Aminiya:
2025-06-30@08:55:35 GMT

Kotu ta ɗaure matashi kan wulaƙanta Naira a TikTok

Published: 16th, May 2025 GMT

Hukumar da ke yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC reshen shiyyar Kaduna ta gurfanar da wani Muhammad Kabir a gaban kotu tare da yanke masa hukunci, wanda ya kasance mai wallafa bidiyo a shafukan TikTok da Instagram.

An gurfanar da Muhammad Kabir a gaban mai shari’a Rilwan Aikawa na babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kaduna bisa laifin wulaƙantawa da lalata takardun Naira.

An kama wata mata kan safarar makamai zuwa Katsina Sabon Hari: An kashe makiyayi da shanu sama da 100 a Filato

An kama Kabir ne a ranar Talata, 29 ga Afrilu, 2025 a Tudun Wada, Jihar Kaduna saboda yin wani bidiyo a shafinsa na TikTok da Instagram @youngcee0066 yayin da yake watsa takardar Naira a ƙasa, yana tattake su yana magana da harshen Hausa da kuma tursasa EFCC ta zo ta kama shi a inda yake.

Daga nan ne aka kama shi da laifin karya dokar babban bankin Najeriya (CBN) da ta haramta cin zarafi da wulaƙanta Naira.

Ɗaya daga cikin tuhume-tuhumen da ake yi masa, ya ce: “Kai Muhammad Kabir Sa’ad (da aka fi sani da  youngcee0066) a wani lokaci a shekarar 2025 a Kaduna da ke ƙarƙashin ikon wannan kotun mai girma, ka wulaƙanta Naira wanda ya saɓa ƙa’ida, ta hanyar tattaka takardun kuɗin Naira yayin da kake yin hoton bidiyo na sada zumunta da yaɗawa a intanet, sannan yin hakan aikata wani laifi ne na Babban Bankin Nijeriya na 2007 mai hukunci a ƙarƙashin Sashe na 21 (1) na wannan dokar.”

Wanda ake tuhumar ya amsa laifin da ake tuhumarsa da aikatawa lokacin da aka karanta masa, wanda hakan ya sa lauyan mai shigar da ƙara, M.U Gadaka ya roƙi kotu da ta yanke masa hukuncin da ya dace.

Sai dai Mai shari’a Aikawa ya yanke wa Muhammed hukuncin ɗaurin watanni shida (6) ko kuma ya biya tarar Naira dubu ɗari uku (₦300,000.00) ga Gwamnatin Tarayyar Najeriya.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Rundunar ta bayyana cewa, an kashe ‘yan bindigar da dama yayin wannan gumurzu da ya dauki tsawon wasu awanni ana fafatawa da sojojin.

Koda-yake dai a cewar rundunar sojin, an kashe musu wasu daga cikin jami’ansu; yayin musayar wuta da ‘yan bindigar a daidai wancan lokacin.

Baya ga haka, rundunar sojin ta kuma kara da cewa; wasu sojoji hudu sun jikkata sakamakon harbin bindiga daga ‘yan ta’addar, amma kuma suna nan suna samun kulawa a asibiti.

Har wa yau, rundunar sojin ta kuma bayyana wadanda suka mutun a matsayin cikakkun Jarumai, wadanda suka tsaya tsayin daka, domin kare matsayinsu da kuma mutuncin kasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Wani Dan Bindiga Dadi Ya Kashe Ma’aikatan Kashe Gobara 2 A Amurka
  • Iran: An Kama Wani Dan Leken Asirin “Mosad” A Tehran A Jiya Lahadi
  • Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
  • An samu amincewar yi wa Dantata jana’iza a Madina
  • Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025
  • Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya
  • Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
  • ’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a Gombe
  • Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja