Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-15@06:13:00 GMT

Man City ta nace wa Guimaraes, Chelsea na son Rodrygo

Published: 10th, April 2025 GMT

Man City ta nace wa Guimaraes, Chelsea na son Rodrygo

Manchester City na nace kan buƙatar ɗanwasan tsakiya na Newcastle da Brazil Bruno Guimaraes, mai shekara 27, yayin da take shirin rabuwa da ɗanwasanta na Belgium Kevin de Bruyne, mai shekara 33. (UOL esporte – in Portuguese)

Chelsea a shirye take ta biya fam miliyan 102 kan ɗanwasan Real Madrid da Brazil Rodrygo, mai shekara 24.

 (Fichajes – in Spanish)

Manchester City na nazarin taya ɗanwasan tsakiya na AC Milan da Netherlands Tijjani Reijnders, mai shekara 26, kan tsakanin fam miliyan 42 zuwa fam miliyan 51 duk da ya sabunta kwangilar shi har zuwa 2030. (Calciomercato – in Italian)

Ana sa ran Everton za ta rasa ɗanwasan bayanta na Ingila Jarrad Branthwaite, mai shekara 22, yayin da Manchester United da Tottenham ke hamayya kan ɗanwasan. (Sun)

Chelsea da Newcastle na son ɗauko ɗanwasan Benfica da Girka Vangelis Pavlidis, mai shekara 26, kan fam miliyan 85 amma suna fuskantar hamayya daga Barcelona da Atletico Madrid. (Record – in Portuguese)

Arsenal da Liverpool na neman wani zaɓi maimakon Alexander Isak yayin da Newcastle ta dage cewa ba za ta sayar da ɗanwasan na gaba ba. (i paper)

Newcastle da Wolves da Brentford na hamayya kan golan Angers da Ivory Coast Yahia Fofana, mai shekara 24. (Football Insider)

Chelsea na kan gaba wajen buƙatar ɗanwasan tsakiya na Sunderland da Ingila Jobe Bellingham, mai shekara 19, duk da Manchester United da Arsenal da Tottenham da Brighton da Crystal Palace na ribibinsa. (Caught Offside)

Juventus za ta sayar da ɗanwasan tsakiya na Brazil Douglas Luiz, mai shekara 26, a bazara amma tana son kusan fam miliyan 34. (Tuttosport – in Italian)

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Wasanni ɗanwasan tsakiya na mai shekara fam miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje

Lamarin ya ci gaba da raguwa har zuwa 2024, inda yawan kudaden da ake kashewa a yawon ketare ya fadi da kaso 14 a matakin shekara-shekara zuwa dala biliyan 2.66.

Hakan na nuni da cewa ‘yan Nijeriya sun rage kashe kudaden da suke kashewa kan safarar jiragen sama da dala biliyan 1.12 ko kuma kashi 30 cikin dari a cikin shekaru biyun.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
  • ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2
  • De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
  • MDD: Adadin ‘Yan Gudun Hijira A Duniya Ya Kai Miliyan 122
  • NAJERIYA A YAU: June 12: Me Ranar Demokradiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya?
  • Kasashen Iran Masar Da Kuma Omman Sun Gudanar Da Taro A Oslo