Ta kashe saurayinta saboda ya gaisa da tsohuwar abokiyar karatunsa
Published: 9th, February 2025 GMT
Wani matashi ɗan kasar Argentina mai shekara 23 ya rasa ransa a sakamakon daɓa masa wuƙa da budurwarsa ta yi saboda kawai ya gaisa da wata mata a kan titi.
Kishi madaidaici zai iya zama abu mai masu alaka da juna, amma mafi yawanci na iya wuce kima!
Abba ya naɗa sabon Sakataren Gwamnatin Kano Shigo da hatsi daga ƙetare ya karya farashinsa a NejaIdan aka dubi labarin Mariano Grinspun, ɗan shekara 23 daga González Catán, wani birni a lardin Buenos Aires na Argentina, wanda budurwarsa mai tsananin kishi ta caka masa wuka wanda ya yi sanadiyya mutuwarsa bayan ya gaisa da wata tsohuwar abokiyar karatunsa a titi, za a ga abin akwai ban mamaki.
Abin ya faru ne ranar 21 ga Oktoba 2024, kusa da titin Balboa da La Bastilla, a birnin González Catan.
Mariano da budurwarsa Natacha Palavecino, suna tafiya tare, sai suka ci karo da wata mata da ta gaida Mariano kuma ta tambaye shi halin da yake ciki.
Gaisuwar ta haukata budurwar Mariano, inda ta zaro wuƙa a ɓoye ta afka masa.
Matar da ta gaisa da Mariano Grinspun, tsohuwar abokiyar karatunsa ce, amma hakan ya tunzura budurwarsa.
Natacha ta kai hannu ta ɗauki wata boyayyiyar wuƙa sannan ta yanki matar mai suna LC kamar yadda kafafen yada labarai na kasar Argentina suka bayyana.
Bayan yankar LC da wuƙar ta faɗi kasa ta yi yunƙurin ƙara yankar ta, amma ta sa hannunta ta kare, wanda da watakila ta kashe ta da ba don wani mutumin ba wanda ya yi nasarar daƙile faruwar hakan.
Abin takaici, Mariano Grinspun bai yi sa’a sosai ba, domin bayan da ta gaza kashe matar, Natacha Palavecino ta far wa saurayin nata, inda ta daɓa masa wuƙa a kirji.
Masoyan sun yi ta muhawara ta tsawon mintuna da dama, kamar yadda kyamarorin sa ido na CCTV a yankin suka nuna, wanda a lokacin Mariano ya fadi kasa yana shure-shure.
Zuwa wani lokaci, ya kasa tashi sai budurwarsa mai shekara 32 ta kai masa hari da hannunta.
Shaidun gani da ido sun kira jami’an agajin gaggawa, amma ba su iya yin komai ba wajen ceto rayuwarsa.
Wani bincike da aka gudanar ya bayyana tarihin tashin hankali Natacha Palavecino.
A 2021, an yanke mata hukuncin daurin shekara daya a gidan yari saboda ta dava wa wani tsohon saurayinta wuƙa a kirji, har ma Mariano da kansa ya kai ƙarar ta ga ’yan sanda saboda barazanar da ta yi masa da kuma yi masa rauni a jiki.
A watan Yulin shekarar bara ce aka ba da umarnin hana Natacha duk wata alaka da Mariano.
Sai dai bayan wucewar wa’adin, sai ya yanke shawarar sake dawowa da alakar.
Palavecino mai shekaru 32 za ta iya kasancewa a gidan yari tsawon shekaru saboda wannan laifi na kisan saurayinta da kuma yunkurin kisan matar da ta gaishe shi a kan titi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Argentina
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
Hukumar Tace Fina-Finai da Dab’i ta Jihar Kano ta haramta shirya duk wata muƙabala tsakanin mawaƙan yabon Annabi (S.A.W), tare da gayyatar mawaƙa Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi su bayyana a gabanta.
Hukumar ta kuma gayyaci mawaƙan ne tare da sauran waɗanda suka jagoranci muƙabalar da fitattun mawaƙan biyu suka yi ranar Litinin, da su bayyana a gabanta cikin sa’o’i 24.
Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin TinubuHakan na zuwa ne ƙasa da kwana ɗaya bayan ɓullar wata muhawara da aka yi tsakanin Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi kuma ta karade shafukan sada zumunta, wacce hukumar ta bayyana a matsayin karya dokokin aikinta.
Shugaban hukumar, Abba El-Mustapha ne ya sanar da hakan ranar Talata, inda ya ce ɗaukar matakin wani yunƙuri ne na tabbatar da zaman lafiya, daidaito da bin doka tsakanin mawaƙan nishaɗi da na addini.
El-Mustapha, a cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar, ya kuma ce an haramta duk wata nau’in muƙabala daga mawaƙan addini a jihar ba tare da izinin hukumar ba.
A yayin da yake ƙaddamar da wani kwamitin bincike da shugaban hukumar ya naɗa karkashin Daraktan Ayyuka na Musamman a hukumar, Isah Abdullahi, El-Mustapha ya umarci waɗanda aka gayyatar da su bayyana a gaban kwamitin domin amsa tambayoyi.
Hukumar ta ce shirya irin waɗannan muhawara ba tare da izininta ba ya saɓa doka kuma zai iya jawo hukunci mai tsanani ga wanda suka karya.
Hukumar ta kuma jaddada ƙudirinta na ci gaba da kula da ayyukan mawaƙan da masu nishaɗantarwa a faɗin jihar tare da yin kira ga jama’a da su zauna lafiya sannan su ci gaba da ba ta haɗin kai a ayyukanta.