Mai Martaba Sarkin Kano 16 Ya Nada Mannir A Matsayin Sabon Galadiman Kano
Published: 10th, April 2025 GMT
A ranar Talata ne mai martaba Sarkin Kano Malam Mohammad Sunusi II ya amince da nadin Alhaji Mannir Sunusi a matsayin sabon Galadiman Kano.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban ‘yan jarida da yada labarai na masarautar Kano, Saddam Nasir Na’ando ya fitar, kuma ya mika wa gidan rediyon Najeriya da ke Kano.
Haka kuma Sarki Sunusi II ya amince da nadin Alhaji Kabiru Tijjani Hashim zuwa Wamban Kano.
Sauran nada nade sun haɗa da “Alhaji Mahmoud Ado Bayero ya tashi daga Tafidan Kano zuwa Turakin Kano da Adam Sanusi yanzu ya zaman Tafidan Kano sai kuma Ahmed Abbas Sanusi ya zamaYariman Kano.
Sanarwar ta kara da cewa wadannan nade-naden sun fara aiki ne nan take, a wani bangare na kokarin da Masarautar Kano ke yi na karfafa shugabancin gargajiya da kuma adana kayayyakin tarihi.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sarki
এছাড়াও পড়ুন:
Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah
Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya reshen Jihar Benuwe, a ranar Alhamis, ta bayyana cewa aƙalla shanu 340 na mambobinta ne aka sace a cikin watan Yuli na 2025.
Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren ƙungiyar na jiha, Ibrahim Galma ya fitar kuma aka rabawa manema labarai a Makurdi.
Tinubu ya tsawaita wa’adin aikin shugaban hukumar Kwastam Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a JigawaA cewar sanarwar, lamarin ya faru ne a garin Agatu da wasu sassan Ƙaramar hukumar Guma da ke Jihar Benuwe.
Galma ya kuma yi zargin cewa, ɓarayin shanu da ke afkawa jama’a a Ƙaramar hukumar Agatu sun faɗaɗa hare-harensu zuwa sassan Jihar Kogi.
“A ranar 19 ga Yuli, 2025 wasu da ake zargin ’yan ƙabilar unguwar Eguma ne a ƙaramar hukumar Agatu sun sace shanu 73 na wani Sale Abubakar (makiyayi Fulani), kuma har ya zuwa yanzu ba a ƙwato shanun ba.
“A ranar 21/7/2025 wani gungun masu aikata laifuka daga unguwar Agatu sun yi awon gaba da shanu 80 na Ardo Sarkin Fulanin Bagana, an yi awon gaba da shanun ne a Jihar Kogi, kusa da kan iyaka da ƙaramar hukumar Agatu ta Jihar Benuwe.
Ɓarayin sun kwashe shanun zuwa ƙauyukan Agatu. Daga baya kuma, an ƙwato shanu 30 daga cikin 80 a Agatu, inda ba a iya gano 50 ba.
“A ranar 24 ga Yuli, 2025 wasu miyagu matasa ‘yan garin Agatu sun yi awon gaba da wasu shanu 213 na Garah Mobaba, hakan kuma ya faru ne a kan iyaka tsakanin Jihar Kogi da Ƙaramar hukumar Agatu ta Jihar Benuwe, haka kuma lamarin na faruwa a wasu sassan Ƙaramar hukumar Guma ta Jihar Benuwe, inda aka samu rahotannin sace-sacen shanu da kuma kashe-kashen makiyaya.”
Shanun mallakin Sale Abubakar (makiyayin Fulani), kuma har ya zuwa yanzu, ba a ƙwato shanun da aka sace ba.