HausaTv:
2025-12-15@04:39:29 GMT

Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Zanta Da Tokwaransa Na Kasar Kuwait

Published: 15th, April 2025 GMT

A zantawarsa ta wayar tarho da tokwaransa na kasar Kuwait, ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya ce tattaunawarsa da Abdullah Ali Al-Yahya ya fi bada karfi kan al-amuran yankin Asiya ta kudu musamman tattaunawa tsakanin Iran da Amurka kan shirinta na makamshin nukliya da kuma dagewa kasar takunkuman tattalin arzikin da aka dora mata.

A cikin tattaunawar dai ministan harkokin wajen kasar Kuwai y ace, kasashen yankin da dama sun ji dadin ganin cewa Iran da Amurka suna tattaunawa a tsakaninsu, kuma fatansu shi ne ya zama daga karshe kasashen biyu sun cimma dai-dato don warware matsalolin da ke tsakaninsu ta hanyar tattaunawa.

Aragchi ya bayyana cewa a halin yanzu ba zamu iya fadar menen sakamakon tattaunawar ba, amma da alamun kasashen biyu suna fatan kawo karshen tattaunawar da fahintar juna da kuma cimma yarjeniya mai amfanar bangarorin biyu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba

Shugaban hukumar makamashin Nukliya na kasar Iran Mohammad Islami ya bayyana cewa, kasar zata ci gaba a fannonin ilmi guda 6 na fasahar nukliya wato Fission, Fussion, Lasers, fasahar Quantum, da kuma Plasma duk tare da barazanar yaki, ko na siyasa ko kuma yakin kwakwalwan da makiya suke wa kasar.

Yace, matsayin  JMI a bayyana yake, kan cewa ba zata daina aikin ci gaba a fannonin ilmin makamashin nukliya don samun ci gaba a bangarorin kiwon lafiya da magunguna ba da wasu bangarorin ci gaba ba.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Islami yana fadar haka, a wani bukin kaddamar wasu sabbin kayakin aikin wadanda aka samar a cikin gida wadanda suka hada da ‘Plasma-Based drug synthesis da kuma wani sabon na’ura na jinyar gulando da fasahar Plasma jets.

A ranar 22 ga watan yunin da ya gabata ne gwamnatin kasar Amurka ta kaddamar da hare-hare kan cibiyoyin makamashin nukliya na kasar Iran dake Fordo, Natanz da kuma Esfahan da kawo karshen shirin a kasar, sannan ta yi haka ne a dai dai lokacinda Iran take tattaunawa da ita.

Muhammad Islami ya karada cewa kasar Iran zata ci gaba wajen bunkasa ilmin masu amfani ga kasar ba tare da wata matsala ba, ya ce, luguden wuta a kan cibiyoyin nukliyar kasar ba zasu tsada wannan ci gaban ba, haka ma yaki da takurawa ta tattalin arziki, siyasa da sauransu.

Yace mutanen kasar Iran ba zasu ci gaba da zama masu sayan ilmi daga waje ba. Musamman ilmomi masu muhimmanci ga ci gaban mutanemmu a wannan zamanin.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026 December 12, 2025  Turkiya A Shirye Take Ta Aike Da Sojoji Zuwa Yankin Gaza December 12, 2025 Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro  Na Venezuela Goyon Bayansa December 12, 2025 Ben Gafir Ya Sha Alwashin Rushe Kabarin Sheikh Izzuddin Alkassam December 12, 2025 Maduro: Amurka Ta Bude Sabon Salon Fashi Akan Doron Ruwa December 12, 2025 Ayatollah Khamenei : Iran na samun ci gaba duk da kalubale da dama December 11, 2025 Kyaftin Traoré : Yau Burkina ta zama misali a duniya December 11, 2025 Iran da Kazakhstan Sun rattaba hannu kan yarjeniyoyi da dama December 11, 2025 Hamas : Isra’ila ta gaza cika alkawarin da ta dauka kan yarjejeniyar tsagaita wuta December 11, 2025 Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu   December 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Bukaci Mutanen Yemen Su Daina Kashe Juna
  • Iran Tayi Tir Da Hare-Haren Sydney Na Kasar Austaralia
  • Iran Ta karbi Bakunci Taron Kasashen Dake Makwabtaka Da Afghanistan Da Rasha
  • Shuwagabannin Majalisar Kasar Iran Da Na Ethiopia Sun Gudanar Da Taron Manema Labarai
  • Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare
  • Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut
  • Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba