Jagora: Yin Shirun da Kasashen Duniya Sun Yi Kan ABinda Yake Faruwa A Gaza Abun Mamaki Ne
Published: 15th, May 2025 GMT
Jagoran juyin juyala halin musulunci a nan Iran Imam Sayyid Aliyul Khaminae, ya zargi kasashen yamma da goyon bayan kissan kare dangin da ke faruwa a gaza.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Jagoran yana fadar haka a jiya Talata a lokacinda yake ganawa da wadanda suka shirya taro na farko don tunawa da likitoci shahidar a yanki mai tsarki na shekaru 8 tsakanin Sadam Hussain na kasar Iraqi wanda yake samun goyon bayan manya manyan kasashen duniya a lokacin da kuma jaririyar JMI a lokacin.
Jagoran ya yi tir da dukkan yake yaken da kasashen yamma suke tallafawa a yammacin Asiya daga ciki har da yakin Gaza, inda HKI wacce take samun goyon bayan manya-manyan kasashen yamma.
Sannan ya kara jaddada matsayin JMI na tallafawa wadanda ake zalunta a yankin Asiya ta kudu da kuma a duk inda suke a duniya.
A wani bangare na Jawabinsa Imam Khamina’ie ya bayyana cewa wajibi ne a kammu gaba daya mu bada gudumawa don kubutar da wadanda ake zalunta a duniya, kowa gwagwadon abinda zai iya.
Ba yadda za’a hada wadannan likitoci wadanda basa dauke da makami amma suna cikin fagen fama don taimakawa wadanda suka ji rauni ko kuma raunana,da wadannan dabbobin daji wadanda basu bar kuwa ba basu san mutunci da kuma abinda ake kira tausayi ba, suna kashe don wanda yake gabansu kama daga mata tsoffi da hatta jarirai.
Daga karshe jagoran yace karya ba zata dade ba, sai dai ba zai bace ba sai tare turjiya da kuma yakar duk azzalumai wadanda suke hana gaskiya tabbata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kasashen Dimokaradiyyar Congo Da Ruwanda Sun Rattaba Hannu Kan Yrajejeniyar Zaman Lafiya
Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo da Rwanda sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya bayan shafe shekaru 30 suna rikici
Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo da Rwanda sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya, shekaru talatin bayan rikicin da ya barke a shekara ta 1994 da ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane daga bangarorin biyu.
An rattaba hannu kan takardar ne a gaban sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio, ministar harkokin wajen Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo, Teresa Kayumba, da na Rwanda Olivier Nduhungirehe.
Yarjejeniyar da Amurka da Qatar suka wakilci shiga Tsakani ta hada da tanade-tanade kan mutunta yankunan kasa, haramta ayyukan soji, kwance damarar makamai da hadewar kungiyoyin da ba na gwamnati ba, da kuma samar da wani tsari na hadin gwiwa don daidaita al’amuran tsaro.