Jami’an Sashen Binciken Laifuka na Rundunar ‘Yan Sanda a Jihar Nasarawa (SCID) sun kama wani mai garkuwa da mutane a Kasuwar Shinge da ke Lafia, bisa rahotonnin sirri da suka samu.

An samu nasarar cafke wanda ake zargin bayan shafe dogon lokaci  rundunar na nemasa ruwa a jallo saboda laifuka da dama da suka hada da garkuwa da mutane da kuma satar shanu.

A yayin bincike, wanda ake zargin ya amsa laifinsa, sannan ya jagoranci jami’an tsaro zuwa maboyarsa da ke kauyen Ruwan Baka a karamar hukumar Doma, inda aka samu bindiga kirar AK-49 mai lamba 453144 tare da alburusai.

Wannan nasarar ta biyo bayan kama wata Fatima Salisu a ‘yan kwanakin baya, wadda aka tare tana jigilar makamai daga Doma zuwa Jihar Katsina domin kaiwa miyagu.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Nasarawa, CP Shattima Jauro Mohammed, ya jaddada kudirin rundunar na ci gaba da yaki da aikata laifuka tare da tabbatar da tsaro ga dukkan mazauna jihar Nasarawa.

Ya bukaci jama’a da su kasance masu lura, tare da bayar da rahoton duk wani motsi ko aikin da ba su yarda da shi ba, domin ‘yan sanda za su ci gaba da aiki tukuru don tabbatar da zaman lafiyar  al’umma.

Aliyu Muraki

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Yan Sanda nasarawa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3, Sun Sace 26 A Zamfara

Akalla mutane uku ne aka ce an kashe tare da yin garkuwa da wasu 26 a wani sabon harin da wasu ‘yan bindiga suka kai a karamar hukumar Kauran Namoda da ke jihar Zamfara. Daily trust ta bankado cewa, hare-haren na tun ranakun Alhamis zuwa Asabar, sun shafi al’ummomi da dama a yankin. Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Bisa Daidaito A Afirilu Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe Shaidun gani da ido sun bayyana cewa, lamarin ya fi kamari akauyen Sabon Gari, inda aka kashe mace guda tare da yin garkuwa da mazauna yankin kusan 20. Wani mazaunin Kauran Namoda, wanda ya bukaci a sakaya sunansa, ya yi ikirarin cewa, adadin ya zarta haka, inda ya ce an kashe mutane hudu – ciki har da mace guda, tare da sace wasu 26. Rahotanni sun ce daga cikin wadanda aka sacen har da wani mutum, da matansa biyu, da ‘ya’yansu uku. An kai hare-haren ne da sanyin safiyar ranar Asabar da misalin karfe 1:00 na dare zuwa 2:30 na daren, duk da kasancewar jami’an tsaro a garin Kaura Namoda. Majiyoyi sun yi zargin cewa, ‘yan bindigar yaran wani fitaccen shugaban ‘yan bindiga, Bello Kaura ne, wanda aka fi sani da Dan Sade, wanda ake alakanta shi da kai hare-haren ta’addanci da dama a fadin kananan hukumomin Kaura Namoda, Bungudu, da Maradun.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3, Sun Sace 26 A Zamfara
  • Mutane 7 Sun Mutu 11Sun Jikkata A Hadarin Mota A Niger.
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 15 Sun Raunata 3 A Jihar Kebbi
  • An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja
  • ’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa
  • ‘Yan Kasuwa 27 Sun Rasu A Wani Hatsarin Kwale-kwale A Kwara
  • Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno
  • Za Mu Ci Gaba Da Binciko Mai A Arewa — Ojulari
  • Iran ta ce babu wata rubutaciyar shawara da ta samu daga Amurka