Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a Gaza
Published: 15th, April 2025 GMT
Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 tare da jikkata wasu 69 a cikin awa 24 a yankin Gaza, inda ta kai harin sama a wani asibiti da ke yankin Khan Younis.
Ma’aikatar Lafiyar Gaza ta sanar cewa jiragen Isra’ila sun kashe wani jami’in lafiya tare da jikkata wasu tara a Asibitin Kuwaiti da ke yankin Al-Musawi da ke Khan birnin Younis da ke Gabashin Gaza.
Mai magana da yawun asibitin, Saber Mohammed, ya bayyana cewa wadanda harin ya rutsa da su sun hada da marasa lafiya da kuma jami’an kiwon lafiya.
Isra’ila ba ta uffan a game da harin ba a halin yanzu, amma wasu rahotanni sun nuna jami’an tsaronta sun yi awon gaba da wasu Palasdinawa 14 a yankin Yamamcin Kogin Jordan.
Matashi ya yi yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a Kano Sojoji sun ceto mafiya 16 da aka yi garkuwa da wasu a Filato NAJERIYA A YAU: Dalilan Rikice-Rikice A Jihar FilatoOfishin Kula da Fursunoni na Palasdinawa ya bayyana cewa yanacin mutanen an kama su ne a yankin Birnin Kudu, inda aka kama mutum uku a unguwar al-Issawiyya da ke Gabashin Birnin Kudus da wasu uku a garin Anata.
A yankin Ramallah kuma na jami’an Isra’ila sun kama Palasinawa uku a garin Al-Mazarra’a Ash-Sharqiya da kuma wani mutum guda a kauyen Kobar.
Sun kuma kama wani mutum guda a unguwar Ezbet al-Jarad da ke birin Tulkarem da wani guda kuma a Ezbet al-Tayah.A yankin Nablu kuma Isra’ila ta kama Palasdinawa uku a yankunan Beit Furik da kuma birnin Nablus.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Isra ila Palasdinawa
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin mota
Aƙalla ɗalibai takwas na Jami’ar Jos ne aka ruwaito sun mutu, yayin da wasu uku suka samu munanan raunuka, a wani mummunan hatsarin da ya rutsa da wata tirela da wata motar bas.
Hatsarin ya faru ne a hanyar Zariya, cikin ƙaramar hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato.
NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a YobeLamarin ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na tsakar daren ranar Alhamis lokacin da ɗaliban ke dawowa daga wani biki.
Jami’in kula da wayar da kan jama’a na hukumar kiyaye haɗɗura ta ƙasa (FRSC) Peter Yakubu Longsan ne ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa motar bas ɗin na ɗauke da ɗalibai 11 na Jami’ar.
A cewar Hukumar ta FRSC, shaidun gani da ido sun danganta hatsarin da tsananin gudu na direban motar yake yi na wuce gona da iri.
Da yake bayar da cikakken bayani kan lamarin, Longsan ya bayyana cewa, “A yau 11 ga Disamba, 2025, Hukumar FRSC reshen Jihar Filato ta samu kiran waya da misalin ƙarfe 02:30 na tsakar dare, inda aka ba da rahoton wani haɗarin mota da ya afku a kusa da hanyar Zariya wajen Unity Bank, a Jos.
“Hatsarin ya haɗa da motoci biyu, tirela da bas, mutum 11 ne a cikin motar kuma an ce ɗaliban jami’ar Jos ne. Da faruwar lamarin ne mutum bakwai ake zargin nan take sun mutu, domin daga ƙarshe likita ya tabbatar da cewa sun mutu, sai kuma wani da ya mutu a asibitin wanda ya kawo adadin waɗanda suka mutu zuwa takwas.
“A yanzu haka wasu uku suna karɓar magani a asibitin, dukkan waɗanda abin ya rutsa da su maza ne, kamar yadda wani ganau ya shaida cewar motar bas ɗin na cikin tsananin gudu, lamarin da ya kai ga rasa natsuwa daga bisani kuma lamarin ya faru. A halin yanzu dai ana ci gaba da gudanar da cikakken bincike,” in ji shi.