Aminiya:
2025-07-31@02:47:38 GMT

Finafinan Kannywood da suke tashe da kuma manyan marubutansu

Published: 6th, April 2025 GMT

Wani nazarin finafinan Kannywood da BBC Hausa ta gabatar ya nuna cewa, Masana’antar Kannywood tana ta samun sauye-sauye, musamman a bangaren shirya fim da kasuwancinsa, inda daga CD aka koma sinima, yanzu aka koma YouTube, sannan ake ta hankoron shiga manhajojin duniya ka’in da na’in.

A wannan shekarar, kamar kowace shekara, masu shirya finafinan Kannywood sun taka muhimmiyar rawa wajen tsarawa da fitar da finafinai masu kyau, wadanda suka kayatar da masu kallo.

Yadda Kanawa suka huce takaicin rashin Hawan Sallah Mene ne matsayin azumin Sitta Shawwal a Mazhabar Malikiyya (2)

Tun bayan komawa dora finafinai a YouTube, yanzu za a iya cewa harkokin Kannywood sun fara komawa yadda suke a baya, bayan a baya masana’antar ta fara durkushewa.

Nazarin ya yi tankaɗe da rairaye, sannan ya zakulo wasu finafinai da suke tashe. Sai dai kusan finafinan duka masu dogon zango ne, wanda hakan ke nuna yadda masana’antar ta sauya da kuma hanyar da ta dosa domin dorewarta.

Da farko da aka fara finafinai masu zango, an yi tunanin kananan masu shirya fim ne kawai suka yi, su ɗora a YouTube, har ma wasu suke ganin ba su da inganci.

Amma yanzu an wayi gari manyan furodusoshin Kannywood sun shiga ana damawa da su.

Daga cikin finafinan da aka zakulo, akwai wadanda an dade da fara yin su, amma har yanzu suna jan hankalin mutane. Ga yadda jerin finafinan ya kasance:

Labarina

Labarina fim ne mai dogon zango na fitaccen darakta, Malam Aminu Saira, wanda sunansa ya riga ya yi amo, ta yadda ba ya bukatar gabatarwa ga dukkan masu kallon finafinan Hausa.

Fim ne mai tsari shigen labarin ‘Dare dubu da daya’, inda daga wannan labarin za a shiga wani labarin daban, wanda a cewar daraktan, hakan zai sa fim din ya dade ba tare da ya salance ba saboda ba labari daya ba ne.

A shekarar 2020 aka fara fim din da labarin Sumayya wato Nafisa Abdullahi, wadda daga baya ta rikide ta koma Fati Washa, inda a karshen zango na bakwai aka dakata da labarin Sumayya, aka tafi hutu.

Amma yanzu labarin ya koma na Alhaji Mainasara wato Sadik Sani Sadik, wanda aka fara daga zango na takwas, kuma yanzu haka ana zango na 11.

Labari ne kan yadda Alhaji Mainasara ya batar da kama, ya fito a matsayin talaka domin samun soyayya ta gaskiya bayan wahalar da ya sha a farko, inda ya hadu da Jamila wato Amina Uba Hassan, ya nuna mata kauna.

Daga bisani ya tura mata direbansa da sunan yana da arziki, ita kuma ta amince da shi, maimakon Mainasara.

Ana cikin haka ita kuma kawarta, Maryam wato Fatima Hussaini ta amince za ta aure shi a haka.

Bayan aure komai ya fito fili. Amma daga baya matsala ta sa Maryam ba za ta haihu da shi ba, ta sa shi auren Dakta Asiya wato Diamond Zahra.

Fim din ya fitar da jarumai mata wadanda yanzu ake yi da su a masana’antar irin su Firdausi Yahaya da Fatima Hussaini da Amina Uba Hassan da sauransu.

Yawancin fitowar fim makomako na samu masu kallo sama da miliyan 1.

Manyan Mata

Fim din Manyan Mata shi ma ba a shekarar 2024 aka fara ba, amma yana ci gaba da jan masu kallo.

Fim ne da ya tara manyan jarumai masu yawan gaske, wanda za a iya cewa ba a saba ganin hakan ba.

Furodusa Abdul Amart Maikwashewa ne ya shirya, kuma ya dauki nauyi, sannan Sadik N. Mafia ya fara bayar da umarni, daga baya Ali Gumzak ya ci gaba.

A fim din an nuna yadda wasu mata suke shan wahala a gidajen miji da ’yan gudun hijira da sauran mata talakawa da yadda wasu suke amfani da damar da suke da ita wajen cin zarafinsu.

Sannan a gefe guda kuma, akwai mata biyu wato Laila (Hadiza Gabon) da Nadiya wato Aisha Tsamiya, wadda aka maye da Rabiatu Kafur da suke kokarin kwato ’yancin mata da kungiyarsu ta ‘Manyan Mata’, tare da kokarin nuna amfanin ilimin ’ya’ya mata.

Yanzu dai kallo ya koma sama, bayan rikici ya barke a tsakaninsu. Kusan duk wani babban jarumi a Kannywood yana cikin fim din, har da waɗanda aka daɗe ba a ji duriyarsu ba.

Yawancin fitowar fim ɗin a mako-mako yana samun masu kallo kusan 500,000.

Gidan Sarauta

Gidan Sarauta na cikin finafinai masu dogon zango na furodusa Abubakar Bashir Maishadda, wanda yake jan hankalin masu kallo.

An fara fitar da fim din ne a ranar 5 Nuwamban 2023 kuma jarumi Umar M. Shareef da jaruma Mommee Gombe ne suke jan fim din tare da taimakon Garzali Miko da Aisha Najamu.

Ali Nuhu da Hadizan Saima da Yakubu Mohammad da Rabiu Rikadawa da Abale duk suna cikin fim din.

An gina fim din ne a kan Umar M. Shareef, wanda ya fito a yarima mai jiran gado, ya fada soyayya da ‘yar talaka, Bintu (Momme Gombe), amma bai bayyana ba, daga kaninsa ya riga shi aurenta.

Amma sai aka gane akwai wani abu a tsakaninsu, wanda hakan ya sa kanin ya sake ta, shi kuma ya aura.

Wannan ya sa aka yi fushi da shi, aka ba shi zabin ko dai Bintu ko sarauta, inda ya zabi matarsa, ya hakura da sarautar.

Daga bisani shi ma Garzali ya hango yarinyar Tafida, wato Badariyya (Firdausi Yahaya), inda ya fada kogin kauna, amma yana tsoron shiga halin da yayansa yake ciki.

Ali Nuhu ne ya ba da umarnin a fim din, wanda dukkan jaruman suka dage wajen fitar da labarin fes.

Garwashi

Garwashi fim ne da aka fara fitarwa a ranar 12 ga watan Agustan 2024 a YouTube. An shirya fim ɗin ne a kan ƙalubalen da matan da mazajansu suka rasu suke fuskanta daga wurin ’yan’uwa da mutanen gari.

Jarumar shirin, Asma’u wato Firdausi Yahaya tana shan fama daga dangin mijinta da ’yan’uwanta da ma wuraren da take aiki.

Fitacciyar marubuciya Fauziyya D. Suleiman ce ta tsara labarin, sannan fitaccen darakta Yaseen Auwal ya ba da umarni.

Fim din ya dauki hankalin masu kallo sosai cikin kankanin lokaci, musamman ganin yadda jarumar take shan wahala.

Allura Cikin Ruwa

Fim ne da aka shirya kan Na’ima wato Rukky Ali, wadda marainiya ce, da aka tsinta bayan an harbe mahaifiyarta.

Daga baya maza irin su Maina wato Yakubu Mohammad, wanda take wa kallon kanin mahaifi da Alhaji Hadi wato Sani Danja da Dakta Hashim wato Adam A. Zango da Sadik wato Isa Ferozhkan, wanda suka daɗe suna soyayya, duk suka nuna sha’awar aurenta.

Daga baya an gano ashe tana da tarin dukiya da aka rasu aka bar mata. Saboda soyayyarta ce Maina ya fallasa cewa, Tijjani Faraga ba mahaifinta ba ne, don haka ya ce babu laifi don ya aure ta.

Kamfanin 2Effects ne ya ɗauki nauyin shirin, sannan Yakubu Mohammed ne ya ba da umarni.

Fitattun marubutan finafinan Kannywood da suke tashe

A harkar finafinan Hausa na Masana’anatr Kannywood, an fi mayar da hankali kan ‘yan fim din da suke fitowa, musamman ma wadanda suke jagorantar finafinan, inda akan manta da wadanda suke bayan fage.

A harkar, akwai masu ruwa da tsaki da dama da suke bayar da gudunmuwa wajen daukar fim, tun daga marubuta da masu fitilla da masu sauti da masu daukar bidiyo da tsara dandali da zirgazirga da sauransu.

A cikin wadanda suke aiki a bayan fage, an fi sanin furodusa da darakta, amma ba a cika ambaton sunan marubuta ba, wadanda kuma alkaliminsu ne yake saita fim, sannan idan ya samu aiki mai kyau, masu kallo su yaba.

Wannan ya sa muka rairayo wasu marubuta da alkalumansu suka rubuta finafinai wadanda suka yi shuhura, duk da cewa akwai zaratan marubuta da a ’yan kwanakin nan ba su yi wani aiki babba ba.

Yakubu M. Kumo

Yakubu M. Kumo, marubuci ne wanda a yanzu alkaminsa ke tashe a rubuce-rubucen finafinan Masana’antar Kannywood.

Daga cikin fitattun finafinan da ya rubuta akwai Labarina da Manyan Mata da Jamilun Jiddan da Gidan Sarauta da sauransu.

Ya dade yana rubuta finafinai masu inganci wadanda mutane suka yaba.

Fauziyya D. Suleiman

Fauziyya marubuciya ce da ta dade tana rubuta fitattun finafinai masu kayatarwa, tun daga kananan har zuwa masu dogon zango.

Daga cikin fitattun finafinan da ta rubuta akwai Dadin Kowa da take cikin marubutan fim din, wanda zuwa yanzu an kai shekara 10 ana yi.

A cikin finafinan da ta rubuta suke tashe, sun hada da fim din da yake tashe a yanzu wato Garwashi, kuma tana cikin masu shiryawa.

Mujahid Koguna

Mujahid Koguna da Yakubu Mohammad ne suka hadu wajen rubuta fim din Allura cikin ruwa na 2Effects kuma ya rubuta fim din Fansa.

Abdulkarim Papalaje

Abdulkarim Papalaje yana cikin sanannun marubuta kuma tsohon marubucin finafinan Hausa ne mai basira da yarubuta finafinai da dama da suka hada da Adamsy da Madubin Dubawa duka na Ali Nuhu da Ni da Matata da Oga Abuja da sauransu.

Nazir Adam Salihi

Nazir Adam Salihi shi ma sanannen marubuci ne da ya rubuta Gidan Badamasi.

Wasu marubutan da suka shahara sun hada da Jamil Nafseen da Nabila Rabi’u Zango da ya rubuta fim ɗin Umarni na furodusa Nazir Ɗanhajiya, waɗanda ana yabawa da su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Allura cikin ruwa Fauziyya D Suleiman Garwashi Labarina Manyan Mata finafinan Kannywood da sauransu Manyan Mata

এছাড়াও পড়ুন:

Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan Almujtaba 121

121- Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da haka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshin da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Murtadha Muttahhari, ko kuma cikin littafin mathnawa na maulana Jalaluddeen Rum ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu.

////… Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata a kuma cikin sarir Imam Al-Hassan Almujtaba (a) diyar Fatima (s) kuma jikan manzon All..(s) na farko , mun tsaya inda muka bayyana yadda Talha da Zubair suka nemi izinin Amirulmuminina (a) na zuwa umra, amma ya basu izini duk da cewa ya san ba umra zasu je ba, sai dai ya bukacesu sun yi ranstuwa su kuma sake yi masa bai’a kafin su fita. Sun yi hakan amma kuma, kamar yadda ake zata suna neman hanyar yi masa tawaye ne, don abinda suka yi Kenan bayan da suka fita madina.

Sannan mun yi maganar ummilmuminina Aisha matar manzon All..(s), wacce ta je aikin hajji a shekarar, ta bar madina a lokacinda yan tawaye suka yiwa gidan Khalifa kawanya. Don haka da ta kare aikin hajji ta kama hanyar zuwa madina, amma da ta isa wani wuri a wajen Makka ta ji labarin cewa Aliyu dan Abitalib (a) shi ne aka yiwa Bai’a. Sai ta yi bakin ciki, sannan a lokaci guda tace sai ta nemi jinin Khalifa Uthman daga Imam Ali (a). mun yadda ta kawo hujjojinta na yin haka, amma gaba daya sun sabawa hankali sun sabawa shari’a, wanda zai sa ta yake shi.

Mun yi magana kan yadda take rayuwa da manzon All..(s) tana ginin yadda yake gairma iyalan gidansa gudu hudu Aliyu da Fatimah da kuma yayansu alhassan da Al-hussain(a).

Tana son manzun All..(s) ya sota kamar yadda yake son wadannan mutane 4 amma bata samu ba, sai ta fara hasada da su. Duk tare da matsayinsu a wajen All.. da ta sha ji a wajen manzon All..(s).

Don haka kiyayyar ne ya sa ta ce dage sai ta yake shi duk da cewa mata da hujjar yan hakan. Munji yadda malamai da dama suka kawo hujjojin da suka sa ta yake shi.

Daga karshe mung a cewa a sharia ma, idan an kashe wani mutum, danginsa ne , musamman yayansa ne suke da hakkin neman jininsa daga wadanda suka kashe shi. Idan har babu su, to shugaban muminai wanda shi ne Aliyu, dan Abitali (a).

Sannan mun fara bayyana cewa matan manzon All..(s) dangane da yakar da Aisha ta yiwa Aliyu dan Abitalib (a) sun rarraba, wasunsu suna tare da Aliyu dan Abitalib (a), kuma Ummu salma ce take jagorantarsu, wasu kuma karkashin Aisha suna goyon bayan yakarsa.

Mun bayyana cewa Aisha bata fito yaki da Aliyu dan Abutalib don neman jinin Khalifa Uthman ba, sai dai ta fake da neman jinin Uthman en don yakarsa da kuma fidda khalifanci daga hannunsa.

Ummil muminina Aish ce ta fara shelanta yaki a kan gwamnatin Amirul muminina (a) a makka, a lokacinda tayi doguwar akhuduba, tana bayyana abinda ya faru da kuma yadda aka kashe Khalifa Uthman. A cikin khudubarta ta tabbatar da cewa Khalifa Uthman yayi kura kurai, sannan manya manyan sahabban manzon All..sun aibata shi.

Kafin mu je, gama, yakamata mu sani daga cikin wadanta suka aibata shi har da ita Aisha ummil muminina, har an jita da dama tana fada, ku kashe Nathaly a kafirta, tana nufin Uthma,  sannan ta yi maganar cewa an bukace shi ya tuba. Wannan gaskiya ce, amma malaman tarihi sun bayyana cewa, bayan ya tuba, yan tawaye daga kasar masar sun kama hanya, sai ya zo cikin masala ci ya ce bai tuba ba zai ci gaba da abinda yake kai. Sai labara ya kaiwa yan tawaye, suka sake dawowa sannan suka ce ya sauka kawai daga kan kujerar khalifanci, ya ce ba zai sauka ba, ba abinda ya rage masu sai yakarsa da kuma kashe shi.

Amma batun cewa, ya tuba sannan suka kashe shi ba haka bane. Ya tuba ne sannan ya kwance tubarsa. A nan ne suka bashi zabi ko ya sauka ko su kashe shi. Sai ya zabi na biyun. Sannan kisansu bai da alaka da Amirulmuminina, (a), gaskiya ne ya yi masa nisaha ya kuma aibata shi kamar yadda sauran sahabban suka yi, amma ba wana ya taba jinshi yana cewa ku kashe uthman.

Wannan duk yana faruwa ne a makka, bayan aikin hajji, inda matan manzon All..(s) da dama suka fito zuwa aikin hajji na wancan shekara , shekara ta 35 bayan hijiran manzon All..(s).

Don haka bayan khudubarta a cikin jama’a , Aisha ta kira sauran matan manzon All..(s) zuwa yakar wasiyyin manzon All..(s) wato Aliyu dan Abitalib (a), kofar ilminsa, baban jikokin manzon All..(s) Al-Hassan da Alhussain.

Don haka ta hadu da ummu salma ® tana kiranta zuwa yakar Aliyu (a) tana cewa: ya ke yar abu Umayya, ke ce farkon wadanda suka yi hijira daga cikin matan manzon All..(s) kuma, kece babban a cikin iyayen muminai, manzon All..(s) yana raba mana a dakinki, sannan mala’ika jibrilu ya fi sauka a dakin ki. …

Sai umma salma ta cewa, mata, na rantse da All..menene kike bukata da dukkan wadannan maganganun? Sai Aisha ta fito fila ta fada mata abinda take so, sai tace: Mutanen nan sun bukaci Uthman ya tuba, a lokacinda ya tuba sai suka kasheshi yana azumi, a cikin wata mai alfarma (zulhajji). Na yi niyya zan fita zuwa Basra, sannan Talha da zubair suna tare da ni, ki fita tare da mu, mai yuwa All..ya kyautata wannan al-amarin a hannummu.

Daga nan sai Ummu Salma ta fara karyatata, da kuma yi mata nasiha da kuma shiryatar da ita, inda take cewa: Kin kasance a jiya din na kina zuga mutane a kan Uthman, kina fadar mafi munin kalmomi a kansa, sunansa a wajenki shi Nathal, Sannan kin san matsayin Aliyu  dan Abitalib (a) a wajen manzon All..(a), ba zan yi maki nasiha ba?

Sai Aisha ta ce, ee.

Shin zaki tuna wata rana, ya zo (Aliyu) muna tare da shi (s), — har zuwa inda take cewa—sai ya kebe da Aliyu yana tattaunawa da shi, sun dade, sai kina son ki fada masu, sai nah ana ki,  sai kin saba mani, kika fada masu, ba’a dade ba sai kika dawo kina kukax, sai na ce maki, me ya same ki?  Sai kika ce na zo masu suna tattaunawa, sai na fadawa Aliyu(a), kwana guda ne kawai nake da shi a wajen manzon All..(a) a cikin ko wani kwanaki 9, shin ba zaka barni da kwanana ba ya dan Abiyalib ?.

Sai manzon All..(s) ya juya gareni fuskansa ta yi ja yana fushi, ki koma baya, na rantse da All..ba wanda za iyi da Aliyu sai wanda sai wanda bai da Imani. Sai na dawo ina nadawa.

Sai Aisha ta ce, ee na tuna!

Sai tace: in kara tunatar da ke?

Sai tace : ee!

Sai tace: wata rana ina zaune ni da ke tare da manzon All…(a) sai yace mana: Wacece daga cikinku, wacce zata hau wata rakuma mai yawan gashi, kuma karnukan Haw’aba zasu yi mata haushi, sai ta kasance ta karkata daga barin hanyar gaskiya?  

Sai muka ce gaba daya: muna neman tsarin All..da manzonsa da kasancewa haka. Sai ya taba bayanki sannan yake: ina gargadinki kada ki kasance, kice ya ke Humaira.

Sai Aisha tace na tuna.

Sai Ummu Salam ta kara cewa: in kara tunatar da ke?  Sai tace: ee.

Sai tace: wata rana ni da ke muna zaune tare da manzon All..(s) a wata tafiyarsa. Aliyu (a) ya kasance shi ne yake kula da takalman manzon All..(s) da kuma wanke kayansa, sai ya zo ya dauki takalman manzon All..(s) ya na gyaransa a karkashin inuwar itaciyar Samara.

Daga nan sai babanki ya zo tare da Umar sai suka nemi shiga wajensa, sai muka tashi muka je wajen Hijabi. Suka shiga suna yi Magana da shi kan abinda suka ga dama, sannan suka cewa masa: Ya manzon All..bamu san zuwa yauce ne zaka kasance tare da mu ba, da ka fada mana waye zaka Sanya khalifanka a bayanka don mu sanda zamu fake da shi a bayanka.

?

Sai yace masau: Amma ni ina ganinsa, da kuma na nuna maku shi da kun waste kun bar shi, kamar yadda banu Isra’ila suka watse suka bar Haruna dan Imrana., sai suka yi shiru. Sannan suka fita.

A lokacinda suka fita, sai muka fito zuwa wajen manzon All..(s). sai ke kika fara masa Magana, kika ce: Ya manzon All..(s) wa zaka Sanya khalifa a kansu  bayanka. Sai yace: wanda yake gyaran takalma. Sai duk muka fita waje sai muka ga Aliyu yana gyran takalma.

Sai kika ce ya manzon All..bamu ga wani ba sai Aliyu.? Sai ya ce: shi ne.

Sai tace na tuna.

Sai ummu salma tace: bayan wannan wani fitowa kuma zaki yi bayan wannan?

Sai Aisha tace: Ni ina fita ne don gyara a cikin mutane. Kuma ina fatan samun lada daga All.. Sai Ummu salma tace, ki tafi da ra’ayinki. 

Sai Ummu salma ta juya ta tafi ta kama hanyar Madina, sannan ta rubutawa Amirul muminina Aliyu dan Abitalib (a) wasika inda ta fada masa abinda Aisha take shirin aiwatarwa.

Wasu malaman tarihi sun bayyana cewa Ummu Salma (a) ta aiki danta Umar dan Abu salama danta daga mijinta na farko wato Abusalma, ta aike shi wajen Imam (a) tare da wasikar sannan ta fadawa Imam (a) kan cewa: Ga dana Umar wanda shi yake kula da ni, ya kasance cikin mataimakanka kan miyanka.  

Wannan ya faru ne bayan da ta gabatar da nasihohi kamar yadda ka ji. Amma Aisha ta yi gabanta, tana son yakar Amirul muminina (a).

Dana nan sai Aisha ta bada umurni a yi shela a cikin Makka kan cewa da ita da \zubai da Talha zasu fita daga Makka zuwa Basra, duk wanda yake son binta kuma bai da abin hawa da kuma guzuri za’a bashi.

Daga nan sai ta hau rakuminta, wanda ake kira Askar, banu Umayya da sauran masu kwadayin duniya, suna bayanta.  Haka ma tsofin gwamnonin Khalifa Uthman suna tare da ira suka kama hanyar Basra daga Makka.

Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu nay au sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu. Wassalamu alaikum.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  • Kissoshin Kayuwa: Sirar Imam Hassan(a) 122
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan Almujtaba 121
  •  Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Birnin Kiev Na Ukiraniya
  • Matsalar Lantarki: Ga tsada ga rashin wuta
  • Araqchi: Tattaunawar Nukiliya Wani Zabi Ne Mai Muhaimmanci Wanda Ya Karfafa Matsayin Iran A Duniya