Martani: Har yanzu muna ci gaba da yajin aiki — Ma’aikatan jinya
Published: 1st, August 2025 GMT
Kungiyar Ma’aikatan jinya da Ungozoma ta Ƙasa (NANNM) ta mayar wa da gwamnati martanin cewa har yanzu tana ci gaba da gudanar da yajin aikin da take yi.
Ministan Lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Ali Pate, ne dai ya bayyana cewa ƙungiyar ta janye yajin aikin gargaɗin.
An ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a Kebbi Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansaninta a KebbiDa yake magana da manema labarai bayan wani taron sirri da aka yi a Abuja ranar Juma’a, Pate ya ce matakin ya biyo bayan yarjejeniyoyin da gwamnati da shugabannin Ƙungiyar NANNM suka cimma ne.
Amma da aka tuntuɓi shugaban Ƙungiyar na ƙasa, Morakinyo Rilwan ya ce ba gaskiya ba ne cewa an janye yajin aikin.
“Idan har Ministan ne ya shirya yajin aikin, to zai iya janye yajin aikin, a ɓangarenmu yajin aikin da ƙungiyar ta shirya yana ci gaba da gudana, Ministan bai shirya yajin aikin ba, don haka ba shi da hurumin janye yajin.
Rilwan ya shaida wa Daily Trust ta wayar tarho cewa, “Akwai hanyoyin da za a bi, idan za a janye yajin aikin gaba ɗaya.
A ranar Laraba ne ma’aikatan jinya suka fara yajin aikin gargaɗi na kwanaki bakwai a faɗin ƙasar. Yajin aikin, a cewar shugabancin NANNM zai magance matsalolin da suka haɗa da rashin biyan albashi, ƙarancin ma’aikata, alawus-alawus da ba a biya ba da kuma rashin yanayin aiki mai kyau.
Wannan yajin aikin dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun takun saƙa tsakanin likitoci da gwamnati kan walwala da sauran batutuwa kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Yajin aikin ma’aikatan jinya da ya biyo bayan cikar wa’adin kwanaki 15 da NNNM ta bai wa gwamnatin tarayya wanda ya kawo cikas ga harkokin kiwon lafiya a faɗin Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Farfesa Ali Pate Kungiyar Ma aikatan jinya da Ungozoma ta Ƙasa Ministan Lafiya da walwalar jama a janye yajin aikin aikatan jinya
এছাড়াও পড়ুন:
Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki
Babban magatakardar kungiyar Hizbullah Sheikh Na’im Kassim ya bayyana cewa; Hizbullah tana yin aiki ne ta fuskoki biyu; na farko gwgawarmaya da HKI, sai kuma a fagen Siyasa a cikin gida.
Shugaban kungiyar ta Hizbullah wanda ya gabatar da jawbai a jiya domin girmama babban kwamandan kungiyar Hizbullah Shahid Sayyid Fu’ad Shukr ya ce; An zabi shugaban kasa Joseph Aun ne bayan da aka dauki shekaru ba tare da shugaban kasa ba a kasar. Kuma kungiyar gwagwarmaya ta tabbatar da cewa ginshiki ne a fagen siyasa, wacce ta saukaka yadda aka zabi shugaban kasar da kafa gwamnati.”
Har ila yau Sheikh Naim Kassim ya yi bayani akan yadda gwagwarmaya ta kafu a cikin kasar Lebanon a matsayin mayar da martani ga mamayar HKI, ta kuma cike gibin da sojoji su ka bari, da a karshe a 2000 ta kori HKI daga cikin Lebanon.
Sheik Na’im Kassim ya kuma ce; Gwgawarmaya wani nauyi ne da rataya akan kowa, ba wai zabi ba ne,kuma lokacin da aka yi aiki a tsakanin gwgawarmaya, soja da al’umma an cimma nasarori masu yawan gaske.
Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah sheik Na’im Kassim ya kuma ce; Batun makaman dake hannun kungiyar Hizbullah wani batu ne da ya shafi cikin gidan kasar Lebanon, don haka ba shi da wata alaka da HKI.”
Akan batun kwance damarar yakin kungiyar ta Hizbullah, Sheikh Na’im Kassim ya ce, duk wanda yake son ganin hakan ta faru, to yana yi wa Isra’ila aiki ne.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata July 31, 2025 Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila July 31, 2025 Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba July 31, 2025 Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine July 31, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci