Aminiya:
2025-10-15@17:45:40 GMT

Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a Gaza

Published: 15th, April 2025 GMT

Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 tare da jikkata wasu 69 a cikin awa 24 a yankin Gaza, inda ta kai harin sama a wani asibiti da ke yankin Khan Younis.

Ma’aikatar Lafiyar Gaza ta sanar cewa jiragen Isra’ila sun kashe wani jami’in lafiya tare da jikkata wasu tara a Asibitin Kuwaiti da ke yankin Al-Musawi da ke Khan birnin Younis da ke Gabashin Gaza.

Mai magana da yawun asibitin, Saber Mohammed, ya bayyana cewa wadanda harin ya rutsa da su sun hada da marasa lafiya da kuma jami’an kiwon lafiya.

Isra’ila ba ta uffan a game da harin ba a halin yanzu, amma wasu rahotanni sun nuna jami’an tsaronta sun yi awon gaba da wasu Palasdinawa 14 a yankin Yamamcin Kogin Jordan.

Matashi ya yi yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a Kano Sojoji sun ceto mafiya 16 da aka yi garkuwa da wasu a Filato NAJERIYA A YAU: Dalilan Rikice-Rikice A Jihar Filato

Ofishin Kula da Fursunoni na Palasdinawa ya bayyana cewa yanacin mutanen an kama su ne a yankin Birnin Kudu, inda aka kama mutum uku a unguwar al-Issawiyya da ke Gabashin Birnin Kudus da wasu uku a garin Anata.

A yankin Ramallah kuma na jami’an Isra’ila sun kama Palasinawa uku a garin Al-Mazarra’a Ash-Sharqiya da kuma wani mutum guda a kauyen Kobar.

Sun kuma kama wani mutum guda a unguwar Ezbet al-Jarad da ke birin Tulkarem da wani guda kuma a Ezbet al-Tayah.A yankin Nablu kuma Isra’ila ta kama Palasdinawa uku a yankunan Beit Furik da kuma birnin Nablus.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila Palasdinawa

এছাড়াও পড়ুন:

Faɗa ya ɓarke tsakanin Palasɗinawa da Hamas bayan sulhu da Isra’ila

Rahotanni sun bayyana cewa wani ƙazamin faɗa ya barke tsakanin wata ƙabilar Palasɗinawa masu ɗauke da makamai da ƙungiyar Hamas a yankin zirin Gaza bayan an kulla yarjejeniyar zaman lafiya da Isra’ila.

A ranar Litinin da aka fara musayar fursunoni tsakanin Hamas da Isra’ila ne rahotanni suka ɓulla game da faɗan da ya ɓarke tsakanin mayaƙan Hamas da ƙabilar Doghmush a ranar Lahadi.

Wani jami’in Hamas ya bayyana cewa an samu asarar rayuka daga kowane ɓangare a yayin musayar wutan daga misalin ƙarfe 9.30 na dare ranar Lahadi.

Wani mazaunin yankin Sebra da ke Birnin Gaza, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na AFP cewa “Mayaƙan Hamas kimanin 200 ne suka zo aka fafata da su, har sai da suka murƙushe ’yan ƙabilar Doghmush.

Issa Bakary Tchiroma ne ya lashe zaɓen Kamaru —’Yan adawa NAJERIYA A YAU: Shin Babu Wata Hanyar Magance Matsalolin ASUU Ne Sai Ta Yajin Aiki?

“Wasu ’yan ƙabilar da mayaƙan Hamas sun rasu a yayin artabun,” in ji shi yana mai neman a dakata sunansa saboda dalilan tsaro.

Wata majiya daga ma’aikatar harkokin cikin gida ta Hamas ta zargi ’yan ƙabilar da yi wa sojojin Isra’ila aiki kuma sun kashe mutane da dama, ta ƙara da cewa an tsare mutum shiga daga danginsu.

Iyalan sun musanta zargin da ake musu na yi wa Isra’ila aiki, amma sun amsa cewa sun kai wasu farmaki ba tare da yin ƙarin haske ba.

Sun kuma zargi Hamas da kai musu hari barkatai, kamar yadda AFP ya ruwaito.

Shugaban kabilar, Abu al-Hassan Doghmush, ya wallafa a Facebook cewa abin “ya kai matakin da in dai kai dan ƙabilarmu ce to a iya harbin ka a ƙafa koma kone maka gida.”

Tun da Hamas ta kwace iko a yankin Gaza a 2007 ta sha fama da kabilu da ƙungiyoyi masu ɗaukar makamai.

A ranar Lahadi ne kungiyar ta sanar da afuwa ga duk kungiyoyin masu laifi, waɗanda ba su aikata kisa a lokacin yaƙin ƙasar da Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila  Za Ta Sake Kai Hare-hare Idan Ta Karbi Dukkan Mutanenta Da Hamas Ta Kama.
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 1, sun sace dabbobi a Katsina
  • A Lokacin Yaki, Iran Ta Tarwatsa Wata Cibiyar Leken Asirin Yahudawan Sahayoniyya Da Ke Yankin Farar Hula
  • An kama mata da miji suna safarar makamai a Kaduna
  • An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa
  • Faɗa ya ɓarke tsakanin Palasɗinawa da Hamas bayan sulhu da Isra’ila
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni
  • Yemen Ta Gargadi Isra’ila Kan Fuskantar Hare-Hare Idan Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta