Mahaifi ya harbe ’yarsa har lahira saboda wallafa bidiyo a Tiktok
Published: 30th, January 2025 GMT
Hukumomi a birnin Quetta na Ƙasar Pakistan, sun kama wani mutum mai shekaru 50, kan zargin kashe ’yarsa mai shekaru 15 a duniya, saboda ta ƙi daina ɗora bidiyonta a kafar TikTok.
Rahoton ’yan sanda ya nuna cewar, mutumin ya dawo da iyalinsa daga Amurka zuwa Pakistan kwanan nan kafin aikata kisan.
Hisbah ta kama masoya kan yin aure ba tare da amincewar iyayensu ba Wata uku uami’o’i ba su da wutar lantarki —SSANUYa amsa laifin harbe ’yarsa, inda ya ce tana aikata abubuwan da ba su dace da addini da al’ada ba, ta hanyar saka bidiyo a TikTok.
An kuma kama ɗan uwansa kan zargin taimaka masa wajen aikata laifin.
Dukkaninsu sun nuna rashin amincewa da yadda matashiyar ke amfani da TikTok, wanda suka ce hakan ya saɓa wa tarbiyya mai kyau.
A halin yanzu, kotu ta bayar da umarnin tsare su na tsawon kwanaki 10 don ci gaba da bincike.
Irin wannan kisa ya zama ruwan dare a Pakistan, inda ’yan uwa ke kashe mata kan wani abu da suke ganin ya saɓa wa al’ada ko zai jawo wa danginsu abun kunya.
Wannan lamari ya tashi hankalin jama’a kan yadda ake amfani da kafofin sada zumunta da kuma tasirin al’adu a tsakanin iyalai.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Tsohon shugaban jam’iyyar PDP kuma tsohon ministan noma daga 2015 zuwa 2019, Audu Ogbeh, ya rasu a ranar Asabar, 9 ga Agusta, yana da shekaru 78 a duniya, kamar yadda iyalinsa suka tabbatar.
A cikin wata sanarwa, iyalan sun ce: “Ya rasu cikin kwanciyar hankali, ya bar mana gado na gaskiya, hidima da jajircewa ga kasa da al’umma. Mun sami kwanciyar hankali daga yadda ya shafi rayuka da kuma yadda ya kafa misali.”
Ko Nawa Za A Bani Ba Zan Iya Fitowa A Matsayin Kwarto Ko Dan Daudu A Fim Ba -Dan Asabe Olala Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – InuwaIyalan sun bayyana cewa za a sanar da yadda za a gudanar da jana’izarsa a nan gaba, tare da godewa abokai, da abokan aiki. Sun kuma roƙi a basu dama domin yin jimamin rasuwar baban nasu.
Rahoton LEADERSHIP ya nuna cewa Ogbeh, wanda ya shahara a siyasa, rubuce-rubuce da aikin gona, ya shugabanci PDP daga 2001 zuwa 2005 kafin ya zama minista a gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp