JMI Ta Cika Shekaru 46 Cib Da Nasarrar Juyin Juya Halin Mususlunci A Kasar, Wani Irin Ci gaba Ne Ta Samu A Cikin Wannan Lokacin
Published: 30th, January 2025 GMT
A ranar 11 Ga Watan Fabarainu na wannan shekarar ne JMI take cika shekaru 46 cib da samun nasara, da kuma kafa JM a Iran, wadanne nasarori ne kasar ta samu a cikin wannan lokaci?.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto kadan daga cikin nasarorin da kasar ta samu daga ciki.
01-Tsawon shekarun da Iraniyawa suke rayuwa ya karu daga 55 zuwa 76.
02-JMI ta iran ce kasa ta farko a duniya, a saurin ci gaba, a mafi yawan fannonin ilmi, wannan bisa rahoton manya-manyan cibiyoyin bincike da sanin hakan a duniya.
03-A bangaren ci gaban kayakin aikin likita, da kiwon lafiya, JMI ce ta farko a yankin gabas ta tsakiya sannan ita ce ta 17TH a duk duniya, shi ma bisa rahotannin cibiyoyin bincike da gano hakan a duniya.
04-JMI tana daga cikin kasashen duniya da suka sami ci gaban a zo a gani a bangarorin masu muhimmaci na aikin likita, wanda ake kira da turanci (stem cells) da kuma radio pharmaceuticals).
05-JMI ta shiga cikin kasashe 12 a duniya wadanda suke da dukkan abinda ake bukata na fasahar shiga cikin sararin samaniya. Sannan ta shiga cikin kasashe 5 a duniya wadanda suke da fasahar amfani da makamashin nukliya.
06-JMI ce kasa ta 13TH a fagen karfin soje, na 5 a fagen fasahar kera jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa, sannan na 10 TH a fagen kera jirgen ruwa yaki mai tafiya karkashin ruwa, wato (subnerins ).
07-kungiyoyin wasanni motsa jiki mata kadai sun sami lambobin yabo kama daga zinari, azurka da tagulla har 7,961 a wasannin kasa da kasa. Sannan mata 335 ne suka zama alkalai a wasannin daban-daban a cikin shekara ta 2024 kadai.
Wannan kadannan Kenan daga irin ci gaban da JMI ta samu a cikin ci gaba a cikin al-amura daban daban a duniya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Cikin jadawalin GII na 2025, kasashe masu karanci da matsakaicin kudin shiga 17, sun taka rawar gani fiye da yadda aka yi hasashe, bisa matsayin ci gabansu, yayin da kasashen Afirka dake kudu da hamadar Sahara ke kan gaba, cikin kasashe mafiya samun ci gaban kirkire-kirkire, inda kasashen Afirka ta Kudu, da Senegal da Rwanda ke kan gaba a jerin kasashen shiyyar. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp