An Kashe Sojojin Yahudawa A Gaza A Yayinda Wasu Da Dam Suka Ji Rauni
Published: 15th, April 2025 GMT
Majiyar Falasdinawa a Gaza sun bada labarin kissan wasu sojojin HKI a unguwar Shuja’iyya kusa da Gaza a jiya Litini, inda wasu kuma suka ji rauni.
Kafafen yada labarai da yahudawan da kuma larabawa sun bayyana cewa kungiyar Jihadul Islami a Gaza ta ce nayakanta masu farautar yahudawa daga nesa sun bayyana cewa suk halaka wasu yahudawa wadanda suka boye a wani gida a garin Rafah kudancin Gaza, inda suke halakasu.
Sannan a sauran wuraren kuma sojojin yahudawan da dama ne suka ji rauni. Kuma sun ga jiragen yakin masu sauran ungulu na yahudawan sun zo sun tafi da wadanda abin ya shafa.
Wannan dai kadan Kenan daga hare-haren maida martanin da dakarun falasdinawan suke mayarwa ga sojojin yahudawan, tun lokacinda suka koma yaki kimani watanni biyu da suka gabata. Ya wan Falasdinawan da suka yi shahada tun bayan fara yakin Tufanul Aksa a ranra 7 ga watan Octoban shekara ta 20230 dai sun kai mutun 51,000 a yayinda wadanda suka ji rauni kuma suka kai fiye da 120,000. Mafi yawan wadanda abin ya shafa mata da yara ne.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Hamas Ta Yi Fatali Da Mahangar Yahudawan Sahayoniyya Ta Neman Falasdinawa Su Rusuna Musu
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta jaddada cewa: Gaza ba za ta mika wuya ba don haka ‘yan gwagwarmaya ne zasu gindaya sharudda
Izzat al-Rishq mamba a ofishin yada labarai na kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ya bayyana cewa: Kalaman fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu na sakin dukkan fursunonin da suke hannun ‘yan gwagwarmaya da kuma mika wuyar Hamas sun sabawa matakin hankali da hakikanin abin da ke gudana a fagen yaki.
Al-Rashq ya tabbatar a cikin wani takaitaccen bayani a shafinsa na Telegram da sanyin safiyar Larabar nan cewa: Bayan da shugabannin ‘yan mamaya makiya suka amince da gazawar da suka yi wajen kwato fursunoninsu ta hanyar karfin soja; Ya bayyana cewa babu yadda za a yi a sake su sai ta hanyar sharuddan da ‘yan gwagwarmaya suka gindaya.
Ya jaddada cewa: Gaza ba za ta mika wuya ba, kuma ‘yan gwagwarmaya zasu gindaya sharudda, kamar yadda ta sanya ma’aunin da ya dace abi.
Kafofin yada labarai sun ambato Netanyahu yana fadar haka daga Washington cewa: Dole ne Gaza ta samu wata makoma ta daban, kuma har yanzu dole ne su kammala aikin sakin dukkan fursunoni tare da kawar da karfin soji da na gwamnatin Hamas gaba daya.