Kungiyar Hams Ta Jinjinawa Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Kan Goyon Bayan Gwagwarmaya
Published: 31st, January 2025 GMT
Kungiyar Hamas ta yaba da rawar da Iran ke takawa wajen tallafawa al’ummar Falasdinu masu neman ‘yanci kai
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya gana da wata tawaga daga jagororin kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas, karkashin jagorancin shugaban majalisar gudanarwa (wanda aka kafa bayan kisan jagoran kungiyar Yahya Sinwar) Mohammed Darwish, a babban birnin Qatar, Doha a jiya Alhamis.
Sanarwar da kungiyar Hamas ta fitar ta bayyana cewa, tawagar kungiyar ta hada da shugabannin Khalil Al-Hayya, Hussam Badran, Izzat Al-Rishq da Basem Na’im.
Darwish ya yaba da rawar da Iran ta taka wajen tallafa wa al’ummar Falasdinu masu neman ‘yancin kai, yana mai jaddada cewa: “Harin Daukan Fansa naAmbaliysar Al-Aqsa Mai Albarka” wani ci gaba ne a yunkurin al’ummar Falasdinu na fatattakar ‘yantar da kai daga ‘yan mamayar Isra’ila.”
Ya kuma jaddada cewa: “Shirye-shiryen da mafarkin da gwamnatin mamayar Isra’ila suke yi na kawar da al’ummar Falasdinu daga kasarsu ta gado ta hanyar kaddamar da yaki da kashe-kashe ta kowane irin nau’in ta’addanci, ba zasu taba amfani ba, kuma al’ummar Falasdinu sun kafu ne a cikin kasarsu, suna sadaukar da kai ne domin hakkinsu da Qudus da kuma Masallacin Al-Aqsa”.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: al ummar Falasdinu
এছাড়াও পড়ুন:
Pezeshkian: Bunkasa Masana’antar Makamashin Nukiliyar Iran Don Inganta Rayuwar Al’ummar Iran Ne
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Faɗaɗa masana’antar makamashin nukiliyar Iran don inganta rayuwar mutanen kasar ne, ba don makamai ba
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya gana da manyan jami’ai a masana’antar makamashin nukiliya ta ƙasar a lokacin ziyarar da ya kai Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran (AEOI).
Shugaban Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Masoud Pezeshkian, ya ziyarci AEOI a ranar Asabar da yamma, inda ya gana da wasu manyan jami’ai a masana’antar makamashin nukiliyar.
A yayin taron, Shugaba Pezeshkian ya jaddada cewa: Abin takaici, farfagandar son zuciya ta sanya ra’ayin “Makamashin nukiliya” ya zama daidai da samar da makaman nukiliya. Ya ce, “Samar da bama-bamai na nukiliya ƙaramin ɓangare ne kawai na sakamakon da ba su dace ba da rashin tausayi na wannan fanni. Sauran wannan masana’antar tana da nufin biyan buƙatun ɗan adam na asali. Manufar Iran da nufin kasar na faɗaɗa wannan masana’antar ita ce biyan buƙatun mutane da inganta rayuwar ƙasar ne, ba don samar da makamai ba.”
Shugaban ya kuma jaddada cewa: “Suna ɗaukar amfani da bama-bamai na nukiliya haramun ne, bisa ga fatawar da Babban Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci ya bayar.” Ya ƙara da cewa: “Ilimin yana cikin tunanin masana kimiyyar Iran, kuma rushe gine-gine da masana’antu ba zai hana kasar ci gaba ba. Za ta sake gina cibiyoyin makamashin nukiliyarta da ƙarfi sosai.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran November 2, 2025 Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani November 2, 2025 Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza November 2, 2025 Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci