Aminiya:
2025-11-03@01:58:56 GMT

Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani

Published: 31st, July 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Jigawa ta horas da Malaman makarantun sakandare kimanin dubu 20 ilimin fasahar sadarwar zamani (digital).

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi ne ya bayyana hakan a lokacin da ya karɓi baƙuncin tawaga daga Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta ƙasa (NITDA) da Cibiyar Zaman Lafiya ƙarƙashin jagorancin Farfesa Hauwa Ibrahim da take Amurka, a ziyarar ban girma da suka kai a gidan gwamnati da ke Dutse.

Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah

Ya ce: “Mun gabatar da cibiya ta dijital don malamai, don sadarwa da kuma kula da ilmantarwa a matakin farko, mun sanya hannu kan haɗin gwiwa na shekaru biyar tare da NewGlobe don ƙarfafa ƙa’idojin rubutu da ƙididdiga ta amfani da kayan aikin dijital.

“Don haka shirin ku ya yi daidai da gyare-gyaren da muke da su kuma yana ƙara ƙimar ilimi matuƙa.” In ji Namadi.

Gwamna Namadi ya kuma nanata ƙudirin gwamnatin Jigawa na ɗorewar shirin, yana mai cewa, “Ina tabbatar muku: Za mu mallaki wannan shiri, za mu ci gaba da faɗaɗa shi, Kwamishinoninmu na ilimi a matakin farko da kuma na manyan makarantu za su sa ido a kansa.”

Darakta mai riƙon ƙwarya na dijital a Hukumar NITDA, Dokta Ahmed Tambuwal ya bayyana hangen nesa na ƙasa da ke jagorantar shirin.

“Muna nan a matsayin wani ɓangare na Hukumarmu ta NITDA na ci gaba da sadaukar da kai don aiwatar da ajandar Sabuwar Najeriya na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.”

“Babban ginshiƙi na wannan ajandar ita ce rarraba tattalin arzikin Najeriya ta hanyar fasahar dijital.”

Tambuwal ya bayyana cewa, NITDA tana ci gaba wajen cimma buri na kashi 70% na ilimin zamani a shekarar 2027, yana mai jaddada buƙatar haɗin gwiwa don cimma burin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

 

Ya kuma bayyana cewa kasar Sin wuri ne mai kyau ga harkokin zuba jari ga ‘yan kasuwa na duniya. Ya ce hadin gwiwa da kasar Sin yana nufin hadin gwiwa da damammaki, imani da kasar Sin yana nufin imani da kyakkyawar makoma, zuba jari a kasar Sin yana nufin zuba jari mai riba ta dogon zango.(Safiyah Ma)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi October 31, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Maganin Nankarwa (3)
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari