Aminiya:
2025-12-14@07:47:27 GMT

Jama’a sun koka kan rashin inganci shinkafar Gwamanti a Kogi

Published: 15th, April 2025 GMT

’Yan Najeriya da suka rabauta da sayen shinkafar kasar waje da Gwamnatin Tarayya ta karya farashinsa sun koka bisa rashin ingancin wata wadda ake sayarwa a Jihar Kogi.

Wadanda suka sayi rukunin farko na shinkafar sun yaba da ingancinta da dandanonta, wasu kuma na korafi a kan yanayi da kuma dandanon wadda suka samu daga wani kamfani daga wata kasar Asiya.

Wasu suka samu shinkafar mai matsala sun yi ikirarin samun kwari a cikinta kuma tana yin kumfa idan ana dafa ta, sa’annan idan ta nuna tana yin danko sosai, sabanin yadda aka san shinkafar kasar waje.

Wani dan kasuwar shinkafar cikin gida a Najeriya ya yi zargin rukunin shinkafar da ta samu matsalar ta jima a ajiye ne kafin a fito da ita, shi ya sa ingancin ya samu matsala.

Duk da samun koma baya: Najeriya ce kasa mafi arzikin danyen mai a Afirka —OPEC Matashi ya yi yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a Kano

Don haka ya shawarci masu saya da su shanya ta a rana kuma su wanke ta sosai sa’annan su dan turara ta domin dawo da ingancinta.

A gefe guda kuma wadanda da suka amfana da wani rukuni na daban na shinkafar gwamnatin sun yaba da ingancinta ta fuskar dandano da kuma yanayi.

Kawo yanzu dai hukumomi ba su ce uffan game da korafin da jama’a ke yi kan wannan lamari ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnati

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige

Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), ta kama tare da tsare Tsohon Ministan Ƙwadago kuma Tsohon Gwamnan Jihar Anambra, Chris Ngige.

Mai magana da yawun Ngige, Fred Chukwuelobe ne, ya tabbatar da hakan da safiyar ranar Alhamis. bayan wasu rahotanni da aka yaɗa cewar an sace Ngige.

An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin miyagun ƙwayoyi a Indiya Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC

Chukwuelobe, ya bayyana a shafinsa na Facebook cewa, “Ngige yana tare da EFCC. Ba a sace shi aka yi ba.”

Har zuwa yanzu EFCC ba ta bayyana dalilin da ya sa ta tsare Ngige ba.

Ana sa ran hukumar za ta fitar da sanarwa game da kama shi da kuma binciken da ta ke yi a kansa.

Ngige ya zama mutum na biyu daga cikin tsoffin ministocin gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari da aka tsare a baya-bayan nan.

Tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami, shi ma yana hannun EFCC.

Hukumar ta ce tana binciken Malami ne kan wasu kuɗaɗen dala miliyan 310, wanda aka dawo da su Najeriya.

Sai dai ya musanta tuhumar da ake masa, inda ya bayyana cewa zarge-zargen ba su da tushe.

Masu sharhi a shafukan sada zumunta sun nuna damuwa kan yadda ake tsare tsoffin ministoci ba tare da bayyana dalili ba.

A gefe guda kuma, masu sharhi kan harkar siyasa sun ce irin wannan mataki na EFCC na nuna yadda hukumar ke zage damtse wajen yaƙi da cin hanci da rashawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Me Ke Kawo Yawaitar Juyin Mulki A Nahiyar Afirka?
  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Karatun Baya Dangane Da Tarihi Shi Ne Abun Da Ya Kamaci Japan
  • Yadda Rashin Bincike Ke Haifar Da Yawaitar Mutuwar Aure
  • Kungiyar NLC A Najeriya Ta Shirya Zanga-Zanga Kan Matsalar Rashin Tsaro A Fadin Kasa
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Babbar Kasuwar Fim Ta Sin Babbar Damar Nollywood Ce
  • NAFDAC Ta Ƙona Kayayyaki Marasa Inganci Na Naira Biliyan 5 A Nasarawa
  • NAJERIYA A YAU: Alfanu Da Kalubalen Sabon Jadawalin Karatun Makarantu Da Gwamnati Ta Bijiro Dashi
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige