Jagora: Yin Shirun da Kasashen Duniya Sun Yi Kan ABinda Yake Faruwa A Gaza Abun Mamaki Ne
Published: 15th, May 2025 GMT
Jagoran juyin juyala halin musulunci a nan Iran Imam Sayyid Aliyul Khaminae, ya zargi kasashen yamma da goyon bayan kissan kare dangin da ke faruwa a gaza.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Jagoran yana fadar haka a jiya Talata a lokacinda yake ganawa da wadanda suka shirya taro na farko don tunawa da likitoci shahidar a yanki mai tsarki na shekaru 8 tsakanin Sadam Hussain na kasar Iraqi wanda yake samun goyon bayan manya manyan kasashen duniya a lokacin da kuma jaririyar JMI a lokacin.
Jagoran ya yi tir da dukkan yake yaken da kasashen yamma suke tallafawa a yammacin Asiya daga ciki har da yakin Gaza, inda HKI wacce take samun goyon bayan manya-manyan kasashen yamma.
Sannan ya kara jaddada matsayin JMI na tallafawa wadanda ake zalunta a yankin Asiya ta kudu da kuma a duk inda suke a duniya.
A wani bangare na Jawabinsa Imam Khamina’ie ya bayyana cewa wajibi ne a kammu gaba daya mu bada gudumawa don kubutar da wadanda ake zalunta a duniya, kowa gwagwadon abinda zai iya.
Ba yadda za’a hada wadannan likitoci wadanda basa dauke da makami amma suna cikin fagen fama don taimakawa wadanda suka ji rauni ko kuma raunana,da wadannan dabbobin daji wadanda basu bar kuwa ba basu san mutunci da kuma abinda ake kira tausayi ba, suna kashe don wanda yake gabansu kama daga mata tsoffi da hatta jarirai.
Daga karshe jagoran yace karya ba zata dade ba, sai dai ba zai bace ba sai tare turjiya da kuma yakar duk azzalumai wadanda suke hana gaskiya tabbata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran: Babu Mika Kai Ga Takurawar kasashen Yamma har sai An Kawo Karshen Barazana
Shugaban hukumar makamashin nukliya na kasar Iran wato (AEOI) Muhammad Eslami ya bayyana cewa babu jada bayana a shirin nukliyar kasar iran, duk tare da takurawar kasashen yamma.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Eslami yana fadar haka a wani taro nay an jarida a nan Tehran a jiya Talata.
Ya kuma kara da cewa kasashen yamma masu babakere kan al-amura a duniya suna son haramtawa mutanen kasar Iran ilmin zamani da kuma ci gaba a fasahar Nukliya. Amma gwamnatin kasar Iran ta dage kan cewa yakin kwanaki 12 da suka dorawa kasar ba zai hana ta ci gaba da shirinta na makamashin nukliya ba.
A wani bangare a maganarsa, shugaban hukumar makamashin nukliya na kasar Iran ya bayyana cewa, hukumar IAEA da kuma kasashen yamma suna nuna fuska biyu a cikin ayyukansu, duk abinda ya shafi Iran suna tsanan tawa, amma ga HKI tana da makaman nukliya, kuma bata cikin yarjeniyar NPT ko kuma hukumar ta IAEA. Amma sai suyi kamar basu gani ba.
Don haka iran zata ci gaba da dagewa har zuwa lokacinda zasu tabbatar da hakkinta. Na mallakar fasahohin daban-daban.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hukuma Mai Kula Da Sauka Da Tashin Jiragen Sama A Paris Ya Dakatar Da Wani Ma’aikacinta August 13, 2025 Iraki Tace: Ita Yentacciyar Kasashe Ce Bayan da Amurka Ta Yi Korafi Kan Yarjeniyar tsaro da Iran August 13, 2025 Ministan Harkokin Wajen Masar Ya sake Ganawa da Aragchi Da Kuma Gorossy August 13, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Alhininsa Kan Kashen Masanan Kasar Iran Da ‘Yan Sahayoniyya Suka Yi August 13, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Lokaci Ya Yi Da Za A Daina Kakaka Takunkumi Da Ba Dace Ba Kan Kasashe August 13, 2025 Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran Ya Jaddada Kasancewar Iran Tare Da Kasar Lebanon Koda Yaushe August 13, 2025 Kasar Iraki Ta Ce: Yarjejeniyar Da Ta Kulla Da Iran Zai Amfani Dukkan Kasashen Yankin August 13, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’Ila Har Sau Shida August 13, 2025 Wakilan Hamas sun isa Alkahira don shawarwarin tsagaita wuta a Gaza August 13, 2025 Iran: Amurka Da Isra’ila Ne Da Kansu Suka Bukaci Dakatar Da Bude Wuta August 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci