Zargin N6.5bn: Ya kamata a dakakar da hadimin Gwamnan Kano — Ƙungiyoyi
Published: 25th, August 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano ta yi shiru yayin da wasu ƙungiyoyin farar hula suka buƙaci ta dakatar da manyan jami’abta da ake zargi da almundahana ta biliyoyin naira tare da gurfanar da su a gaban kotu.
Wani rahoto na kafar yaɗa labarai ta Daily Nigerian ya bayyana cewa hukumomin ICPC da EFCC masu ya ki da almundahana sun gano badaƙalar Naira biliyan 6.
Takardun da kafar ta ambato cewa ta samu suna zargin almundahanar ta faru ne tsakanin watan Nuwambar 2023 da Fabrairun 2025 ta hanyar kwangilolin bogi da sunan kamfanonin H&M Construction Nigeria Ltd, A.Y. Maikifi Petroleum da Ammas Oil & Gas Ltd.
Sai dai duk ƙoƙarin jin ta bakin gwamnatin jihar ya ci tura, yayin da Kwamishinan Watsa Labarai, Ibrahim Wayya da Sakataran Gwamna ba su ɗauki kiran waya ba, kuma Darakta Janar na Watsa Labarai na Gwamnan, Sunusi Bature ya yi bukaguro zuwa ƙasar waje.
Wannan dambarwar na zuwa ne bayan rahoton jaridar Nigerian Tribune a watan Yuli 2025, wanda ya bayyana cewa ICPC ta kammala bincike kan badaƙalar Naira biliyan 1.02 da ake zargin jami’an Hukumar Zaɓe ta Jihar Kano (KANSIEC).
A wata sanarwa da wasu ƙungiyoyin fararen hula 20 suka sa hannu, sun yi gargaɗi cewa zarge-zargen na iya ɓata amincewar jama’a da gwamnati, tare da sare gwiwar masu zuba jari daga ƙasashen waje da kuma durƙushewar da ci-gaban jihar.
“Wannan ba ƙaramin lamari ba ne. Ya nuna tsarin almundahana ta hanyar amfani da muƙaman gwamnati don amfanin kai,” in ji ƙungiyoyin.
Sun kuma buƙaci a dakatar da duk jami’an da ake zargi tare da gudanar da bincike mai zaman kansa kan dukkanin ma’aikatun gwamnati.
Haka kuma sun buƙaci Majalisar Dokokin Jihar Kano ta ƙarfafa aikin sa ido tare da kafa dokar kare waɗanda ke fallasa rashawa.
“Zaɓi yana a hannunmu: ko mu yaƙi rashawa mu dawo da martabar shugabanci ko kuma mu bari ta ƙara zurfi har ta kai ga rugujewar cibiyoyinmu da makomar ’ya’yanmu,” in ji sanarwar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
Hukumar Tace Fina-Finai da Dab’i ta Jihar Kano ta haramta shirya duk wata muƙabala tsakanin mawaƙan yabon Annabi (S.A.W), tare da gayyatar mawaƙa Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi su bayyana a gabanta.
Hukumar ta kuma gayyaci mawaƙan ne tare da sauran waɗanda suka jagoranci muƙabalar da fitattun mawaƙan biyu suka yi ranar Litinin, da su bayyana a gabanta cikin sa’o’i 24.
Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin TinubuHakan na zuwa ne ƙasa da kwana ɗaya bayan ɓullar wata muhawara da aka yi tsakanin Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi kuma ta karade shafukan sada zumunta, wacce hukumar ta bayyana a matsayin karya dokokin aikinta.
Shugaban hukumar, Abba El-Mustapha ne ya sanar da hakan ranar Talata, inda ya ce ɗaukar matakin wani yunƙuri ne na tabbatar da zaman lafiya, daidaito da bin doka tsakanin mawaƙan nishaɗi da na addini.
El-Mustapha, a cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar, ya kuma ce an haramta duk wata nau’in muƙabala daga mawaƙan addini a jihar ba tare da izinin hukumar ba.
A yayin da yake ƙaddamar da wani kwamitin bincike da shugaban hukumar ya naɗa karkashin Daraktan Ayyuka na Musamman a hukumar, Isah Abdullahi, El-Mustapha ya umarci waɗanda aka gayyatar da su bayyana a gaban kwamitin domin amsa tambayoyi.
Hukumar ta ce shirya irin waɗannan muhawara ba tare da izininta ba ya saɓa doka kuma zai iya jawo hukunci mai tsanani ga wanda suka karya.
Hukumar ta kuma jaddada ƙudirinta na ci gaba da kula da ayyukan mawaƙan da masu nishaɗantarwa a faɗin jihar tare da yin kira ga jama’a da su zauna lafiya sannan su ci gaba da ba ta haɗin kai a ayyukanta.