Amurka ta janye harajin kayan laturoni da ake shiga da su ƙasar
Published: 13th, April 2025 GMT
Gwamnatin Amurka ta sanar da janye sabon harajin da ta ƙaƙaba wa kayayyakin laturoni irin su wayoyin salula, kwamfutoci da sauran na’urorin da ake shigo mata daga ƙetare.
Ana sa ran matakin ya rage raɗaɗin tashin farashin kayayyakin da zai faru a Amurka bayan da a kwanaki Shugaba Donald Trump ya lafta wa ƙasashe ciki har da China haraji kan kayayyakin da ake shigowa da su ƙasar.
Sai dai gwamnatin ta Amurka wacce ta sanar da sassaucin ta hannun hukumar kwastam ba ta bayyana dalilin cire harajin ba.
Amma dai ana sa ran kamfanonin fasaha na Amurka kamar Apple da Dell za su ci gajiyar hakan matuƙa, ganin yawancin kayayyakinsu ana haɗa su ne a China.
Trump ya janye harajin wayoyi da kwamfutoci.
Bayanai sun ce sassaucin na zuwa ne bayan kamfanonin fasahar zamani na Amurkan sun koka kan yadda na’urori za su yi tashin gwauron zabi, saboda yawancinsu daga China suke sayensu, musamman ma iPhone da kusan kashi 80 na wayoyin Amurkawa ke amfani da su.
Masana sun ce wannan sauƙin zai rage hauhawar farashi da kuma matsin da masana’antar harkokin fasahar zamani ke fuskanta.
Tuni China ta mayar da martani da ƙarin haraji har kashi 125% kan kayayyakin Amurka da ke shiga ƙasar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Haraji kwamfutoci
এছাড়াও পড়ুন:
Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce za a yi taro karo na hudu na shawarwari tsakanin Tehran da Washington kan shirin nukiliyar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a birnin Rome na kasar Italiya a ranar Asabar mai zuwa.
M. Araghchi ya fadawa manema labarai a gefen taron majalisar ministocin gwamnatin kasar na mako-mako yau Laraba cewa, inda ya ce taron na Rome zai kasance gabanin wani taro a ranar Juma’a na tsakanin Tehran da kasashen Turan nan uku da ake wa lakabi da E3 wato – Ingila, Faransa da kuma Jamus wadanda suka sanya hannu kan yarjejeniyar nukiliyar Iran ta 2015.
Ya ce rawar da kasashen Turai uku ke takawa ta ragu sakamakon manufofinsu a tattaunawar da aka dade ana yi, don haka a shirye muke mu gudanar da zagaye na gaba na shawarwari da su a birnin Rome.
Babban jami’in diflomasiyyar ya kara da cewa, Tehran na da burin warware batun nukiliyarta cikin lumana.”
Da aka tambaye shi game da halin da ake ciki na baya-bayan nan na kudaden da Iran ta toshe saboda takunkumin da kasashen yamma suka kakaba mata, Araghchi ya ce daskararrun kudaden na daga cikin takunkumin da ya zama dole a dagewa iran.
Kawo yanzu Iran da Amurka sun yi tattaunawa har uku ta farko a Oman, ta biyu a Italiya sai kuma wace aka gudanar a ranar Asabar data gabata a Oman.
Dukkanin bangarorin na cewa akwai fata mai kyau a jerin tattaunawar da suka gabata.