Taron PDP: Akwai yiwuwar NEC ta yanke hukunci kan Wike da Ortom
Published: 25th, August 2025 GMT
A yau ne babbar jam’iyyar adawa ta PDP za ta gudanar da zama na 102 na Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC), inda ake sa ran ta yanke hukunci kan wasu jiga-jiganta da ake zargi da cin dunduniyarta, ciki har da Ministan Abuja Nyesom Wike da tsohon Gwamnan Jihar Binuwai, Samuel Ortom.
Majiyoyi a jam’iyyar sun ce a yayin taron, za a gabatar da rahoton kwamitin ladabtarwa ƙarƙashin jagorancin Tom Ikimi, wanda ya ba da shawarar ɗaukar mataki a kan waɗanda ake zargi da yi wa jam’iyyar zangon ƙasa.
Har ila yau, taron zai tattauna shirin gudanar da babban taron jam’iyya na ƙasa a Ibadan a ranakun 15 da 16 ga watan Nuwamba, inda za a zaɓi sababbin shugabanni.
Kazalika rahoton Kwamitin Rabon Mukamai na daga cikin abubuwan da za a tattauna.
Mataimakin Jami’in Yaɗa Labarai na PDP na Ƙasa, Ibrahim Abdullahi, ya ce an kammala duk shirye-shirye, kuma taron zai gudana lafiya ba tare da wata rigima ba, yana mai cewa za a sake tabbatar da matsayar jam’iyyar kafin zaben 2027.
Dambarwar MikeSai dai saɓani ya ƙi ƙarewa a babbar jam’iyyar adawar, musamman kan matsayin Wike, wanda ke adawa da wurin taron, yana mai cewa dole ne jam’iyya ta fara amincewa da taron Kudu maso Kudu da masu goyon bayansa suka gudanar wanda NEC ta yi watsi da shi.
Wasu jiga-jigan PDP na zargin ministan da lalata jam’iyya, yayin da wasu ke ganin a bi a hankali don kada a ƙara rura rikici.
Shugabannin matasa da wasu shugabannin jihohi sun nuna goyon baya ga taron na Ibadan da tsarin rabon muƙamai, suna kira ga mambobi da su fifita haɗin kan Jam’iyyar.
Masana sun ce wannan zama na NEC zai taka muhimmiyar rawa wajen ganin ko PDP za ta tsira daga rikicin cikin gida kafin zaben 2027.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babban taro Jam iyyar PDP
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta dakatar da jam’iyyar PDP daga gudanar babban taronta na ƙasa da aka shirya yi a Ibadan, Babban Birnin Jihar Oyo, a watan gobe.
Mai shari’a James Omotosho ne, ya bayar da wannan umarni, yayin da yake yanke hukunci kan wata ƙara da aka shigar domin sanin ko jam’iyyar PDP na da ikon ci gaba da shirya taron da aka tsara gudanarwa a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba.
Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4mWaɗanda suka shigar da ƙarar sun haɗa da Austine Nwachukwu, shugaban PDP na Jihar Imo; Amah Abraham Nnanna, shugaban PDP na Jihar Abiya da Turnah George, sakataren PDP na yankin Kudu maso Kudu.
Waɗanda ake ƙarar sun haɗa da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), PDP, Sakataren Jam’iyyar na Ƙasa, Samuel Anyanwu, Sakataren shirya taruka na jam’iyyar, Umar Bature, Kwamitin Ayyuka na jam’iyyar na Ƙasa (NWC) da Kwamitin Zartarwa na jam’iyyar na Ƙasa (NEC).
Masu shigar da ƙarar sun kasance ’yan tsahin Nyesom Wike ne.
Sun roƙi kotu da ta hana gudanar da taron, inda suka bayyana cewar jam’iyyar ta saɓa wa dokokinta, Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999, da kuma Dokar Zaɓe wajen shirya taron.
Lauyansu ya shaida wa kotu cewa: “Ba a gudanar da taron wakilai a jihohi 14 ba don haka shirin taron ya saɓa wa doka.”
Sai dai PDP ta kare kanta, inda ta ce lamarin na harkokin cikin gidan jam’iyyar ne, don haka bai kamata kotu ta tsoma baki ba.
Jam’iyyar ta zargi masu ƙarar da ƙoƙarin tayar da rikici domin hana ta gudanar da sabon zaɓen shugabanni.
Aminiya ta ruwaito cewa wannan rikici ya ƙara dagula al’amura a jam’iyyar PDP.
Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, a baya ya yi zargin cewa an yi amfani da hannunsa na bogi a takardun da aka aike wa INEC game da shirya taron.
Amma shugabancin jam’iyyar ya ƙaryata wannan zargi.
A halin yanzu, Kwamitin Shirya Taron na Ƙasa (NCOC) ya ɗage tantance ’yan takara da aka tsara gudanarwa a ranar 28 ga watan Oktoba.
Mutane da dama na ganin ɗage tantance ’yan takarae na da nasaba da jiran sakamakon hukuncin kotu kafin a ci gaba da shirye-shirye.