Leadership News Hausa:
2025-08-11@10:23:08 GMT

Sojoji Sun Daƙile Harin Boko Haram A Yobe

Published: 22nd, April 2025 GMT

Sojoji Sun Daƙile Harin Boko Haram A Yobe

A yayin harin, mutane da dama sun gudu zuwa dazuka, amma sun fara dawowa yayin da zaman lafiya ya fara samuwa.

“Yanzu mutane sun fara dawowa garin kuma abubuwa sun fara dawowa dai-dai,” inji wani mazaunin yankin.

Wani dagacin ƙauyen, wanda ya buƙaci a sakaya sunansa, ya ce an samu zaman lafiya kuma al’umma sun fara komawa harkokinsu na yau da kullum.

“Muna gode wa sojojin bisa yadda suka daƙile harin cikin gaggawa,” inji shi.

Wannan ba shi ne karo na farko da aka kai hari a Buni Yadi ba, lamarin da ke ƙara tayar da hankalin jama’a game da buƙatar ƙarin tsaro a yankin.

Mazauna yankin na kira ga gwamnati da ta tura ƙarin sojoji don hana faruwar irin wannan hari a gaba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Boko Haram Daƙilewa Hari

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatan shari’a 97 sun samu ƙarin girma a Borno

Hukumar Shari’a ta Jihar Borno ta ƙara wa ma’aikatanta 97 girma bayan wani taro na kwanaki huɗu da ta gudanar a Maiduguri.

Muƙaddashin sakataren hukumar, Saleh Khala Jidda ne, ya bayyana hakan a wata sanarwa cewa ma’aikatan sun samu ƙarin girma ne saboda ƙwazonsu.

EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo  ’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato

Waɗanda abin ya shafa sun hada da Majistare 10 daga matakin Majistare mataki na ɗaya zuwa Babban Majistare mataki na biyu.

Sai Majistare daga matakin farko zuwa Babban Majistare na biyu.

Sauran sun haɗa manyan Magatakarda daga mataki na ɗaya zuwa na biyu.

Sai dai a gefe guda, hukumar ta ɗauki mataki kan wani alƙalin Babban Kotun Majistare ta 4 da ke Wulari, Maiduguri, mai suna Yusuf Garba.

Binciken da kwamitin ƙorafe-ƙorafen jama’a ya gudanar ya gano cewa alƙalin ya karkatar da kuɗaɗen shiga na gwamnati har Naira 100,000.

Saboda haka aka sauke shi daga muƙaminsa tare da umartar ya kai rahoto ga Babban Magatakarda domin a sake masa muƙami.

Hukumar ta tabbatar wa jama’a cewa tana da niyyar ci gaba da tabbatar da gaskiya da adalci a kotuna.

Sannan ta ce za ta ladabtar da masu cin hanci da rashawa da kuma girmama masu gaskiya da riƙon amana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan
  • Ma’aikatan shari’a 97 sun samu ƙarin girma a Borno
  • Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram a Borno
  • Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika
  • Ana Alhinin Tunawa Da Harin Nukiliyar Nagasaki Shekarau 80 Da Suka Gabata A Japan
  • An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro
  • Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 
  • Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno
  • UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari
  • ’Yan damfara 2 sun shiga hannun ’yan sanda a Yobe