Femi Falana SAN Ya Yi Kiran A Inganta Harkar Shari’a A Najeriya
Published: 10th, April 2025 GMT
Lauyan kare hakkin bil’adama Femi Falana SAN ya yabawa jihar Kano bisa yadda take tafiyar da harkokin shari’a.
Falana ya bayyana hakan ne a yayin wani taron karawa juna sani ga masu gabatar da kara kan ingancin gudanar da shari’ar laifuka da Kurawa Hussein And Associates tare da hadin giwar Ma’aikatar Shari’a ta Kano suka shirya, wanda aka gudanar a otal din Bristol Kano.
Falana ya yabawa jihar Kano bisa amincewa da dokar hukumar kula da laifuka ta FIDRA a shekarar 2019 tare da zama jiha ta farko da ta soke tuhumar da jami’an ‘yan sanda ke yi na aikata laifuka.
Ya kuma jaddada bukatar masu gabatar da kara su samar da na’urori na zamani da horarwa masu inganci don bunkasa ayyukansu.
Falana ya kuma jaddada mahimmancin inganta yanayin aiki ga masu gabatar da kara don ba su damar mai da hankali kan ayyukansu.
Kungiyar kare hakkin dan Adam ta bayyana irin kalubalen da talakawa ke fuskanta wajen samun adalci, inda ta bayyana yanayin tattalin arziki da kuma bukatar gwamnati ta shiga tsakani.
Falana ya ba da shawarar cewa a baiwa ofishin kare hakkin jama’a ikon taimakawa talakawa, tare da kasancewa a kowace karamar hukuma.
“Hakan zai baiwa talakawa damar samun adalci da kuma samun lauyoyin da za su gudanar da shari’o’insu, inda ya ba da misali da hukumar ba da agajin lauya ta kasa (Legal Aid Council) wacce ke da ofisoshi a dukkan jihohin kasar nan 36.
Falana ya kuma jaddada mahimmancin kare hakkin wadanda ake tuhuma da kuma karfafa amincewa da tsarin shari’a.
Ya kara da cewa wadanda ake tuhuma suna da ‘yancin neman a ba su lauya, kuma dole ne ‘yan sanda su tuntubi hukumar bayar da agaji ta Legal Aid don samar da lauya. Ya kuma bukaci kafafen yada labarai da su taka rawa wajen wayar da kan jama’a, game da hakkokinsu a karkashin doka.
Femi Falana SAN ya yi kira ga kafafen yada labarai da su rika wayar da kan jama’a domin su sanar da jama’a hakkinsu a karkashin doka.
Cover /Abdullahi jalaluddeen/Kano
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Shari a kare hakkin
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
A nasa ɓangaren, mai bai wa Gwamnan Shawara Kan Al’ammuran Tsaro, Janar Dahiru Abdusalam (Mai Ritaya), ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar tana ɗaukar matakai tare da jami’an tsaro don samar da tsaro mai inganci.
Ya kuma bayyana cewa duk da matsalolin tsaro da ake fuskanta a hanyar Damaturu zuwa Gujba, jami’an tsaro na ƙoƙarin yin sintiri domin tabbatar da tsaro.
Janar Dahiru ya ce, “Koda yake muna fuskantar ƙalubale daga Boko Haram a yankunan wasu sansanin sojoji, jami’an tsaro na ci gaba da aikinsu domin kare yankin.”
Ya ƙara da cewa, “Muna taka-tsan-tsan musamman wajen daƙile karɓar haraji daga Boko Haram a wasu yankuna. Wannan al’amari yana da matuƙar wahala, amma muna fatan za mu samu nasara.”
Janar Dahiru ya tabbatar da cewa akwai tsaro a dukkanin sassan jihar tare da haɗin gwiwar sojoji, ‘yansanda, Civilian JTF da ‘yan sa-kai.
Ya kuma bayyana cewa za a fitar da sabbin dabaru cikin makonni masu zuwa domin yaƙar ‘yan ta’adda.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp