Aminiya:
2025-06-30@22:38:55 GMT

Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a Gaza

Published: 15th, April 2025 GMT

Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 tare da jikkata wasu 69 a cikin awa 24 a yankin Gaza, inda ta kai harin sama a wani asibiti da ke yankin Khan Younis.

Ma’aikatar Lafiyar Gaza ta sanar cewa jiragen Isra’ila sun kashe wani jami’in lafiya tare da jikkata wasu tara a Asibitin Kuwaiti da ke yankin Al-Musawi da ke Khan birnin Younis da ke Gabashin Gaza.

Mai magana da yawun asibitin, Saber Mohammed, ya bayyana cewa wadanda harin ya rutsa da su sun hada da marasa lafiya da kuma jami’an kiwon lafiya.

Isra’ila ba ta uffan a game da harin ba a halin yanzu, amma wasu rahotanni sun nuna jami’an tsaronta sun yi awon gaba da wasu Palasdinawa 14 a yankin Yamamcin Kogin Jordan.

Matashi ya yi yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a Kano Sojoji sun ceto mafiya 16 da aka yi garkuwa da wasu a Filato NAJERIYA A YAU: Dalilan Rikice-Rikice A Jihar Filato

Ofishin Kula da Fursunoni na Palasdinawa ya bayyana cewa yanacin mutanen an kama su ne a yankin Birnin Kudu, inda aka kama mutum uku a unguwar al-Issawiyya da ke Gabashin Birnin Kudus da wasu uku a garin Anata.

A yankin Ramallah kuma na jami’an Isra’ila sun kama Palasinawa uku a garin Al-Mazarra’a Ash-Sharqiya da kuma wani mutum guda a kauyen Kobar.

Sun kuma kama wani mutum guda a unguwar Ezbet al-Jarad da ke birin Tulkarem da wani guda kuma a Ezbet al-Tayah.A yankin Nablu kuma Isra’ila ta kama Palasdinawa uku a yankunan Beit Furik da kuma birnin Nablus.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila Palasdinawa

এছাড়াও পড়ুন:

Bincike Ya Tabbatar da Cewa HKI Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 Tun Bayan Fara Yaki A Gaza

Masu bincike sun gano cewa sojojin HKI sun kashe Falasdinawa akalla 100,000 tun bayan fara yakin tufanul Aksa a ranar 7 ga watan Octoban shekara 2023.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kan cewa farfesa Michael Spagat da kuma Khalil Shikaki  Bafalasdine masanin masanin fasahar siyasa a Jami’ar London na kasar Burtania suka jagoranci bincike wanda ya kai ga fitar da wannan sakamakon.

Labarin ya kara da cewa masu binciken sun kiyasta mutane a gidaje 2000 a birnin  Gaza kadai wanda falasdinawa kimani 10,000 suke rayuwa, sannan suka yi lissafi suka kaim ga wannan sakamakon.

Bincike ya kara da cewa daga watan jenerun shekara ta 2025 falasdinawa 75,200 sojojin yahudawan suka kashe da makamai, sannan wasu kimani 8,540 sun mutu sabada yunwa da karancin magunguna da kuma wasu hanyoyi ba da wuta ba.

Amma ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza ta bayyana cewa daga watan Jeneru zuwa yanzu sojojin yahudawan sun kashe falasdinawa 10,000.

Ma’aikatar ta kara da cewa a baya bayan nan sojojin yahudawa suna kashe Falasdinawa a wuraren karban abinci da suka shirya a matsayin tarko ga Falasdinawa wadanda suke fama daga tsananin yunwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe ubangidan Turji, Kacalla Ɗanbokolo a Zamfara
  • HKI Ta Kashe Falasdinawa 72 A Cikin Gaza A Yua Litinin
  •  Wani Dan Bindiga Dadi Ya Kashe Ma’aikatan Kashe Gobara 2 A Amurka
  • Iran: An Kama Wani Dan Leken Asirin “Mosad” A Tehran A Jiya Lahadi
  • Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
  • Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila
  • Bincike Ya Tabbatar da Cewa HKI Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 Tun Bayan Fara Yaki A Gaza
  • Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
  • Yunwa ta kashe ƙananan yara 66 a Gaza
  • ‘An kashe ’ya’yana da mijina da ’yan uwana a hanyar ɗaurin auren ɗana’