Ya kuma buƙaci mambobin jam’iyyar da su ci gaba da haƙuri da fahimtar juna domin haɗa kai tare da tabbatar da goyon baya ga jam’iyyar.

A nasa ɓangaren, Sakataren APC na Zamfara, Hon. Ibrahim Umar Dangaladima, ya gode wa Shugaban Ƙasa Tinubu da Minista Matawalle bisa wannan tallafi.

Ya ce shinkafar ta zo a daidai lokacin da jama’a ke fuskantar wahalar rayuwa, kuma ya yi alƙawarin cewa ’yan jam’iyyar za su ci gaba da haɗa kai da kaunar juna.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Matawalle

এছাড়াও পড়ুন:

Wike: Za mu kare duk wani soja da ke aiki bisa doka — Ministan Tsaro

Ministan Tsaro, Mohammed Badaru, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya tare da shugabannin Rundunonin Sojin Najeriya, za su ci gaba da kare duk wani jami’i da ke gudanar da aikinsa bisa doka.

Badaru, ya bayyana hakan ne lokacin da yake ganawa da manema labarai a taron da aka shirya domin bikin tunawa da Sojojin Najeriya na shekarar 2026 a Abuja.

’Yan sanda sun kama mutum 14 kan zargin ta’amali da miyagun ƙwayoyi a Jigawa MDD ta sanya Najeriya cikin ƙasashe 16 da ke fama da tsananin yunwa

Wannan na zuwa ne bayan ce-ce-ku-cen da ya faru ranar Talata tsakanin Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, da wani jami’in rundunar sojan ruwa, Laftanar A. M. Yerima.

An yi taƙaddama ne kan wani fili da ke Abuja da ake zargin mallakar wani tsohon Shugaban Rundunar Sojin Ruwa, Vice Admiral Awwal Gambo (mai ritaya) ne.

“A Ma’aikatar Tsaro, da kuma rundunonin sojoji, za mu ci gaba da kare jami’anmu masu aiki bisa doka,” in ji Badaru.

“Muna binciken al’amarin da ya faru, kuma muna tabbatar da cewa duk wani jami’i da yake aikinsa yadda doka ta tanada za a kare shi. Ba za mu bari wani abu ya same shi ba matuƙar yana yin aikinsa da kyau.”

Ministan, ya kuma sanar da sabon shirin gwamnati na haɗa tsofaffin sojoji cikin aikin tsaron al’umma da ci gaban yankuna ta hanyar shirin “Reclaiming the Ungoverned Space for Economic Benefits Programme (RUSEB-P)”.

Ya ce manufar shirin ita ce amfani da ƙwarewar tsofaffin jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a yankunan da ake samun rikice-rikice.

Badaru, ya bayyana cewa shirin RUSEB-P zai taimaka wajen rage aukuwar ta’addanci da kuma bunƙasa harkokin noma, hakar ma’adinai, da sauran ayyukan tattalin arziƙi.

Ya ƙara da cewa an kafa kwamiti da ke aiki kan yadda za a aiwatar da shirin.

Haka kuma, ya bayyana cewa gwamnati na shirin sake duba ‘Nigerian Legion Act’ domin kafa Ƙungiyar Tsofaffin Sojojin Najeriya (Veterans Federation of Nigeria – VFN), wacce za ta ƙarfafa tsarin kariya da tallafa wa walwalar tsofaffin jami’an tsaro.

Ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da aiwatar da sauye-sauye da za su inganta tsaron ƙasa, inganta walwalar sojoji, da kuma girmama sadaukarwar tsofaffin jami’an tsaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 
  • Wike: Za mu kare duk wani soja da ke aiki bisa doka — Ministan Tsaro
  • ’Yan sanda sun kama mutum 14 kan zargin ta’amali da miyagun ƙwayoyi a Jigawa
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina
  • Gwamnatin Jihar Nasarawa Ta Shirya Faɗaɗa Gonakin Shinkafar Jangwa Don Ƙara Samar da Shinkafa
  • Kungiyar Wamban Shinkafi Ta Amince Da Tinubu a 2027
  • PDP ta sha alwashin gudanar da babban taronta duk da umarnin kotu
  • Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal
  • ’Yan bindiga sun kashe mai juna biyu da wasu mutum 4 a Sakkwato
  • Kogunan Hausa Ya Raba Kayan Solar Ga Al’umma A Kano