Zargin N6.5bn: Ya kamata a dakakar da hadimin Gwamnan Kano — Ƙungiyoyi
Published: 25th, August 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano ta yi shiru yayin da wasu ƙungiyoyin farar hula suka buƙaci ta dakatar da manyan jami’abta da ake zargi da almundahana ta biliyoyin naira tare da gurfanar da su a gaban kotu.
Wani rahoto na kafar yaɗa labarai ta Daily Nigerian ya bayyana cewa hukumomin ICPC da EFCC masu ya ki da almundahana sun gano badaƙalar Naira biliyan 6.
Takardun da kafar ta ambato cewa ta samu suna zargin almundahanar ta faru ne tsakanin watan Nuwambar 2023 da Fabrairun 2025 ta hanyar kwangilolin bogi da sunan kamfanonin H&M Construction Nigeria Ltd, A.Y. Maikifi Petroleum da Ammas Oil & Gas Ltd.
Sai dai duk ƙoƙarin jin ta bakin gwamnatin jihar ya ci tura, yayin da Kwamishinan Watsa Labarai, Ibrahim Wayya da Sakataran Gwamna ba su ɗauki kiran waya ba, kuma Darakta Janar na Watsa Labarai na Gwamnan, Sunusi Bature ya yi bukaguro zuwa ƙasar waje.
Wannan dambarwar na zuwa ne bayan rahoton jaridar Nigerian Tribune a watan Yuli 2025, wanda ya bayyana cewa ICPC ta kammala bincike kan badaƙalar Naira biliyan 1.02 da ake zargin jami’an Hukumar Zaɓe ta Jihar Kano (KANSIEC).
A wata sanarwa da wasu ƙungiyoyin fararen hula 20 suka sa hannu, sun yi gargaɗi cewa zarge-zargen na iya ɓata amincewar jama’a da gwamnati, tare da sare gwiwar masu zuba jari daga ƙasashen waje da kuma durƙushewar da ci-gaban jihar.
“Wannan ba ƙaramin lamari ba ne. Ya nuna tsarin almundahana ta hanyar amfani da muƙaman gwamnati don amfanin kai,” in ji ƙungiyoyin.
Sun kuma buƙaci a dakatar da duk jami’an da ake zargi tare da gudanar da bincike mai zaman kansa kan dukkanin ma’aikatun gwamnati.
Haka kuma sun buƙaci Majalisar Dokokin Jihar Kano ta ƙarfafa aikin sa ido tare da kafa dokar kare waɗanda ke fallasa rashawa.
“Zaɓi yana a hannunmu: ko mu yaƙi rashawa mu dawo da martabar shugabanci ko kuma mu bari ta ƙara zurfi har ta kai ga rugujewar cibiyoyinmu da makomar ’ya’yanmu,” in ji sanarwar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa
Madagascar ta sanar da kafa sabuwar gwamnati wadda ta kunshi fitattun ‘yan adawa guda uku a manyan mukamai na ministoci.
An gabatar da majalisar ministoci mai mambobi 29, wacce ta kunshi mata 10, a wani biki da aka gudanar a Fadar Gwamnatin Yavoloha da ke babban birnin kasar, Antananarivo.
Shugaban rikon kwarya Michael Randrianireina ya bayyana a lokacin bikin cewa manyan abubuwan da sabuwar gwamnatin ta sa gaba sun hada da yaki da rashin adalci, aiwatar da matakan tsuke bakin aljihu, da kuma samar da yanayin kasuwanci mai dorewa.
Ya kara da cewa kowane minista dole ne ya samar da sakamako mai kyau cikin watanni biyu, yana mai gargadin cewa rashin yin hakan a cikin wannan lokacin zai zama gazawa kuma zai iya haifar da maye gurbin minister a nan take.
An nada Christine Razanahasoa, tsohuwar Ministar Shari’a kuma tsohuwar Kakakin Majalisar Dokoki ta Kasa, a matsayin Ministar Harkokin Waje, kuma an nada Fanerisoua Irinavo, tsohuwar alkali wacce ta dawo daga gudun hijira daga Faransa, a matsayin Ministar Shari’a.
An nada Hanitra Razavimanantsoa, ’yar majalisa daga jam’iyyar Tiaco Madagascar karkashin jagorancin tsohon shugaban kasar Marc Ravalomanana, a matsayin Ministar Kasa a ma’aikatar Sake Gina Kasa. Waɗannan mutane uku suna wakiltar muryoyin manyan bangarorin ‘yan adawa a Madagascar.
Jagoran juyin mulkin, Michel Randrianireina, ya kwace mulki a ranar 14 ga Oktoba bayan tsohon shugaban kasar Andry Rajoelina ya tsere daga kasar a cikin jirgin saman sojojin Faransa bayan makonni na zanga-zanga.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya October 30, 2025 Isra’ila ta amince da fadada matsugunai a Yammacin Kogin Jordan October 30, 2025 Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu October 30, 2025 Sudan : Kasashen duniya na tir da cin zarafi a El-Fasher October 30, 2025 Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin October 30, 2025 Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher October 30, 2025 An Kafa Dokar Ta Baci A Darul-Salam Saboda Tarzoman Zaben Shugaban Kasa A Tanzania October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci