An Horas Da Mata 600 Kan Abincin Yara Mai Gina Jiki A Jigawa
Published: 31st, July 2025 GMT
A wani yunkuri na yaki da rashin abinci mai gina jiki da kuma karfafa tattalin arzikin mata a jihar Jigawa, Gwamna Umar Namadi ya jagoranci bikin yaye mata 600 da suka samu horo kan yadda ake sarrafa abincin yara mai gina jiki daga kayayyakin da ake samarwa a gida, wanda aka fi sani da “Tom Brown”.
Malam Umar Namadi ya bayyana wannan shiri a matsayin wata dabara ta cikin gida da aka kirkira domin shawo kan matsalolin rashin abinci mai gina jiki a tsakanin yara, da kuma karfafa tattalin arzikin mata.
“Muna matukar godewa Allah da ya ba mu hikima da basira don kirkirar wannan tsari wanda zai taimaka mana mu cimma manufofi da dama a lokaci guda.” In ji shi.
“Bayan bai wa wadanda aka horar damar samun ingantacciyar hanyar dogaro da kai, wannan kuma wata babbar dabara ce wajen yaki da rashin abinci mai gina jiki a cikin yara. Hakan kuma zai taimaka wajen hana matsalolin nakasa a kwakwalwa, domin kare damar girman yaron yadda ya dace.”
Gwamnan ya jaddada cewa Tom Brown, wanda wasu ke kira da Kwashpap, an tabbatar da ingancinsa wajen magance matsalar rashin matsakaicin abinci mai gina jiki (Moderate Acute Malnutrition – MAM) ta hanyar hadin kayan gida kamar gero, gyada da wake.
Ya kara da cewa wannan shiri na da cikakken daidaito da manufofin gwamnatin jihar na bunkasa abinci mai gina jiki, wanda ya fara haifar da sakamako mai kyau.
A cewarsa, kowace daga cikin matan 600 da suka amfana da shirin ta samu kayan fara sana’a da suka hada da injin rufe roba da kayan masarufi domin farawa da sarrafa Tom Brown a matakin gida.
Namadi ya bayyana cewa kananan hukumomi da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a fadin jihar za su hada gwiwa domin tabbatar da amfani da kuma shigar da wadannan kayayyaki cikin shirye-shiryen inganta abincin yara.
Ya ce, horar da wadannan mata 600 wani bangare ne na kokarin gwamnati wajen hanzarta samun ci gaba a fannin kula da rayuwar al’ummar, da ingantacciyar lafiyar yara.
Gwamna Namadi ya kuma sake jaddada kudirin gwamnatinsa na rage dogaro da kayan abinci masu tsada da ake shigowa da su daga kasashen waje, ta hanyar bunkasa hanyoyin cikin gida masu saukin samu da kuma arha.
Ya sanar da cewa jihar Jigawa na cikin jerin jihohin da ke amfana da shirin ANRiN na Bankin Duniya, wanda ke mayar da hankali kan kara samun damar kula da lafiyayyen abinci ga mata da yara ‘yan kasa da shekaru biyar.
“Babban burin wannan shiri shi ne kara yawan amfani da ingantattun hanyoyin kula da abinci ga mata masu juna biyu da masu shayarwa da kuma yara ‘yan kasa da shekaru biyar. Wannan yana da nasaba da hangenmu cewa shirin ANRiN zai taka rawar gani wajen hanzarta ci gabanmu ta bangaren samar da abinci mai gina jiki ga yara.”
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
A yayin da ake ci gaba da cece-kuce kan kalaman Shugaban Amurka Donald Trump da ke zargin gwamnatin Nijeriya da watsi da batun kisan Kiristoci a ƙasar, Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta bayyana cewa ta fara shirin kai farmaki a Nijeriya.
Sakataren Ma’aikatar, Pete Hegseth, ne ya tabbatar da hakan cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Asabar, yana mai cewa ma’aikatarsa “na shirye-shiryen ɗaukar mataki” bayan umarnin da Trump ya bayar.
Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya“Muna shirye-shirye don ɗaukar mataki a Nijeriya. Idan gwamnatin Nijeriya ba ta kare Kiristoci ba, za mu kai hari, mu kawar da ‘yan ta’addan Musulmai da ke aikata wannan ta’asar,” in ji Hegseth.
Trump dai ya yi wannan barazanar ne a cikin wani saƙo da ya wallafa a Truth Social, inda ya ce Amurka za ta dakatar da duk tallafin da take bai wa Nijeriya, kuma tana iya “shiga ƙasar da ƙarfin soji domin share ‘yan ta’addan da ke kashe Kiristoci.”
“Idan gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, Amurka za ta dakatar da duk wata tallafi, kuma mai yiwuwa ta shiga wannan ƙasar, ta cike da ƙarfin gwiwa domin kawar da ’yan ta’addan Musulmai masu zafin kishin addini,” in ji Trump.
Ya kuma gargaɗi gwamnatin Nijeriya da ta gaggauta ɗaukar mataki, yana cewa idan Amurka ta kai farmaki “za ta yi shi cikin sauri, da tsananin ƙarfi, da gamsuwa.”
Lamarin na zuwa ne kwana guda bayan Trump ya mayar da Nijeriya cikin jerin ƙasashen da za a sanyawa ido, yana zargin cewa “ana yi wa Kiristoci kisan gilla” a hannun ƙungiyoyin Musulmi masu tsattsauran ra’ayi.
Sai dai a martanin da ya mayar, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce Nijeriya tana nan daram a matsayin ƙasa mai dimokuraɗiyya wadda kundin tsarin mulkinta ke tabbatar da ‘yancin yin addini da haƙuri tsakanin mabambantan addinai.
“Tun daga shekarar 2023, gwamnatinmu tana gudanar da tattaunawa sosai da shugabannin addinai na Kiristanci da Musulunci, tare da ci gaba da magance matsalolin tsaro da ke shafar ‘yan ƙasa daga addinai da yankuna daban-daban,” in ji Tinubu.
A cewar mai ba wa Tinubun shawara na musamman kan yaɗa manufofi, Daniel Bwala, za a yi ganawa tsakanin Shugaba Tinubu da Shugaba Trump “a cikin kwanaki kaɗan masu zuwa” domin tattaunawa da warware wannan saɓanin fahimta.