Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-07-31@00:39:08 GMT

Man City ta nace wa Guimaraes, Chelsea na son Rodrygo

Published: 10th, April 2025 GMT

Man City ta nace wa Guimaraes, Chelsea na son Rodrygo

Manchester City na nace kan buƙatar ɗanwasan tsakiya na Newcastle da Brazil Bruno Guimaraes, mai shekara 27, yayin da take shirin rabuwa da ɗanwasanta na Belgium Kevin de Bruyne, mai shekara 33. (UOL esporte – in Portuguese)

Chelsea a shirye take ta biya fam miliyan 102 kan ɗanwasan Real Madrid da Brazil Rodrygo, mai shekara 24.

 (Fichajes – in Spanish)

Manchester City na nazarin taya ɗanwasan tsakiya na AC Milan da Netherlands Tijjani Reijnders, mai shekara 26, kan tsakanin fam miliyan 42 zuwa fam miliyan 51 duk da ya sabunta kwangilar shi har zuwa 2030. (Calciomercato – in Italian)

Ana sa ran Everton za ta rasa ɗanwasan bayanta na Ingila Jarrad Branthwaite, mai shekara 22, yayin da Manchester United da Tottenham ke hamayya kan ɗanwasan. (Sun)

Chelsea da Newcastle na son ɗauko ɗanwasan Benfica da Girka Vangelis Pavlidis, mai shekara 26, kan fam miliyan 85 amma suna fuskantar hamayya daga Barcelona da Atletico Madrid. (Record – in Portuguese)

Arsenal da Liverpool na neman wani zaɓi maimakon Alexander Isak yayin da Newcastle ta dage cewa ba za ta sayar da ɗanwasan na gaba ba. (i paper)

Newcastle da Wolves da Brentford na hamayya kan golan Angers da Ivory Coast Yahia Fofana, mai shekara 24. (Football Insider)

Chelsea na kan gaba wajen buƙatar ɗanwasan tsakiya na Sunderland da Ingila Jobe Bellingham, mai shekara 19, duk da Manchester United da Arsenal da Tottenham da Brighton da Crystal Palace na ribibinsa. (Caught Offside)

Juventus za ta sayar da ɗanwasan tsakiya na Brazil Douglas Luiz, mai shekara 26, a bazara amma tana son kusan fam miliyan 34. (Tuttosport – in Italian)

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Wasanni ɗanwasan tsakiya na mai shekara fam miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

Yau Talata, kwamitin kwaskwarima da raya kasar Sin, ya fitar da kudin Sin RMB yuan miliyan 200, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 28, domin tallafawa wajen farfado da sassan birnin Beijing da bala’in ambaliyar ruwa ya shafa, musamman ma fannin sake gina ababen more rayuwar jama’a na sufuri, da samar da ruwan sha, da kiwon lafiya, da na hidimomin al’umma a gundumomin Miyun da Huairou, a kokarin ganin rayuwa ta dawo kamar yadda take a wuraren, an kuma dawo da ayyuka kamar yadda aka saba.

Ban da haka kuma, ma’aikatar kudi, da ma’aikatar lura da ayyukan gaggawa ta kasar sun zuba kudin Sin yuan miliyan 350, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 49 don tallafawa biranen Beijing, da Tianjin, da lardunan Hebei, da Shanxi, da Jilin, da Shandong, da Guangdong, da Shaanxi da jihar Mongolia ta Gida, ta yadda za su samu zarafin gudanar da ayyukan ceto, da rage radadin bala’u, da kuma taimakawa wadanda bala’in ya shafa. (Tasallah Yuan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa
  • Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China
  • Mutum miliyan 1.2 na fama da ciwon hanta a Kano
  • Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin Bai Wa Malaman Manyan Makarantun Nijeriya Rancen Miliyan 10
  • Za A Fara Bayar Da Bashin Miliyan 10 Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu