Saura ƙiris Bello Turji ya zo hannu – Ministan Tsaro
Published: 5th, February 2025 GMT
Ministan Tsaro, Muhammad Badaru Abubakar, ya bayyana cewa sun kusa da kama ƙasurgumin ɗan ta’addan nan da ya addabi yankin Arewa Maso Yamma, Bello Turji.
Ministan ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya tana da tabbacin cewa matsalar tsaro za ta zama tarihi kafin ƙarshen shekarar 2025.
Sarkin Jiwa a Abuja ya yi rashin mahaifiya Tinubu ya ƙara kasafin kuɗin 2025 zuwa N54.2trn
“Shugaban ƙasa na cewa yaushe matsalar tsaro za ta ƙare, saboda lokacin da ya kamata ta ƙare ya yi.
“A wani zama da muka yi da shi da shugabannin hafsoshin tsaron, an tattauna sosai, kuma shugaban ya ce su faɗa masa yaushe matsalar za ta ƙare, suka ce da yardar Allah zuwa ƙarshen shekarar nan,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa: “Sun ce ko matsalar ba ta ƙare gaba ɗaya ba, to za a ga sauƙin da kowa zai gani ya kuma ji daɗi.”
A wani taron da aka yi tare da shugabannin tsaro, Badaru, ya ce Shugaban Ƙasa ya bayyana cewa yana tsammanin matsalar tsaro za ta ƙare kafin ƙarshen shekara mai zuwa.
Hakazalika, ya ce idan matsalar ba ta ƙare, gwamnatin za ta ɓullo da sabbin dabaru domin murƙushe ta’addanci a yankin da ma Najeriya baki ɗaya.
A yayin tattaunawa da BBC Hausa, Ministan ya bayyana cewa duk da a yanzu ba a kama Turji ba, amma suna da labarin ya fara guje-guje, kuma nan ba da jimawa ba zai shiga hannu.
Ministan ya tabbatar da cewa tsare-tsaren da Gwamnatin Tarayya da hafsoshin tsaro suke aiwatarwa, za su kai ga gagarumar nasara wajen inganta tsaro a Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa maso yamma Ministan tsaro Muhammad Badaru Abubakar
এছাড়াও পড়ুন:
Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai, ya bayyana cewa sauyin jam’iyyar da manyan ‘yan suke yi zuwa jam’iyyar APC ana kamba ma shi fiye da yadda ya kamata, yana cewa wannan sauyin ba zai shafi kokarinsa na neman mafita ga matsalolin Nijeriya ba. Ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da manema labarai a Kano yau Litinin.
El-Rufai ya bayyana cewa shi ne na farko da ya koma jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) daga APC a kokarinsa na warware matsalolin Nijeriya ta hanyar kawar da tsarin kawancen siyasa.
Ficewar El-Rufai Daga APC Babban Rashi Ne – Tsohon Hadimin Buhari El-Rufai Ya Shiga Tsilla-tsilla Bayan Rasa Kujerar Minista – APC“SDP ta hankali wajen nemo mafita ga matsalolin Nijeriya da kuma ba da dama ga wadanda a siyasance ta hanyar kawancen jam’iyyu” in ji El-Rufai.
Ya kara da cewa sauyin jam’iyyar ‘yan siyasa ba shi ne babban batu ba, a cewarsa, babban batu shi ne wanda zai iya warware matsalolin Nijeriya da kuma isar da wannan ga al’umma ta yadda za su fita zabe a ranar zabe.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp