Aminiya:
2025-08-15@17:44:31 GMT

Kotu ta ɗaure matashi kan wulaƙanta Naira a TikTok

Published: 16th, May 2025 GMT

Hukumar da ke yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC reshen shiyyar Kaduna ta gurfanar da wani Muhammad Kabir a gaban kotu tare da yanke masa hukunci, wanda ya kasance mai wallafa bidiyo a shafukan TikTok da Instagram.

An gurfanar da Muhammad Kabir a gaban mai shari’a Rilwan Aikawa na babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kaduna bisa laifin wulaƙantawa da lalata takardun Naira.

An kama wata mata kan safarar makamai zuwa Katsina Sabon Hari: An kashe makiyayi da shanu sama da 100 a Filato

An kama Kabir ne a ranar Talata, 29 ga Afrilu, 2025 a Tudun Wada, Jihar Kaduna saboda yin wani bidiyo a shafinsa na TikTok da Instagram @youngcee0066 yayin da yake watsa takardar Naira a ƙasa, yana tattake su yana magana da harshen Hausa da kuma tursasa EFCC ta zo ta kama shi a inda yake.

Daga nan ne aka kama shi da laifin karya dokar babban bankin Najeriya (CBN) da ta haramta cin zarafi da wulaƙanta Naira.

Ɗaya daga cikin tuhume-tuhumen da ake yi masa, ya ce: “Kai Muhammad Kabir Sa’ad (da aka fi sani da  youngcee0066) a wani lokaci a shekarar 2025 a Kaduna da ke ƙarƙashin ikon wannan kotun mai girma, ka wulaƙanta Naira wanda ya saɓa ƙa’ida, ta hanyar tattaka takardun kuɗin Naira yayin da kake yin hoton bidiyo na sada zumunta da yaɗawa a intanet, sannan yin hakan aikata wani laifi ne na Babban Bankin Nijeriya na 2007 mai hukunci a ƙarƙashin Sashe na 21 (1) na wannan dokar.”

Wanda ake tuhumar ya amsa laifin da ake tuhumarsa da aikatawa lokacin da aka karanta masa, wanda hakan ya sa lauyan mai shigar da ƙara, M.U Gadaka ya roƙi kotu da ta yanke masa hukuncin da ya dace.

Sai dai Mai shari’a Aikawa ya yanke wa Muhammed hukuncin ɗaurin watanni shida (6) ko kuma ya biya tarar Naira dubu ɗari uku (₦300,000.00) ga Gwamnatin Tarayyar Najeriya.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

Ahmed Maiyaki da Sadiq Mamman Legas a madadin gwamnatin jihar Kaduna sun ce ofishin babban lauyan gwamnati da kwamishinan shari’a zai yi nazari kan kalaman da kungiyar hadaka ta ADC ta yi tare da baiwa gwamnatin jihar shawara kan mataki na gaba.

Tun da farko a wani taron manema labarai, jam’iyyar African Democratic Congress da hadin gwiwarta sun zargi gwamnatin jihar Kaduna da daukar hayar ‘yan baranda sama da 4000 tare da cire naira miliyan 30 daga asusun kowace karamar hukuma domin kawo cikas ga zaben da ke tafe.Wannan shi ne bayanin da mataimakin shugaban jam’iyyar ADC na kasa reshen Arewa maso Yamma, Jafaru Ibrahim Sani da Shugaban Jam’iyyar na Jihar Kaduna Patrick Ambut.

A cewarsu, sun aika da koke ga INEC da hukumomin tsaro dangane da hakan.Wannan shi ne bayanin da mataimakin shugaban jam’iyyar ADC na kasa reshen Arewa maso Yamma, Jafaru Ibrahim Sani da Shugaban Jam’iyyar na Jihar Kaduna Patrick Ambut.

A cewarsu, sun aika da koke ga INEC da hukumomin tsaro dangane da hakan.ugaban jam’iyyar ADC na kasa reshen Arewa maso Yamma, Jafaru Ibrahim Sani da Shugaban Jam’iyyar na Jihar Kaduna Patrick Ambut.

A cewarsu, sun aika da koke ga INEC da hukumomin tsaro dangane da hakan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe
  • ‘Yan Majalisa Na Amsar Cin Hanci Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.
  • ‘Yan Majalisa Na Amsar Cin Hancin Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.
  • An kama Mai Unguwa kan yi wa yarinya fyaɗe a Gombe
  • ‘Yan Majalisa Na Ba Da Cin Hancin Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Iya Gabatar Da Ƙudiri – Kamfani.
  • ’Yan sanda sun kama matashi kan zargin aikata fashi a Gombe
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 127
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 124
  • Jama’a sun koka kan rashin kammala aikin titi a Kafanchan
  • An kama basarake kan zargin yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a Gombe