Ya nuna rashin jin daɗinsa da rabon ayyukan tituna kamar yadda aka samu a cikin wata sanarwa da ma’aikatar ayyuka ta fitar a watan Mayun 2025, wanda a cewarsa, an ware Naira tiriliyan 1.394 wa yankin Kudu-maso-Yamma, yayin da ɗaukacin yankin Arewa-maso-gabas suka samu Naira biliyan 30, sai kuma yankin Arewa-maso-Yamma Naira 105 biliyan.

“Rashin tsaro ya zama babban abin damuwa, ƴan fashi, tada ƙayar baya, da kuma garkuwa da mutane na ci gaba da wanzuwa a sassan Arewa da dama, inda jihohi kaɗan ne kamar Kaduna da Bauchi suka samu kwanciyar hankali,” in ji shi.

Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta fito da manufofin siyasa don kawo ƙarshen rikicin.

ɗalhatu ya kuma soki manufofin gwamnatin tarayya kan harkokin noma, inda ya ce sun jawo ce-ce-ku-ce a harkar noma a cikin gida, sakamakon ƙaruwar shigo da abinci daga ƙasashen waje, lamarin da ya sa aka rufe wasu masana’antun shinkafa a yankin. Ya yi gargaɗin cewa irin waɗannan manufofin suna raunana ƙashin bayan tattalin arzikin yankin.

Ya ƙara da nuna damuwa game da giɓin da ake samu na wutar lantarki a yankin, ya kuma buƙaci shugaba Tinubu ya kafa dokar ta-ɓaci a fannin wutar lantarki. Ya buƙaci a gaggauta kammala wasu muhimman ayyukan makamashi kamar madatsar ruwa ta Mambilla da bututun iskar gas daga Abuja zuwa Kaduna da Kano, waɗanda a cewarsa, suna da matuƙar muhimmanci ga makomar masana’antun Arewacin Nijeriya.

A ɓangaren ilimi kuwa, ɗalhatu ya buga misali da bayanan bankin duniya da ke nuni da cewa kashi 80 cikin 100 na yara miliyan 20 na Nijeriya da aka ƙiyasta ba sa zuwa makaranta ƴan Arewa ne. Ya buƙaci gwamnatin Tinubu da ta sake ƙaddamar da shirin ilimi na bai ɗaya (UBE) tare da himma wajen da mai da hankali kan ilimi kyauta.

Ya kuma yi tir da taɓarɓarewar ababen more rayuwa na kiwon lafiyar al’umma, da sake ɓullar cututtuka, da yawaitar shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin matasan Arewa, inda ya yi kira da a gaggauta ɗaukar matakin na gwamnatin tarayya a fannonin kiwon lafiya na matakin farko, da sarrafa magunguna, da samar da ruwan sha.

Ya bayyana tafiyar hawainiyar da ake yi a kan aikin kamfanin tama da ƙarafa na Ajaokuta a matsayin abin takaici, ya kuma yi gargaɗin a kan dogaro da ƙawancen jama’a da masu zaman kansu (PPP) fiye da kima wajen samar da irin waɗannan kadarorin.

ɗalhatu ya zargi gwamnatin Tinubu da nuna ɓangaranci, son zuciya, da rashin sanin halin da Arewa ke ciki.

Hausawa na Karin magana cewa “Gyara kayanka ba ya zama sauke mu raba,”. Ya ba da shawarar sake farfaɗo da kwamitin tuntuɓar gwamnatin tarayya domin zurfafa tattaunawa.

Sai dai kuma a wani martani da ya mayar, Shugaban ƙungiyar gwamnonin jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ce Shugaba Tinubu ya cika alƙawuran da ya ɗaukar wa Arewa kuma yana ci gaba da aiwatar da ajandarsa ta ‘Renewed Hope’

Gwamna Yahaya ya ce tarurrukan da suka haɗa da ƙungiyar SABMF na da matuɗar muhimmanci wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya da tabbatar da bin doka da oda, amma ya jaddada cewa shaidun da ke ƙasa na nuna ci gaba mai ma’ana a sassa daban-daban na faɗin yankin.

“Lokacin da Bola Ahmed Tinubu ya yi yaƙin neman zaɓe a faɗin Arewa a shekarar 2023, ya yi alƙawuran da ya dace, a yau muna ganin cikarsu ta hanyar ayyukan da aka kammala da kuma waɗanda ke ci gaba da gudana,” in ji Yahaya, inda ya ƙara da cewa an samu gagarumin ci gaba a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna zuwa Kano, layin dogo na Kano-Katsina-Maradi, gyaran matatar mai ta Kaduna, da kuma bunƙasa man fetur na Kolmani.

Yahaya lauded the newly established Ministry of Liɓestock ɗeɓelopment, calling it a major step towards modernising pastoral systems in the region.

Ya kuma bayyana cewa an samu ci gaba a harkokin tsaro a jihohi da dama, inda ya yi nuni da yadda aka kawar da shugabannin ta’addanci da ƴan fashi sama da 300.

Yahaya ya yaba wa sabuwar ma’aikatar kula da kiwon dabbobi da aka kafa, inda ya bayyana hakan a matsayin wani babban mataki na zamanantar da tsarin kiwo a yankin.

A cewarsa, sabbin ababen more rayuwa na tituna da na dogo, inganta kiwon lafiya, ayyukan noma, da kuma ɗaukar matakan da suka dace a fannin ilimi, musamman kan matsalar Almajirai da yaran da ba su zuwa makaranta, na nuni da dabarun da gwamnatin tarayya ta yi domin ɗaukaka yankin.

A nasa jawabin, Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Sanata George Akume, wanda ya wakilci Shugaba Tinubu, ya nanata ƙudurin Shugaban ƙasa na samar da ci gaba mai amfani, yana mai bayyana cewa “ba wani yanki da za a barI baya.

Akume, wanda ya jagoranci tawagar ministoci, shugabannin hukumomi, da mataimakan shugaban ƙasa a wajen taron, ya ce ajandar Renewed Hope an kafa ta ne a kan ginshiƙan daidaito, shiga tsakani, da kuma gaskiya.

Ya zayyana muhimman ayyukan da ake gudanarwa a Arewa da ma faɗin ƙasar nan.

Ya ambaci babbar hanyar Legas zuwa Calabar, babbar titin Sokoto-Badagry, Kano-Maradi da Fatakwal-Maiduguri, da ayyukan gina gidaje da na noma da dama a matsayin shaida na ayyukan gwamnati.

Akan sake fasalin tattalin arziki, Akume ya ce cire tallafin man fetur da kuma haɗewar farashin canji abu ne mai zafi amma an yi su a matakan da suka dace domin daidaita tattalin arzikin ƙasar.

Ya bayyana cewa an riga an bayar da sama da Naira biliyan 53 ta tsarin bayar da lamunin rancen ɗalibai don cin gajiyar ɗaliban manyan makarantu sama da 400,000 a faɗin ƙasar nan.

Akume ya ce Tinubu ya ɗau turbar kai Nijeriya matsayin da ya yi alƙawri, inda ya ƙara da cewa.

“Zan buƙaci ƴan siyasa daga yankin Arewa da su jira har zuwa 2031. Kada ku shiga ƙungiyar da za ta haifar da lalata ci gaba daban-daban da Shugaba Tinubu ya samu. Shugaban ƙasa ya taɓa dukkan sassan ƙasar nan da kowane ɗan ƙasa.”

Ya kuma jinjinawa marigayi Firimiyan Arewacin NIjeriya, Sir Ahmadu Bello, inda ya bayyana shi a matsayin ɗan siyasa mai wakiltar haɗin kai, hangen nesa, da gudanar da mulki na bai ɗaya. Ya kuma yaba da gudunmawar da wasu fitattun shugabannin Arewa suka bayar da suka haɗa da Cif Solomon Lar da Malam Adamu Ciroma.

Waɗanda suka yi wa ƙasa hidima da tsaffin gwamnonin Arewa, ministoci, masu ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro (NSA) Malam Nuhu Ribadu, Shugaban ma’aikatan Fadar Shugaban ƙasa Sanata George Akume, shugabannin gargajiya, shugabannin MɗA na tarayya, shugabannin tsaro, da shugabannin masana’antu ne suka hallarci taron.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gwamnatin tarayya

এছাড়াও পড়ুন:

ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta

Jam’iyyar APC reshen jihar Zamfara, ta bayyana matukar damuwarta kan yadda matsalar tsaro ke kara ta’azzara a jihar, inda ta bayyana hakan a matsayin abin ban tsoro da rashin fahimta.

