Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-08-02@05:12:56 GMT

Shugaba Tinubu Zai Ziyarci Takwaransa Na Faransa Emmanuel Macron

Published: 5th, February 2025 GMT

Shugaba Tinubu Zai Ziyarci Takwaransa Na Faransa Emmanuel Macron

A yau ne shugaba Bola Ahmed Tinubu zai tashi daga Abuja zuwa birnin Paris na kasar Faransa a wata ziyarar kashu kai, inda daga nan zai wuce Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha.

A cikin wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga ya fitar, ya ce a birnin Addis Ababa, shugaba Tinubu zai bi sahun shugabannin Afirka a zaman taron majalisar zartarwa karo na 46 da kuma zaman taro na 38 na shugabannin kasashen kungiyar tarayyar kasashen Afirka wato AU, wanda aka shirya daga ranar 12 zuwa 16 ga watan Fabarairun 2025.

Shugaban zai isa Addis Ababa a farkon mako mai zuwa don halartar taron kungiyar  ta AU.

Yayin da yake kasar Faransa, shugaba Tinubu zai gana da takwaransa na Faransa, shugaba Emmanuel Macron.

 

Bello Wakili

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Faransa Taron AU Ziyara

এছাড়াও পড়ুন:

Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta sanar da cewa za ta kammala aikin shimfiɗa layin dogo wanda ya taso daga Kaduna zuwa Kano a cikin shekarar 2026 mai zuwa.

Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris ne ya bayyana hakan cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X a yau Laraba.

Kazalika, takwaransa na sufuri, Sa’idu Ahmed Alkali ya jaddada hakan ne a yayin jawabinsa a wajen wani taron tuntuɓa tsakanin ’yan ƙasa da gwamnati da ke gudana a Jihar Kaduna.

Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa

A cewar ministan, lokacin da Shugaba Bola Tinubu ya hau mulki kashi 15 cikin 10 na aikin kawai aka kammala.

Wata sanarwa da ma’aikatar yaɗa labarai ta fitar ta ambato ministan yana cewa “amma zuwa yanzu an kammala kashi 53 cikin 100.”

A 2024 Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa ta samu rancen kuɗin da za ta kammala aikin daga wani bankin kasuwanci na ƙasar China, abin da ministan ya jaddada a yau ɗin.

Kazalika, ministan ya ce Gwamnatin Tarayyar ta samu duka kuɗin gudanar da aikin gina layin dogo daga birnin Maiduguri na Jihar Borno zuwa garin Aba na Jihar Abiya.

“Layin dogon mai tsawon kilomita 1,443 zai ratsa jihohin Borno, da Yobe, da Gombe, da Bauchi, da Filato, da Kaduna, da Nasarawa, da Binuwai,” in ji sanarwar da kakakin ministan Rabiu Ibrahim ya fitar.

Sai dai sanarwar ba ta bayyana inda gwamnatin ta samo kudin ba.

Ministan ya kuma bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta gyara layin dogo na dakon kaya tsakanin Legas zuwa Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Haɗarin tirela ya yi sanadin asarar awaki sama da 100 a Zariya
  • Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa
  • Shugaban Kasar Iran Zai Ziyarci Pakistan A Gobe Asabar
  • Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
  • Tinubu ya tsawaita wa’adin aikin shugaban hukumar Kwastam
  • Tinubu ya tsawaita wa’adin shugaban hukumar Kwastam
  • An Yaba Da Kwazon Shugaba Bola Ahmad Tinubu
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya