Gwamnati: Farashin Kayan Abinci Na Raguwa, Tattalin Arziki Na Ingantuwa
Published: 13th, March 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta ce ‘yan Najeriya sun fara samun sauki yayin da farashin kayan abinci ke raguwa da farashin fetur ke daidaita, kuma naira ke karɓar ƙarfi.
Da yake magana a taron manema labarai na ministoci karo na huɗu a Abuja, Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohamed Idris, ya ce ci gaban, suna nuna cewa gyare-gyaren tattalin arziki na Shugaba Bola Tinubu na yin tasiri.
Ya amince da wahalhalun da ‘yan Najeriya suka sha amma ya tabbatar da cewa hakan ya fara wucewa.
Mohamed Idris ya ce Gwamnatin Tarayya tana nan daram wajen daidaita tattalin arziki da inganta rayuwar al’umma.
A jawabinsa, Ministan Ilimi, Dr. Maruf Alausa, ya ce kudaden da aka ware za su karfafa ilimin fasaha da sana’o’i a kasan nan.
Ya bayyana cewa za a samar da dakunan gwaji a manyan makarantu shida na koyar da aikin likitanci domin inganta horo. “Muna mai da hankali kan horo a aikace, musamman a fannin sauya injunan mota zuwa na CNG, kula da hasken rana, da kuma noma na zamani domin samar da karin ayyukan yi.”
Haka nan, Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, ya ce yarjejeniyar hadin gwiwa tsakanin Emirates da Air Peace za ta karfafa harkokin jiragen saman cikin gida.
Gwamnati na kuma aiwatar da sabbin manufofi don tallafawa kamfanonin jiragen saman cikin gida 13, domin su ci gaba da yin gogayya a da ire iren su a duniya.
Keyamo ya tabbatar da cewa an inganta tashoshin jiragen Hajj don kyautata tsarin aikin hajji.
A halin yanzu, Jami’ar Kimiyya da Fasahar Jiragen Sama ta Afirka ta fara aiki gaba ɗaya, kuma Najeriya ta rattaba hannu kan yarjejeniya da Boeing domin inganta sayan jirage da matakan tsaro.
A fannin amincewar kasa da kasa, tashoshin jirgin saman Port Harcourt da Abuja sun samu matsayi mafi kyau a Afirka dangane da tsaron fasinjoji da shirin gaggawa, a cewar Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama ta Duniya (ACI) a Afirka ta Kudu.
Radio Nigeria/Adamu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Arziki Gwamnati Farashin Kayan Abinci Ingantuwa Raguwa
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Kakkabo Jiragen Yakin HKI Fiye Da 196 A Yakin Kwanaki 12
Gwamnatin kasar Iran ta bada sanarwan cewa ta kakkabo jiragen yakin HKI fiye da 196 a cikin yakin kwanaki 12 da aka dora mata a cikin watan Yunin da ya gabata. Daga ciki har da jiragen yaki samfurin Heron da Hermes -900 wadanda ke aiki da kayakin zamani.
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto wata tashar talabijin ta cikin gida tana fadar haka a yau Asabar ta kuma kara da cewa
Sashen garkuwar sararin samaniya na sojojin sama sun nuna hutunan lokacin da suke kakkabo jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa na HKI a lokacinda suka shigo sararin samaniyar kasar kafin su kai ga bararsu.
Burgediya Janar Reza Khajeh mataimakin kwamandan garkuwar sararin samaniya na sojojin kasar Iran yace sun kakkabu fiye da jiragen yaki 196 a cikin yakin.
Khajeh ya kara da cewa nan gaba kadan zamu kaddamar da garkuwan sararin samaniya na kasar wanda zai kakkabo jiragen yake samfurin jet mafi inganci a wajen makiya daga sararin samaniyar kasar.
Yakin kwanaki 12 dai ya zama kamar gwaji ne ga ingancin makamai da kuma garkuwan sararin samania na kasar Iran.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Trump Ya Bada Sanarwan Rufe Sararin Samaniyar Kasar Venezuela Gaba Daya November 29, 2025 Kamfanin Kera Jiragen Sama Na Airbus Ya Bukaci A Dawo Da Jiragen Sama Samfrin A320 Saboda Gyara November 29, 2025 An Kammala Gasar ‘Rayan’ Na AI Ta Kasa Da Kasa A Nan Tehran November 29, 2025 Iran da Kasashen Larabawa Sun Yi Allah wadai da kutsen sojojin Isra’ila a Kudancin Siriya November 29, 2025 MDD ta yi kira da a gudanar da cikakken bincike kan kisan gillar da aka yi wa Falasdinawa November 29, 2025 Lebanon ta shigar da kara ga Kwamitin Tsaro bayan Isra’ila ta Gina katanga a Yankinta November 29, 2025 AU ta dakatar da Guinea-Bissau daga zama mamba a cikinta bayan juyin mulkin sojoji November 29, 2025 Najeriya : An yi jana’izar Sheikh Dahiru Usman Bauchi November 29, 2025 Larijani: Da’awar lalata karfin nukiliyar Iran wauta ce November 29, 2025 Babban banki Najeriya Ya Tura Dala Miliyan 50 Don Ƙarfafa Kasuwar Musayar Kudade November 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci