Aminiya:
2025-11-03@01:57:23 GMT

An ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a Kebbi

Published: 1st, August 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Kebbi ta ce ta ceto wasu mutane uku da aka yi garkuwa da su, bayan sun yi artabu da wasu da ake zargin sun yi garkuwa da su a wani mummunan musayar wuta da aka yi a tsaunin Shanga.

Waɗanda aka yi garkuwan da su sun haɗa da: Muhammad Nasamu Namata mai shekara 25, da Gide Namata mai shekara 20 da Hamidu Alhaji Namani mai shekara 35.

INEC za ta fara rajistar ƙuri’a a ranar 18 ga Agusta Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansaninta a Kebbi

An  yin garkuwa da su ne a safiyar ranar 27 ga watan Yuli, 2025, lokacin da masu garkuwa da mutane ɗauke da makamai suka mamaye ƙauyen Sangara da ke Ƙaramar hukumar Shanga.

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, CSP Nafiu Abubakar ya fitar a ranar Juma’a, ya bayyana cewa wannan ceton ya biyo bayan ɗaukar matakin gaggawa da jami’an ’yan sanda na yankin Shanga suka ɗauka, wanda ya haɗa tawagar jami’an tsaro da suka haɗa da jami’an sojojin Najeriya, jami’an tsaro na Civil Defence da ’yan banga na yankin da mafarauta.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Rundunar ta bi sahun masu garkuwa da mutanen ne zuwa tsaunin Shanga, inda aka yi musayar wuta a tsakaninsu, musayar wutar ta sa jami’an tsaro suka yi nasara kan masu garkuwar.

Daga nan masu garkuwan suka tsere zuwa cikin daji da raunukan harbin bindiga.

“An kuɓutar da waɗanda aka yi garkuwa da su ne ba tare da wani rauni ba, a ranar Alhamis, 31 ga Yuli, 2025 da misalin ƙarfe 3:30 na rana kuma a halin yanzu suna samun kulawar likita kafin su sake haɗuwa da iyalansu.”

Ya ce, Kwamishinan ’yan sanda, CP Bello M. Sani ya yaba wa jarumtaka da ƙwarewa na rundunar, inda ya buƙaci dukkan hukumomin tsaro su ci gaba da haɗa kai. Ya nanata ƙudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi a Jihar Kebbi.

Kwamishinan ya kuma yi kira ga al’ummar yankin da su sanya ido tare da kai rahoto ga jami’an tsaro mafi kusa domin ɗaukar matakin gaggawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: masu garkuwan da mutane da aka yi garkuwa yi garkuwa da su jami an tsaro masu garkuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?

Shugabannin Rundunar tsaro da Tinubu ya sallama sun hada da shugaban rundunar tsaro ta kasa Janar Christopher Musa da shugaban sojojin ruwa, Emmanuel Ikechukwu Ogalla da shugaban sojojin sama Hassan Abubakar.

Wadanda suka maye gurbin su da idanu ya koma kan hobbasar kwazon da za su nuna su ne shugaban rundunar tsaro Olufemi Oluyede, shugaban sojojin kasa Waidi Shaibu, shugaban sojojin ruwa Idi Abbas da shugaban sojojin sama S.K Aneke sai kuma shugaban rundunar leken asiri, EAP Undiendeye wanda ya ci-gaba da rike kujerar sa.

Yan Nijeriya sun jima suna kukan duk da kwarewa da gogewar jami’an sojojin Nijeriya da irin makuddan kudaden da gwamnati ke kashewa a sha’anin tsaro a kowace shekara amma matsalar kullum gaba- gaba take kara yi.

Yankuna da dama a Nijeriya musamman a Arewa- Maso- Yamma, Arewa- Maso- Gabas da Arewa ta tsakiya sun zama lahira kusa a bisa ga yadda barayin daji ke garkuwa da mutane, kone garuruwa da yi wa jama’a kisan kare dangi.

Gagarumar matsalar wadda tuni ta zama tamkar ruwan dare a tsayin shekaru ta ci dimbin rayuka da dukiyoyin al’umma ba adadi ba tare da samun gagarumar nasarar dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin al’umma ba.

Masana tsaro sun bayyana ra’ayoyi mabambanta kan sauye- sauyen. Wasu na ganin cewa sabbin jini za su iya kawo canji, yayin da wasu suka yi gargadin cewa sauya shugabanni kadai ba zai wadatar ba idan ba a yi gyaran tsari ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  October 30, 2025 Manyan Labarai Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC October 30, 2025 Manyan Labarai Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?