Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Zanta Da Tokwaransa Na Kasar Kuwait
Published: 15th, April 2025 GMT
A zantawarsa ta wayar tarho da tokwaransa na kasar Kuwait, ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya ce tattaunawarsa da Abdullah Ali Al-Yahya ya fi bada karfi kan al-amuran yankin Asiya ta kudu musamman tattaunawa tsakanin Iran da Amurka kan shirinta na makamshin nukliya da kuma dagewa kasar takunkuman tattalin arzikin da aka dora mata.
A cikin tattaunawar dai ministan harkokin wajen kasar Kuwai y ace, kasashen yankin da dama sun ji dadin ganin cewa Iran da Amurka suna tattaunawa a tsakaninsu, kuma fatansu shi ne ya zama daga karshe kasashen biyu sun cimma dai-dato don warware matsalolin da ke tsakaninsu ta hanyar tattaunawa.
Aragchi ya bayyana cewa a halin yanzu ba zamu iya fadar menen sakamakon tattaunawar ba, amma da alamun kasashen biyu suna fatan kawo karshen tattaunawar da fahintar juna da kuma cimma yarjeniya mai amfanar bangarorin biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sudan ta soki shirun kasashen duniya game ta’asar dake faruwa a kasar
Ministan Harkokin Wajen Sudan Mohieldin Salem ya yi Allah wadai da shirun da kasashen duniya suka yi game da ci gaba da cin zarafin dan Adam da Rundunar Taimakon Gaggawa ta (RSF) ke yi a yankunan El-Fasher, Darfur ta Arewa, da Bara, da Kordofan ta Arewa.
Ya yi wadannan kalaman ne a lokacin wani taro a Port Sudan da Darakta Janar na Kungiyar Kula da kaura ta Duniya (IOM), Amy Pope, wacce ta isa Sudan don ziyarar kwanaki biyar, a cewar kamfanin dillancin labarai na SUNA.
Salem ya yi Allah wadai da shirun da kasashen duniya suka yi game da ci gaba da take hakkin dan adam da RSF ke yi a El-Fasher da Bara.
Ya jaddada bukatar hada karfi da karfe na kasa da kasa don ayyana RSF a matsayin kungiyar ta’addanci.
Ministan ya kuma sake jaddada cikakken kudurin gwamnati na samar da ayyukan jin kai da kuma tabbatar da tsaron ma’aikatan jin kai, yana mai nuna hadin gwiwa da ake ci gaba da yi da IOM, musamman a ayyukan da ke tallafawa komawar ‘yan gudun hijirar Sudan gida bisa rajin kansu.
Sudan na fuskantar mummunan rikicin jin kai sakamakon rikicin da ke tsakanin sojoji da RSF tun daga watan Afrilun 2023, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar dubban mutane tare da raba miliyoyi da gidajensu.
A ranar 26 ga Oktoba, RSF ta kwace iko da El-Fasher kuma ta yi kisan gilla a can, a cewar ƙungiyoyin cikin gida da na ƙasashen waje, duk da gargadin cewa harin zai iya ƙara ta’azzara rarrabuwar kawuna a ƙasar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hamas ta soki kudurin Isra’ila na yin dokar hukuncin kisa kan laifin ta’addanci November 11, 2025 Iran Za Ta Harba Taurarin Dan Adam Guda Uku Zuwa Sararin Samaniya November 11, 2025 Lebanon: An Saki Hannibal Kaddafi Bayan Zaman Kaso Na Shekaru 10 November 11, 2025 An Sake Bude Gidajen Mai Da Makarantu Da Aka Rufe A Kasar Mali November 11, 2025 Trump Ya Yi Wa Ma’aikatan Filayen Jiragen Sama Barazana November 11, 2025 Donald Trump Na Amurka Ya Karbi Bakuncin Shugaban Rikon Kwaryar Kasar Syria Ahmad Shar November 11, 2025 Amnesty Ta Kira Yi Gwamnatin Najeriya Da Ta Wanke ‘Yan Ogoni 9 Da Aka Zartarwa Da Hukuncin Kisa Shekaru 30 A Baya November 11, 2025 Hukumar Alhazai Ta Kasa A Nigeriya Ta sanar Da Rage Kudin Farashin Aikin Hajji Na Bana November 10, 2025 Hukumar Kare Hakkin Bil Adama Ta M D D Ta yi Gargadi Game Da Abin Da ke Faruwa A El-Fasher November 10, 2025 Iran Tayi Tir Da Rashin Kyakkyawar Niyyar Amurka Kan Batun Tattaunawa Bayan Kalaman Trump November 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci