Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a Gaza
Published: 15th, April 2025 GMT
Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 tare da jikkata wasu 69 a cikin awa 24 a yankin Gaza, inda ta kai harin sama a wani asibiti da ke yankin Khan Younis.
Ma’aikatar Lafiyar Gaza ta sanar cewa jiragen Isra’ila sun kashe wani jami’in lafiya tare da jikkata wasu tara a Asibitin Kuwaiti da ke yankin Al-Musawi da ke Khan birnin Younis da ke Gabashin Gaza.
Mai magana da yawun asibitin, Saber Mohammed, ya bayyana cewa wadanda harin ya rutsa da su sun hada da marasa lafiya da kuma jami’an kiwon lafiya.
Isra’ila ba ta uffan a game da harin ba a halin yanzu, amma wasu rahotanni sun nuna jami’an tsaronta sun yi awon gaba da wasu Palasdinawa 14 a yankin Yamamcin Kogin Jordan.
Matashi ya yi yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a Kano Sojoji sun ceto mafiya 16 da aka yi garkuwa da wasu a Filato NAJERIYA A YAU: Dalilan Rikice-Rikice A Jihar FilatoOfishin Kula da Fursunoni na Palasdinawa ya bayyana cewa yanacin mutanen an kama su ne a yankin Birnin Kudu, inda aka kama mutum uku a unguwar al-Issawiyya da ke Gabashin Birnin Kudus da wasu uku a garin Anata.
A yankin Ramallah kuma na jami’an Isra’ila sun kama Palasinawa uku a garin Al-Mazarra’a Ash-Sharqiya da kuma wani mutum guda a kauyen Kobar.
Sun kuma kama wani mutum guda a unguwar Ezbet al-Jarad da ke birin Tulkarem da wani guda kuma a Ezbet al-Tayah.A yankin Nablu kuma Isra’ila ta kama Palasdinawa uku a yankunan Beit Furik da kuma birnin Nablus.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Isra ila Palasdinawa
এছাড়াও পড়ুন:
Trump zai haramta wa ’yan Najeriya da wasu ƙasashe zuwa Amurka
Shugaban Amurka Donald Trump, ya bayyana cewa yana shirin daina karɓar mutane daga “ƙasashe masu tasowa” gaba ɗaya, ciki har da Afirka, Asiya da sauransu.
Ya bayyana haka ne yayin wani taro da ya gudana a fadar shugaban Amurka.
Ƙasar Japan ta fara sayar da i njin da ke yi wa mutane wankaA cewarsa, tsohon tsarin shige da fice na Amurka yana rage ƙarfin tsaron ƙasa kuma yana matsa wa makarantun gwamnati, asibitoci, da sauran hidimomin jama’a.
Trump ya ce yawan baƙin haure a Amurka ya kai mutane miliyan 53, sannan ya yi zargin cewa mutane daga ƙasashen da ke fama da rikice-rikice, laifuka, da miyagun ƙungiyoyi suna ta zuwa ƙasar.
Ya ce shigowar baƙi ya kawo rabuwar kawuna da matsaloli a Amurka.
Haka kuma ya yi zargin cewa masu katin zama ’yan ƙasar da ke da tsarin ƙaramin albashi na rikice-rikice.
Ya batar da misali da Jihar Minnesota, yana inda ’yan gudun hijira daga Somaliya suka cika ta
Ya ce “ci gaban ƙasa ya lalace,” amma ya bayyana matakan da zai ɗauka.
Ya kuma ce zai soke shiga ƙasar ba bisa ƙa’ida ba wanda gwamnatin Biden ta bari ke faruwa.
Trump, ya ce burinsa shi ne rage yawan waɗanda yake ganin ba su da tasiri mai kyau ko kuma suna kawo matsala a ƙasar.
Ya ce “mayar da mutane ƙasashensu” shi ne kawai mafita mai ɗorewa.
Wannan sanarwa na zuwa ne bayan harin da aka kai a Washington, D.C, inda aka yi wa sojoji biyu rauni.
Hukumomi a ƙasar sun ce mutumin da ake zargi da kai harin, ya shiga Amurka a 2021 bayan ya taimaka wa sojojin ƙasar a Afghanistan, kuma an ba shi mafaka.