Aminiya:
2025-12-11@00:08:48 GMT

Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a Gaza

Published: 15th, April 2025 GMT

Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 tare da jikkata wasu 69 a cikin awa 24 a yankin Gaza, inda ta kai harin sama a wani asibiti da ke yankin Khan Younis.

Ma’aikatar Lafiyar Gaza ta sanar cewa jiragen Isra’ila sun kashe wani jami’in lafiya tare da jikkata wasu tara a Asibitin Kuwaiti da ke yankin Al-Musawi da ke Khan birnin Younis da ke Gabashin Gaza.

Mai magana da yawun asibitin, Saber Mohammed, ya bayyana cewa wadanda harin ya rutsa da su sun hada da marasa lafiya da kuma jami’an kiwon lafiya.

Isra’ila ba ta uffan a game da harin ba a halin yanzu, amma wasu rahotanni sun nuna jami’an tsaronta sun yi awon gaba da wasu Palasdinawa 14 a yankin Yamamcin Kogin Jordan.

Matashi ya yi yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a Kano Sojoji sun ceto mafiya 16 da aka yi garkuwa da wasu a Filato NAJERIYA A YAU: Dalilan Rikice-Rikice A Jihar Filato

Ofishin Kula da Fursunoni na Palasdinawa ya bayyana cewa yanacin mutanen an kama su ne a yankin Birnin Kudu, inda aka kama mutum uku a unguwar al-Issawiyya da ke Gabashin Birnin Kudus da wasu uku a garin Anata.

A yankin Ramallah kuma na jami’an Isra’ila sun kama Palasinawa uku a garin Al-Mazarra’a Ash-Sharqiya da kuma wani mutum guda a kauyen Kobar.

Sun kuma kama wani mutum guda a unguwar Ezbet al-Jarad da ke birin Tulkarem da wani guda kuma a Ezbet al-Tayah.A yankin Nablu kuma Isra’ila ta kama Palasdinawa uku a yankunan Beit Furik da kuma birnin Nablus.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila Palasdinawa

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC ta tsare Malami kan binciken kuɗaɗen Abacha

Hukumar EFCC ta tsare tsohon Antoni-Janar na Tarayya, Abubakar Malami, saboda binciken da ya shafi dawo da wani ɓangare na kuɗaɗen Abacha.

Hukumar ta kira Malami a makon da ya gabata, inda ta yi masa tambayoyi kan wani bincike da ta ke inda ta sake shi daga bisani, amma yanzu ta tsare shi.

Real Madrid  za ta ɓarje gumi da Manchester City a Santiago Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro

Malami ya ce bai aikata komai ba, kuma ba shi da alaƙa da abin da ake zargi.

A cikin wata sanarwa, ya ce: “Ba a taɓa zargina, gayyata ko bincikena game da tallafa wa ta’addanci ba. Duk wani yunƙuri na danganta ni da irin wannan laifi ƙarya ne.”

Ya ƙara da cewa rahotannin kafofin yaɗa labarai ke watsawa sun yi masa mummunar fassara.

“Ba daidai ba ne a ce aikina na gwamnati ya zama hujja ta tallafa wa ta’addanci. A lokacin aikina, na yi aiki tuƙuru wajen ƙarfafa yaƙi da ta’addanci, ba goyon bayansa ba.”

EFCC ba ta fitar da wata sanarwa kan tsare Malami ba.

Haka kuma bai wallafa komai a shafukan sada zumunta ba tsawon kwanaki huɗu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD
  • Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye
  • EFCC ta tsare Malami kan binciken kuɗaɗen Abacha
  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kai Hare-Hare Kan Sojojin Pakistan Sun Kuma Kashe 6 Daga Cikinsu
  • Kasar China Ta Zartar Da Hukuncin Kisa Akan Wani Babban Jami’in Banki
  • RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne
  • ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
  • MِِِِDD:  Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya