Za a kashe biliyan 712.26 don yi wa filin jirgin saman Legas garanbawul
Published: 1st, August 2025 GMT
Majalisar Zartarwa ta Kasa ta amince da kashe Naira biliyan 712.26 don yi wa wani sashe na filin jirgin saman a Murtala Muhammad da ke Legas garambawul.
Hakan dai ya biyo bayan zaman majalisar wanda Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta a Abuja ranar Laraba.
NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi? Za a fara yi wa ɗaliban jami’o’i gwajin ƙwaya — Gwamnatin NijeriyaAikin dai wani bangare ne na Naira biliyan 900 da aka ware domin inganta harkokin sufurin jiragen sama a fadin Najeriya.
Ministan Harkokin Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo ne ya bayyana hakan jim kadan da kammala taron majalisar, inda ya ce tuni har an ba da kwangilar aikin ga kamfanin gine-gine na kasar China (CCECC).
A cewar Ministan, aikin ya kuma kunshi canza kayayyakin da ake amfani da su a wurin saukar jirage na filin daga na da zuwa na zamani.
Keyamo ya kuma ce majalisar ta kuma amince a kashe Naira biliyan 49.9 wajen aikin katange filin jirgin na Legas domin a inganta tsaro a cikin shi,
Katangar mai tsawon kilomita 14.6 wacce ta karfe ce, za kuma a saka mata na’urori a jikinta da kyamarorin CCTV da fitilu masu amfani da hasken rana da kuma tituna a gefenta.
“Duk wanda ko kuma duk abin da ya rabi katangar za mu gan shi cikin gaggawa sannan a nuna wajen da yake,” in ji Minista Keyamo.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
Sarakunan suna bada haɗin kai wajen tafiyar da harkokin gwamnatin ƙasarsu, suna kuma jin basu tare da wata matsala ba tare da matsayinsu. Yawancin Sarakuna da kuma wasu manyan msu Sarautar gargajiya bugu da ƙari suna cikin majlisar dattawa a lokacin.
Duk kuma wani lokaci da Sarakunan gargajiya suka fahimci suna fuskantar barazana dangane da tsaronsu, ta haka ne za su fara wasu tafiye- tafiye basu nan basu can, wanda idan ba sa’a aka yi ba, kusan ƙarshen ƙasar ke nan a matsayinta na tarayyar Nijeriya a lokacin. Duk wani ƙoƙarin da Abubbakar Tafawa Balewa ya yi na kasancewa ya zama kamar yadda Kwame Nkrumah na Ghana, wanda a zamaninsa kome ya ce daidai ne sai an bi ko amfani da shi, irin hakan ba zai iya haifar da ɗa mai ido ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp