Amurka ta janye harajin kayan laturoni da ake shiga da su ƙasar
Published: 13th, April 2025 GMT
Gwamnatin Amurka ta sanar da janye sabon harajin da ta ƙaƙaba wa kayayyakin laturoni irin su wayoyin salula, kwamfutoci da sauran na’urorin da ake shigo mata daga ƙetare.
Ana sa ran matakin ya rage raɗaɗin tashin farashin kayayyakin da zai faru a Amurka bayan da a kwanaki Shugaba Donald Trump ya lafta wa ƙasashe ciki har da China haraji kan kayayyakin da ake shigowa da su ƙasar.
Sai dai gwamnatin ta Amurka wacce ta sanar da sassaucin ta hannun hukumar kwastam ba ta bayyana dalilin cire harajin ba.
Amma dai ana sa ran kamfanonin fasaha na Amurka kamar Apple da Dell za su ci gajiyar hakan matuƙa, ganin yawancin kayayyakinsu ana haɗa su ne a China.
Trump ya janye harajin wayoyi da kwamfutoci.
Bayanai sun ce sassaucin na zuwa ne bayan kamfanonin fasahar zamani na Amurkan sun koka kan yadda na’urori za su yi tashin gwauron zabi, saboda yawancinsu daga China suke sayensu, musamman ma iPhone da kusan kashi 80 na wayoyin Amurkawa ke amfani da su.
Masana sun ce wannan sauƙin zai rage hauhawar farashi da kuma matsin da masana’antar harkokin fasahar zamani ke fuskanta.
Tuni China ta mayar da martani da ƙarin haraji har kashi 125% kan kayayyakin Amurka da ke shiga ƙasar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Haraji kwamfutoci
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya gana da sabbin hafsoshin tsaro
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wata ganawar sirri da sabbin hafsoshin tsaron Najeriya a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.
Sai dai babu wani cikakken bayani kan dalilin ko maudu’in wannan taron, wanda shi ne karo na farko bayan sauya manyan hafsoshin tsaron Najeriya da shugaban ƙasar ya yi.
An kashe wasu makiyaya 10 a Kebbi Zanga-zanga ta ɓarke a KamaruSai dai wata majiya daga fadar shugaban kasar ta ce taron ba zai nasaba da ƙoƙarin da ake yi na ƙarfafa tsarin tsaro da inganta aikin rundunar sojoji a ƙasar nan ba.
Aminiya ta ruwaito cewa, a makon jiya ne Shugaba Tinubu ya tuɓe hafsan hafsoshin Najeriya, Janaral Christopher Musa da sauran hafsoshin tsaron ƙasar, a wani sauyi a tsarin jagorancin sojin ƙasar domin inganta da ƙarfafa sha’anin tsaro a Najeriya.
Wata sanarwa da fadar shugaban ƙasar ta fitar ta ce Tinubu ya yi musu fatan alkairi tare da bayyana sunayen sabbin hafsoshin da za su maye gurbin waɗanda aka sauke ɗin.
Sabbin hafsoshin tsaron da Tinubu ya nada sun hada da Janar Olufemi Oluyede — Hafsan Hafsoshi da Manjo Janar W Sha’aibu — Hafsan sojojin ƙasa da Air Vice Marshall S.K Aneke — Hafsan sojin sama.
Akwai kuma Rear Admiral I. Abbas — Hafsan sojin ruwa da Manjo Janar E.A.P Undiendeye — Shugaba sashen tattara bayan sirri na soji.