Aminiya:
2025-10-14@00:46:17 GMT

Kotu ta ɗaure matashi kan wulaƙanta Naira a TikTok

Published: 16th, May 2025 GMT

Hukumar da ke yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC reshen shiyyar Kaduna ta gurfanar da wani Muhammad Kabir a gaban kotu tare da yanke masa hukunci, wanda ya kasance mai wallafa bidiyo a shafukan TikTok da Instagram.

An gurfanar da Muhammad Kabir a gaban mai shari’a Rilwan Aikawa na babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kaduna bisa laifin wulaƙantawa da lalata takardun Naira.

An kama wata mata kan safarar makamai zuwa Katsina Sabon Hari: An kashe makiyayi da shanu sama da 100 a Filato

An kama Kabir ne a ranar Talata, 29 ga Afrilu, 2025 a Tudun Wada, Jihar Kaduna saboda yin wani bidiyo a shafinsa na TikTok da Instagram @youngcee0066 yayin da yake watsa takardar Naira a ƙasa, yana tattake su yana magana da harshen Hausa da kuma tursasa EFCC ta zo ta kama shi a inda yake.

Daga nan ne aka kama shi da laifin karya dokar babban bankin Najeriya (CBN) da ta haramta cin zarafi da wulaƙanta Naira.

Ɗaya daga cikin tuhume-tuhumen da ake yi masa, ya ce: “Kai Muhammad Kabir Sa’ad (da aka fi sani da  youngcee0066) a wani lokaci a shekarar 2025 a Kaduna da ke ƙarƙashin ikon wannan kotun mai girma, ka wulaƙanta Naira wanda ya saɓa ƙa’ida, ta hanyar tattaka takardun kuɗin Naira yayin da kake yin hoton bidiyo na sada zumunta da yaɗawa a intanet, sannan yin hakan aikata wani laifi ne na Babban Bankin Nijeriya na 2007 mai hukunci a ƙarƙashin Sashe na 21 (1) na wannan dokar.”

Wanda ake tuhumar ya amsa laifin da ake tuhumarsa da aikatawa lokacin da aka karanta masa, wanda hakan ya sa lauyan mai shigar da ƙara, M.U Gadaka ya roƙi kotu da ta yanke masa hukuncin da ya dace.

Sai dai Mai shari’a Aikawa ya yanke wa Muhammed hukuncin ɗaurin watanni shida (6) ko kuma ya biya tarar Naira dubu ɗari uku (₦300,000.00) ga Gwamnatin Tarayyar Najeriya.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

A cewarta, shirin ya taimaka wajen noman shinkafa da ta kai kimanin tan 99,452, wacce kuma kudinta ya kai kimanin Naira biliyan 13.527 tare kuma da noman rogo da ya kai kimanin tan 87,237, wanda kudinsa ya kai Naira biliyan 3.925, musamman domin a kara samar da wadataccen abinci da kuma kara bunkasa fannin tattalin arzikin jihar.

 

Sai dai, ta bayyana cewa; har yanzu a jihar ba a samar da wani cikakken tsari a hukumance ba, a kan tsarin na shirin na CAF wanda hakan ke haifar wa da shirin koma baya a jihar.

 

Ta yi kira ga sauran masu ruwa da tsaki a fannin bunkasa aikin noma, domin samun riba a jihar da su bayar da hadin kai wajen shiga cikin tsarin na CAF, musamman a bangaren noman shinkafa da rogo da sauran amfanin gona.

 

Kazalika, ta bukaci mahukunta a jihar da su samar da tsari a hukumance, musamman na dogon zango domin ci gaba da samar da wadataccen abinci a fadin jihar baki-daya.

 

Shi ma a nasa bangaren, jami’in shirin na jihar; Dakta Emmanuel Igbaukum ya bayyana cewa, masu ruwa da tsaki a jihar, sun nuna sha’awarsu ta shiga cikin shirin tare kuma da sanya shi a cikin tsarin jihar na samar da abinci mai gina jiki.

 

Ya kara da cewa, shirin zai kuma taimaka matuka wajen kara bunkasa fannin aikin noma na jihar baki-daya.

 

A nata jawabin, Babbar Sakatariya a ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci, Pharm. Elijah ta bayar da tabbacin cewa; gwamnatin jihar za ta bayar da kason kudi a kan lokaci tare kuma da yin rangwame wajen sayen kayan aikin noma cikin rahusa.

 

Ta bayyana cewa, gudunmawar shirin na IFAD ya taimaka matuka wajen kara bunkasa fannin tattalin arziki da kuma fannin aikin noma na jihar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Noma Da Kiwo Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara October 11, 2025 Noma Da Kiwo Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina October 3, 2025 Noma Da Kiwo Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo October 3, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA
  • Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako
  • Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya
  • Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice  
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno
  • Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe