‘Yan Sanda Sun Kama Wani Kasurgumin Barowon Shanu Da Garkuwa Da Mutane A Kasuwar Shinge
Published: 20th, May 2025 GMT
Jami’an Sashen Binciken Laifuka na Rundunar ‘Yan Sanda a Jihar Nasarawa (SCID) sun kama wani mai garkuwa da mutane a Kasuwar Shinge da ke Lafia, bisa rahotonnin sirri da suka samu.
An samu nasarar cafke wanda ake zargin bayan shafe dogon lokaci rundunar na nemasa ruwa a jallo saboda laifuka da dama da suka hada da garkuwa da mutane da kuma satar shanu.
A yayin bincike, wanda ake zargin ya amsa laifinsa, sannan ya jagoranci jami’an tsaro zuwa maboyarsa da ke kauyen Ruwan Baka a karamar hukumar Doma, inda aka samu bindiga kirar AK-49 mai lamba 453144 tare da alburusai.
Wannan nasarar ta biyo bayan kama wata Fatima Salisu a ‘yan kwanakin baya, wadda aka tare tana jigilar makamai daga Doma zuwa Jihar Katsina domin kaiwa miyagu.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Nasarawa, CP Shattima Jauro Mohammed, ya jaddada kudirin rundunar na ci gaba da yaki da aikata laifuka tare da tabbatar da tsaro ga dukkan mazauna jihar Nasarawa.
Ya bukaci jama’a da su kasance masu lura, tare da bayar da rahoton duk wani motsi ko aikin da ba su yarda da shi ba, domin ‘yan sanda za su ci gaba da aiki tukuru don tabbatar da zaman lafiyar al’umma.
Aliyu Muraki
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba
Wata mummunar guguwa ta yi sanadin mutuwar mutum shida sannan ta jikkata wasu 30 a garin Garba-Chede da ke karamar hukumar Bali a jihar Taraba.
A cewar wani mazaunin yankin wanda guguwar ta lalata wa gida mai suna Abubakar Dodo, an shafe shekaru masu yawa ba su ga irin ta ba a yankin saboda munin barnar da ta yi.
Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a FilatoA cewarsa, ban da gidaje, guguwar ta kuma lalata makarantu da masallatai da coci-coci, sannan kayan abinci na miliyoyin Naira sun salwanta.
Dagacin garin na Garba-Chede, Kaigama Maigandi, ya yi kira ga Gwamnan Jihar, Agbu Kefas, da ya taimaka wa mutanen yankin da iftila’in ya shafa domin su samu su gyara gidaje da wuraren kasuwancinsu.
A wani labarin kuma, wata tawagar wakilai daga Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas (NEDC), ta ziyarci yankin domin jajanta musu da kuma ganin girman barnar domin ganin irin tallafin da za a yi musu.
Ayarin, wanda ke karkashin jagorancin Dr. Balutu Isa Mohammed, ya yi jaje ga mutanen tare da yi musu alkawarin ba su tallafin muhimman abubuwan da suke bukata domin su rage radadi.
Tawagar ta kuma ziyarci Dagacin garin tare da yi masa bayanin musabbabin zuwansu da kuma ayyukan da suke yi.