Lauyan kare hakkin bil’adama Femi Falana SAN ya yabawa jihar Kano bisa yadda take tafiyar da harkokin shari’a.

 

Falana ya bayyana hakan ne a yayin wani taron karawa juna sani ga masu gabatar da kara kan ingancin gudanar da shari’ar laifuka da Kurawa Hussein And Associates tare da hadin giwar Ma’aikatar Shari’a ta Kano suka shirya, wanda aka gudanar a otal din Bristol Kano.

 

 

Falana ya yabawa jihar Kano bisa amincewa da dokar hukumar kula da laifuka ta FIDRA a shekarar 2019 tare da zama jiha ta farko da ta soke tuhumar da jami’an ‘yan sanda ke yi na aikata laifuka.

 

Ya kuma jaddada bukatar masu gabatar da kara su samar da na’urori na zamani da horarwa masu inganci don bunkasa ayyukansu.

 

 

Falana ya kuma jaddada mahimmancin inganta yanayin aiki ga masu gabatar da kara don ba su damar mai da hankali kan ayyukansu.

 

 

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta bayyana irin kalubalen da talakawa ke fuskanta wajen samun adalci, inda ta bayyana yanayin tattalin arziki da kuma bukatar gwamnati ta shiga tsakani.

 

Falana ya ba da shawarar cewa a baiwa ofishin kare hakkin jama’a ikon taimakawa talakawa, tare da kasancewa a kowace karamar hukuma.

 

“Hakan zai baiwa talakawa damar samun adalci da kuma samun lauyoyin da za su gudanar da shari’o’insu, inda ya ba da misali da hukumar ba da agajin lauya ta kasa (Legal Aid Council) wacce ke da ofisoshi a dukkan jihohin kasar nan 36.

 

 

Falana ya kuma jaddada mahimmancin kare hakkin wadanda ake tuhuma da kuma karfafa amincewa da tsarin shari’a.

 

 

Ya kara da cewa wadanda ake tuhuma suna da ‘yancin neman a ba su lauya, kuma dole ne ‘yan sanda su tuntubi hukumar bayar da agaji ta Legal Aid don samar da lauya. Ya kuma bukaci kafafen yada labarai da su taka rawa wajen wayar da kan jama’a, game da hakkokinsu a karkashin doka.

 

Femi Falana SAN ya yi kira ga kafafen yada labarai da su rika wayar da kan jama’a domin su sanar da jama’a hakkinsu a karkashin doka.

 

 

Cover /Abdullahi jalaluddeen/Kano

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Shari a kare hakkin

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala

Hukumar Tace Fina-Finai da Dab’i ta Jihar Kano ta haramta shirya duk wata muƙabala tsakanin mawaƙan yabon Annabi (S.A.W), tare da gayyatar mawaƙa Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi su bayyana a gabanta.

Hukumar ta kuma gayyaci mawaƙan ne tare da sauran waɗanda suka jagoranci muƙabalar da fitattun mawaƙan biyu suka yi ranar Litinin, da su bayyana a gabanta cikin sa’o’i 24.

Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu

Hakan na zuwa ne ƙasa da kwana ɗaya bayan ɓullar wata muhawara da aka yi tsakanin Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi kuma ta karade shafukan sada zumunta, wacce hukumar ta bayyana a matsayin karya dokokin aikinta.

Shugaban hukumar, Abba El-Mustapha ne ya sanar da hakan ranar Talata, inda ya ce ɗaukar matakin wani yunƙuri ne na tabbatar da zaman lafiya, daidaito da bin doka tsakanin mawaƙan nishaɗi da na addini.

El-Mustapha, a cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar, ya kuma ce an haramta duk wata nau’in muƙabala daga mawaƙan addini a jihar ba tare da izinin hukumar ba.

A yayin da yake ƙaddamar da wani kwamitin bincike da shugaban hukumar ya naɗa karkashin Daraktan Ayyuka na Musamman a hukumar, Isah Abdullahi, El-Mustapha ya umarci waɗanda aka gayyatar da su bayyana a gaban kwamitin domin amsa tambayoyi.

Hukumar ta ce shirya irin waɗannan muhawara ba tare da izininta ba ya saɓa doka kuma zai iya jawo hukunci mai tsanani ga wanda suka karya.

Hukumar ta kuma jaddada ƙudirinta na ci gaba da kula da ayyukan mawaƙan da masu nishaɗantarwa a faɗin jihar tare da yin kira ga jama’a da su zauna lafiya sannan su ci gaba da ba ta haɗin kai a ayyukanta.

Yadda aka yi muƙabala tsakanin Shehi Tajul Izzi da Maidubun Isa

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Ma’aikatar Shari’ar Iran Ta Sanar Da Rataye Dan Leken Asirin Hukumar Mossad Ta Isra’ila
  • Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa