Aminiya:
2025-09-17@23:17:45 GMT

Hisbah ta haramta al’adun gargajiya yayin bukukuwan aure a Bauchi

Published: 26th, August 2025 GMT

Hukumar Hisbah ta haramta karuwanci da duk wasu munanan ɗabi’u da ake gudanarwa a otal-otal, wuraren casu da duk wasu cibiyoyin nishaɗi a Jihar Bauchi.

Babban Kwamishinan Hisbah, Barista Aminu Balarabe Isah, ya bayyana haka ne a yayin wani taron tattaunawa da masu otal-otal da wuraren shaƙatawa a Bauchi.

Trump ya yi barazanar korar Gwamnar Babban Bankin Amurka Jirgin kasa dauke da fasinjoji ya yi hastari a hanyar Kaduna-Abuja

Ya ce an haramta gudanar da al’adun gargajiya irin su Shadi, Sharo, Garaya da kuma shagulgulan wannan zamani kamar Kauyawa Day, Gala, DJ, Aloba da sauransu a bukukuwan aure.

Isah ya ce an ɗauki waɗannan matakan ne bayan samun korafe-korafe daga jama’a kan yadda abubuwa na rashin tarbiyya da tayar da fitina ke ƙaruwa a faɗin jihar.

Daga cikin dokokin da aka shimfiɗa akwai hana cakuɗuwar mata da maza, rawa tsakanin jinsi daban-daban tare da ƙananan yara.

Haka kuma an hana fatauci ko shan barasa da miyagun ƙwayoyi, bukukuwan birthday da duk wasu ababe na yaɗa fasadi da ka iya tayar da tarzoma.

Kazalika, sanarwar ta haramta caca, kallace-kallacen fina-finai na batsa a ko’ina da kuma jan hankali jama’a kan sanya tufafin da suka dace yayin zuwa wuraren nishaɗi.

Ya yi kira da cewa za a dakatar da duk wasu harkoki a wuraren shaƙatawa da zarar lokacin sallah ya yi.

Isah ya ce duk wanda bai kiyaye waɗannan ƙa’idoji ba, hukumar Hisbah za ta ɗauki matakin da ya dace a kansa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Bauchi karuwanci Sharo da duk wasu

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

 

Haka kuma, wannan na faruwa ne makonni biyu bayan yin garkuwa da Pastor Friday Adehi na Christian Evangelical Fellowship of Nigeria (CEFN) tare da wani abokin cocinsa bayan kammala wa’azi. Wannan ya kara nuna yadda matsalar garkuwa ke ta’azzara a yankin Kogi East.

 

A gefe guda, kungiyar lauyoyi ta Najeriya (NBA), reshen Idah, ta bukaci gwamnati a matakai daban-daban da ta dauki matakan gaggawa don kawo karshen satar mutane a jihar. Shugaban kungiyar, Barr. James Michael, ya ce yawaitar garkuwa a kan titunan yankin ya jefa rayukan jama’a cikin hatsari, don haka gwamnati ya kamata ta dauki tsauraran matakai domin kare lafiyar al’umma.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban
  • Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa