Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-30@19:03:11 GMT

Man City ta nace wa Guimaraes, Chelsea na son Rodrygo

Published: 10th, April 2025 GMT

Man City ta nace wa Guimaraes, Chelsea na son Rodrygo

Manchester City na nace kan buƙatar ɗanwasan tsakiya na Newcastle da Brazil Bruno Guimaraes, mai shekara 27, yayin da take shirin rabuwa da ɗanwasanta na Belgium Kevin de Bruyne, mai shekara 33. (UOL esporte – in Portuguese)

Chelsea a shirye take ta biya fam miliyan 102 kan ɗanwasan Real Madrid da Brazil Rodrygo, mai shekara 24.

 (Fichajes – in Spanish)

Manchester City na nazarin taya ɗanwasan tsakiya na AC Milan da Netherlands Tijjani Reijnders, mai shekara 26, kan tsakanin fam miliyan 42 zuwa fam miliyan 51 duk da ya sabunta kwangilar shi har zuwa 2030. (Calciomercato – in Italian)

Ana sa ran Everton za ta rasa ɗanwasan bayanta na Ingila Jarrad Branthwaite, mai shekara 22, yayin da Manchester United da Tottenham ke hamayya kan ɗanwasan. (Sun)

Chelsea da Newcastle na son ɗauko ɗanwasan Benfica da Girka Vangelis Pavlidis, mai shekara 26, kan fam miliyan 85 amma suna fuskantar hamayya daga Barcelona da Atletico Madrid. (Record – in Portuguese)

Arsenal da Liverpool na neman wani zaɓi maimakon Alexander Isak yayin da Newcastle ta dage cewa ba za ta sayar da ɗanwasan na gaba ba. (i paper)

Newcastle da Wolves da Brentford na hamayya kan golan Angers da Ivory Coast Yahia Fofana, mai shekara 24. (Football Insider)

Chelsea na kan gaba wajen buƙatar ɗanwasan tsakiya na Sunderland da Ingila Jobe Bellingham, mai shekara 19, duk da Manchester United da Arsenal da Tottenham da Brighton da Crystal Palace na ribibinsa. (Caught Offside)

Juventus za ta sayar da ɗanwasan tsakiya na Brazil Douglas Luiz, mai shekara 26, a bazara amma tana son kusan fam miliyan 34. (Tuttosport – in Italian)

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Wasanni ɗanwasan tsakiya na mai shekara fam miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi

Wani wanda ake zargi da safarar sassan jikin ɗan Adam ya shaida wa jami’an tsaro cewa ya shafe sama da shekara 10 yana sayar da sassan jikin mutum don samun kuɗi.

Dubun mutumin sun cika ne a ranar Asabar din da ta gabata inda sojoji suka kama shi a yankin Kulanla Odomoola da ke Jihar Ogun.

A furucinsa da ya amsa laifin, wanda ake zargin ya amince da sayar da sassan jikin mutum ga masu buƙata don samun kuɗin shiga.

“Na dogara ne da sayar da sassan jikin mutum tsawon shekaru 10 da suka gabata. Yawancin sassan da nake sayarwa ina tono su ne daga sabbin kaburbura a makabartu, yayin da wasu kuma nake samun su daga gawarwakin da aka watsar a gefen hanyoyi,” in ji shi.

Aminu Bayero ya naɗa Sanusi a matsayin Galadiman Kano Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji laifi ne — Janar Chibuisi NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”

Wanda ake zargin, wanda ya amsa laifinsa ga wani taron jama’a da suka yi yunƙurin kashe shi kafin sojoji su cece shi, ana zargin yana kan hanyarsa ne na kai wani sassan jiki ga wani mai siye lokacin da aka kama shi.

Daga nan aka miƙa wanda ake zargin ga ’yan sanda a yankin Noforija don ƙarin bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.

Laftanar Kanar Olabisi Olalekan Ayeni, Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Sojin Najeriya ta 81, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya bayan kama wanda ake zargin daga baya an miƙa shi tare da kayayyakin da aka samu a wurinsa, ga ’yan sandan Najeriya don ƙarin bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.

“Sojojin sun ceto wanda ake zargin daga wani taron jama’a da suka yi yunƙurin kashe shi,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
  • Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi