An Kashe Sojojin Yahudawa A Gaza A Yayinda Wasu Da Dam Suka Ji Rauni
Published: 15th, April 2025 GMT
Majiyar Falasdinawa a Gaza sun bada labarin kissan wasu sojojin HKI a unguwar Shuja’iyya kusa da Gaza a jiya Litini, inda wasu kuma suka ji rauni.
Kafafen yada labarai da yahudawan da kuma larabawa sun bayyana cewa kungiyar Jihadul Islami a Gaza ta ce nayakanta masu farautar yahudawa daga nesa sun bayyana cewa suk halaka wasu yahudawa wadanda suka boye a wani gida a garin Rafah kudancin Gaza, inda suke halakasu.
Sannan a sauran wuraren kuma sojojin yahudawan da dama ne suka ji rauni. Kuma sun ga jiragen yakin masu sauran ungulu na yahudawan sun zo sun tafi da wadanda abin ya shafa.
Wannan dai kadan Kenan daga hare-haren maida martanin da dakarun falasdinawan suke mayarwa ga sojojin yahudawan, tun lokacinda suka koma yaki kimani watanni biyu da suka gabata. Ya wan Falasdinawan da suka yi shahada tun bayan fara yakin Tufanul Aksa a ranra 7 ga watan Octoban shekara ta 20230 dai sun kai mutun 51,000 a yayinda wadanda suka ji rauni kuma suka kai fiye da 120,000. Mafi yawan wadanda abin ya shafa mata da yara ne.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Sun jaddada cewa dole ne manyan kafafen sada zumunta su kare ‘yancin yin magana.
Sun kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya, ‘yan jarida, da masu fafutukar kare haƙƙin bil’adama su tashi tsaye don hana abin da suka kira yunƙurin mayar da Nijeriya “mulkin kama-karya a intanet.”
Lamarin ya biyo bayan wa’adin sati guda da DSS ta bai wa Sowore da ya goge wasu wasu rubuce-rubuce game da Shugaba Bola Tinubu, wanda ya ƙi amincewa.
Hakan ya sa hukumar ta shigar da shi ƙara a kotu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp