Ɗalibin Jami’a Ya Hallaka Kansa Saboda Matsin Rayuwa A Jihar Kwara
Published: 5th, February 2025 GMT
An kuma samu labarin cewa ɗalibin ya rasa mahaifinsa a wasu shekarun baya, lamarin da ya mahaifiyarsa wadda tsohuwar malamar makaranta ce ta ci gaba da ɗaukar nauyin karatunsa tun daga lokacin.
Rahotanni sun nuna cewa matsalarsa ta ƙara tsananta tun bayan dawowarsa makaranta a bara, inda abokan karatunsa suka tara kuɗi domin biya masa kuɗin makaranta da kuma siya masa kayan abinci.
Duk da cewa jami’ar ba ta fitar da sanarwa a hukumance ba, amma wani babban jami’i a makarantar, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Talata, yana mai bayyana hakan a matsayin abin mamaki da ya jefa jami’ar cikin jimami.
এছাড়াও পড়ুন:
An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi
Wata rundunar haɗin gwiwa ta jami’an tsaro ta samu nasarar kuɓutar da wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su da shanu da aka sace a Jihar Kebbi.
Bayanai sun ce an sace mutanen da dabbobin ne a ƙauyukan Ukuhu da Kokanawa a Karamar Hukumar Danko Wasagu ta jihar.
‘ADC za ta mayar da APC jam’iyyar adawa a 2027’ Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADCWani daraktan tsaro a Gwamnatin Kebbi, Abdurrahama Zagga ne ya sanar wa manema labarai nasarar da aka samu a ranar Talata, inda ya ce an kai samamen ne bayan umarni da aka samu daga Gwamna Nasiru Idris bisa bayanan sirri da aka tattaro a yankin.
A cewar Zagga, tawagar jami’an tsaro ta fatattaki ’yan ta’addan da suka yi garkuwa da mutanen da kuma shanun da suka sace a wani gulbi da ke iyaka da Jihar Zamfara.
“Mutane da aka ceto an mika su ga iyalansu. Kuma wannan abin farin ciki ne ga gwamna musamman a kokarin da jami’an tsaro suke yi, lamarin da zai kara inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin masarautar Zuru.”
Ya bayyana fatan da suke da shi na kawar da ɓarayin shanu da ’yan bindigar Lukurawa a yankin Zuru da Argungu.