano da goge-goge da sarrafa dukiya

 

Me ya ja hankalinki da har kike sha’awar wannan sana’ar?

Ni dai gaskiya ban yadda da rayuwa akan dogaro da wani ba, rayuwata ita ce, kuma na fi yarda da in samu abu na kaina ba sai na je roko ba ko kuma sai na jira an bani saboda ni ba na son wulakanci kuma na yi amfani da baiwar da Allah ya ba ni ta sana’a.

Ni jajirtacciya ce, ina tambayar wani, wane irin business yake ganin ya kamata na yi, ya ce min cleaning da property management. Daganan sai na yi kokari na fara neman yadda zan yi, cikin ikon Allah sai na samu, nan da nan na yi kokarin yadda zan samu ma’aikata, daga nan na dauki ma’aikata muka yi ciniki da su yadda zan rika biyansu a wata, suma wadanda suka bani aiki suka gaya min yadda za su rika biyana a wata shike nan na fara. Da haka da haka tafiya tai tafiya na kara samun wasu wuraren har na bunkasa.

 

Wanne irin kalubale kika taba fuskanta a cikin sana’arki?

Ina ga kowace sana’a da nata kalubalen na wahala, a da can baya wurin samun kwastomomi, asarar kudade, ga rashin samun zama, wasu za su ce za su ba da adbance daga baya su ciko  amma sam ba su yi.

 

Zuwa yanzu wadanne irin nasarori kika cimma?

Gaskiya Alhamdulillah, ba abin da zan ce sai godiya ga Allah. Ban taba tunanin a cikin karamin lokaci zan samu kwantiragi din da na samu a yanzu ba a fannin property management. Kuma ta haka na samu damar haduwa da mutanen da ban yi tsammani zan hadu da su ba kai har da wurare daban-daban.

 

Wane abu ne ya fi faranta miki rai game da sana’arki?

Ba abin da na fi so kamar in ga an yaba min aikin da na yi shi ya sa na ke ba da dukka ma’ana lokaci, kudadena don ganin na ba da sakamako mai kyau fiye da yadda ake zato. Kuma Alhamdulillah ayyukana suna kyau da taimakon ma’aikatana.

 

Dame kike so mutane su rika tunawa dake?

Na yi gidauniya a baya YOTD inda na taimaka wa marasa lafiya na samo musu kudin magani, a yanzu ma na canza wa gidauniyar suna ta koma Bisit the sick saboda na maida hankali kan marasa lafiya sosai.

 

Wace irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

Addu’ar samun miji da ‘ya’ya nagari da rabuwa da iyaye lafiya

 

Wane irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan  uwanki?

Gaskiya ina samun goyon baya sosai daga iyayena, ‘yan uwa da kuma wanda zan aura a da ya tsaya sosai wajen ganin komai ya tafi daidai

 

Kawaye fa?

Hahahaha, ai ni ta kowa ce duk inda na shiga ina blending da wuri amma kawaye na sosai ba su da yawa don ni dai sana’a ce kawata amma ina da kawaye biyu zuwa uku haka.

 

Me kika fi so cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Ni ba mai son kwalliya sosai bace wato na fi son sanya kaya masu sauki wanda ba zai takura min ba kuma ni na ni son atamfa kuma masoyiyar turare ce ni.

 

A karshe wace irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

Mata mu tsaya da kafafunmu, kar mu jira sai an ba mu kuma roko ba kyau, ka jira an baka yau, gobe an baka jibi ai ba za a bayar ba. Ko auna ka fiya tambaya. Kuma yandu yawanci naza sun fi son auren mai sana’a ko kuma mai yin aiki don kar ki zame musu larura, kuma wasu mazan ganin cewa kina kokarin neman naki zai sa su tallafa miki.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

 Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A Zirin Gaza

Sojojin HKI suna ci gaba da kai hare-hare a sassa daban-daban na yankin zirin Gaza da su ka hada da sansanonin ‘yan hijira da kuma rusa gidajen da su ka saura a tsaye.

Tashar talabijin din ‘almayadin” ta bayyana cewa; An sami shahidai 7 da safiyar yau Laraba, bayan harin da ‘yan sahayoniyar su ka kai akan wani gida da yake a Deir-Balah,dake tsakiyar zirin Gaza.

A can sansanin ‘yan hijira dake kusa da filin wasa na ‘al-Anan’ kuwa mutane 4 ne su ka jikkata.

 A yankin Safdawi dake cikin birnin Gaza, jiragen yakin HKI sun kai hare-hare akan wani gida wanda ya haddasa gobara, da kuma shahadar mutane 8.

A unguwar “Shuja’iyya” sojojin na mamaya sun rushe gidaje da dama.

Gabanin wannan lokacin, an sami wasu shahidan 3 da kuma jikkatar mutane 46 a kusa da cibiyar da Amurka da Isra’ila su ka ware domin raba kayan abinci.

Kididdiga ta karshe wacce ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta fitar ta bayyana cewa; adadin Falasdinawan da su ka yi shahada daga 7 ga Oktoba, sun kai dubu 45,56, sai kuma wadanda su ka jikkata da sun kai 129, da kuma 123.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)
  • Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa
  • Yadda ambaliyar Neja ta ci mutum 12 ’yan gida daya
  • NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin 2025
  • Ɗalibai sun maƙale lokacin da gini ya rufta suna jarrabawa
  • Ko kwabo ban ciyo bashi ba tun da na zama Gwamnan Kaduna – Uba Sani
  •  Yemen: Wuce Gona Da Irin HKI Ba Zai Sauya Mana Ra’ayi Akan Ci Gaba Da Taimaka Wa Gaza Ba
  • Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi
  • Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana
  •  Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A Zirin Gaza