 

A wata sanarwa dauke da sa hannun sakataren yada labarai na jam’iyyar, Yusuf Idris Gusau, jam’iyyar APC ta ce yawaitar ‘yan fashi da makami, garkuwa da mutane da kashe-kashe a Zamfara ya kai matakin da ba a taba ganin irinsa ba, yayin da ta zargi gwamnatin jihar a karkashin Gwamna Dauda Lawal da nuna halin ko in kula.

 

A cewar sanarwar, jam’iyyar ta damu matuka da wani faifan bidiyo na baya-bayan nan inda aka ga sama da mutane 200 mazauna Kaura Namoda suna rokon a taimaka musu biyo bayan sace su da wasu da ake zargin ‘yan fashi ne suka yi.

 

Jam’iyyar APC ta kuma soki gwamnatin kan abin da ta bayyana a matsayin rashin mayar da martani da kuma rashin cika alkawarin da ta dauka na kare rayuka da dukiyoyi a lokacin yakin neman zabe.

 

Jam’iyyar ta tuna cewa, Gwamna Dauda Lawal ya yi kakkausar suka ga gwamnatocin baya kan rashin tsaro, ya kuma yi alkawarin kawo karshen ‘yan fashi a cikin watanni biyun farko na mulki.

 

Sai dai jam’iyyar APC ta bayyana cewa a maimakon haka lamarin ya tabarbare, inda a kullum ake ta yin garkuwa da mutane da kashe-kashe a sassan jihar.

 

Sanarwar ta kuma bayyana wasu muhimman hanyoyi da suka hada da Gusau –Talata Mafara –Tureta, da Mayanchi –Anka –Gummi – wadanda a yanzu suke da hatsarin tafiya ba tare da rakiyar sojoji ba.

 

Jam’iyyar ta kara da cewa, hanyar Gusau zuwa Kaura Namoda ta zama daya daga cikin mafi hadari, inda a kullum ake samun rahotannin sace-sacen mutane da kashe-kashe.

 

Da take ba da misalin harin baya-bayan nan da aka ce an kashe mutane 38 da aka yi garkuwa da su daga unguwar Banga da ke karamar hukumar Kaura Namoda bayan an biya kudin fansa, jam’iyyar APC ta ce gwamnatin jihar ta yi shiru duk da cewa ana ci gaba da samun tashin hankali a tsakanin mazauna yankin.

 

A yayin da wasu sabbin rahotanni suka ce an sace sama da mutane 200 a cikin makon nan, jam’iyyar APC ta sake yin kira ga gwamnatin tarayya da ta kafa dokar ta-baci a Zamfara domin ba da damar aikewa da karin sojoji da kuma aiwatar da sahihin matakan tsaro.

 

Jam’iyyar ta zargi gwamnatin jihar da gazawa yadda ya kamata ga hukumomin tsaro na tarayya tare da zargin gwamnan da wasu mataimakansa kan harkokin yada labarai sun fito fili suna sukar ayyukan sojoji a jihar.

 

“Haka zalika ta yi Allah-wadai da rufe kasuwanni da hana zirga-zirgar ababen hawa, inda ta bayyana su a matsayin matakan da ba su da inganci da suka yi illa ga tattalin arzikin jihar.

 

Jam’iyyar APC ta kuma yi kakkausar suka kan tafiye-tafiyen da Gwamna Lawal ya yi a kasashen waje, inda ta yi zargin cewa yana halartar bukukuwan ‘yan uwa na kashin kansa yayin da mazauna gida ke kokawa da rashin tsaro.

 

Jam’iyyar ta yabawa bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara karkashin jagorancin Bashar Aliyu Gummi bisa jajircewar da ta yi wajen ganin ta yi wa bangaren zartarwa hukunci kan al’amuran da suka shafi rashin tsaro da cin hanci da rashawa.

 

A karshe jam’iyyar APC ta jajantawa iyalan wadanda rikicin ya shafa tare da yin addu’ar Allah ya dawo mana da zaman lafiya a jihar Zamfara da Najeriya baki daya.

 

REL/AMINU DALHATU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Har yanzu ana fama da cutar kwalara a Najeriya – UNICEF
  • Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa
  • Iran ta yi watsi da zargin gwamnatocin turai na yunkurin kashe wasu mutane a kasashensu
  • Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka
  • Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya
  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
  • Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF