Jihar Sakkwato ta ciyo bashin N70.4bn domin inganta kiwon lafiya
Published: 2nd, August 2025 GMT
Bankin Raya Ci-gaban Afirka (AfDB) ya amince da ba wa Gwamnatin Jihar Sakkwato bashin Naira biliyan 70.4 domin inganta fannin kiwon lafiya.
Wannan shiri na da nufin bunƙasa fannin kiwon lafiya da ingancinsa, da kuma cike giɓin da ake da shi a ɓangaren a Jihar Sakkwato, a cewar AfDB ta bayyana a cikin wata sanarwa ranar Juma’a.
Rahotanni na nuni da cewa, yaro ɗaya cikin kowane yara 20 ne akale yi wa allurar rigakafi cikakke a Jihar Sakkwato a, a yayin da adadin mutuwar jarirai ya kai 104 daga cikin 1,000 a Jihar.
Ƙasa da kashi 14 cikin 100 na cibiyoyin lafiya a jihar ne suke da kayan aiki masu aiki, kuma likita ɗaya ne kawai ke kula da mutum 8,285, wanda ya gaza abin da Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayar na likita 1 ga 1,000 mutum.
Har yanzu ana fama da cutar kwalara a Najeriya – UNICEF PDP ta mutu murus a Kano — Shugaban NNPPKuɗaɗen da bankin ya ware za su tallafa wa samar kayan aikin kula da lafiya masu inganci a matakai uku na kula da lafiya a Jihar Sakkwato.
Wannan ya haɗa da gina sabon asibitin koyarwa mai gado 1,000, da manyan asibitoci na yankuna uku masu jimillar gadaje 450, da kuma cibiyoyin kiwon lafiya guda shida da aka tsara a domin kuka da al’ummomin karkara.
Aikin ya kuma haɗa da gyaran cibiyoyin horar da ma’aikatan lafiya da ƙirƙirar sabon ma’ajiyar magunguna ta zamani.
Darakta-Janar na Ofishin AfDB a Najeriya, Abdul Kamara, ya ce, “Wannan rancen na nuna yadda muke jajircewa wajen aiki tare da gwamnati don magance giɓin kayan kiwon lafiya a Najeriya, tare da gina cibiyoyin kula da lafiya masu ƙarfi da suka dace da tsari na yanayi.
“Ta hanyar ƙarfafa kayan aikin lafiya a Jihar Sakkwato, muna gina fata da hanyoyin samun kyakkyawan sakamako ga miliyoyin ’yan Najeriya.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kiwon Lafiya lafiya Sakkwato a Jihar Sakkwato kiwon lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Yadda kasashen yammacin duniya suka ki sauke nauyin dake wuyansu, ya danne wa kasashe masu tasowa hakkinsu. Misali, a lokacin da ake samun bazuwar annobar COVID-19, dimbin kasashen yamma sun yi ajiyar alluran rigakafi a gida, inda suka hana fitar da su zuwa ketare, da musayar fasahohi masu nasaba da su. Sai dai a lokacin, hukumomi masu kula da harkokin kasa da kasa, kamar su Hukumar Lafiya ta Duniya, da Majalisar Dinkin Duniya dukkansu sun kasa tilasta musu sauya manufofinsu. Wannan tsarin kasa da kasa, idan mun bar shi haka ba tare da wani sauyi ba, to, wata rana za mu ga an koma tsarin zalunci na zamanin mulkin mallaka, wanda zai yi barazana ga hakkin rayuwa, da raya kai na al’ummar kasashe masu tasowa. Ta haka za mu san cewa gyara ya riga ya wajaba.
Saboda haka, shawarar inganta jagorancin duniya ta zama wani abun dake biyan bukatun dake akwai a duniyarmu. Wannan ya sa ta samun karbuwa a tsakanin kasashe masu tasowa, musamman ma kasashen Afirka. Inda shahararren dan jarida a Najeriya Lawal Sale, ya rubuta a cikin wani sharhinsa cewa, “Wannan shawara za ta haifar da karin kwanciyar hankali, da tabbas a duniyarmu mai cike da tashin hankali, musamman ma a nahiyar Afirka.” Kana a nasa bangare, Paul Frimpong, wani shehun malami dan kasar Ghana, ya ce shawarar nan “tana tabbatar da cewa tsarin jagorancin duniya ba zai ci gaba da zama karkashin mallakar wasu kasashe masu karfi ba.” Kana dan jaridar kasar Lesotho, Silence Charumbira, ya ce shirin na baiwa kananan kasashe damar zama masu hakikanin ‘yancin kai.
Ta wannan shawara ta inganta jagorancin duniya, za mu iya kara fahimtar halayyar kasar ta Sin. Ko da yake wani yanayin da duniyarmu ke ciki shi ne dishewar tauraron kasashen yamma, amma duk da haka, kasar Sin ba ta neman yin koyi da kasashen yamma wajen yin babakere a duniya. Tana neman gyara, da inganta tsare-tsaren kula da harkokin duniya, ta yadda za ta tabbatar da moriyar dukkan kasashe, musamman ma kasashe masu tasowa, maimakon kafa wani sabon tsari da ya saba wa tsarin kasa da kasa na yanzu. Dalilin da ya sa haka shi ne babban burin kasar Sin ta fuskar diflomasiyya, shi ne kafa al’umma mai kyakkyawar makomar bai daya ga bil’adama, da kokarin tabbatar da ci gaban harkokinsu na bai daya.
Yayin da karin kasashe ke nuna goyon bayansu ga shawarar kula da al’amuran duniya da kasar Sin ta gabatar, tabbas za mu shaida hadin gwiwar karin mutane a duniya don neman wanzar da adalci, abin da zai haifar da damar tabbatar da daidaito da adalci a duniyarmu. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp