Gwamnatin Tarayya ta ce ‘yan Najeriya sun fara samun sauki yayin da farashin kayan abinci ke raguwa da farashin fetur ke daidaita, kuma naira ke karɓar ƙarfi.

 

Da yake magana a taron manema labarai na ministoci karo na huɗu a Abuja, Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohamed Idris, ya ce ci gaban, suna nuna cewa gyare-gyaren tattalin arziki na Shugaba Bola Tinubu na yin tasiri.

 

Ya amince da wahalhalun da ‘yan Najeriya suka sha amma ya tabbatar da cewa hakan ya fara wucewa.

 

Mohamed Idris ya ce Gwamnatin Tarayya tana nan daram wajen daidaita tattalin arziki da inganta rayuwar al’umma.

 

A jawabinsa, Ministan Ilimi, Dr. Maruf Alausa, ya ce kudaden da aka ware za su karfafa ilimin fasaha da sana’o’i a kasan nan.

 

Ya bayyana cewa za a samar da dakunan gwaji a manyan makarantu shida na koyar da aikin likitanci domin inganta horo. “Muna mai da hankali kan horo a aikace, musamman a fannin sauya injunan mota zuwa na CNG, kula da hasken rana, da kuma noma na zamani domin samar da karin ayyukan yi.”

 

Haka nan, Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, ya ce yarjejeniyar hadin gwiwa tsakanin Emirates da Air Peace za ta karfafa harkokin jiragen saman cikin gida.

 

Gwamnati na kuma aiwatar da sabbin manufofi don tallafawa kamfanonin jiragen saman cikin gida 13, domin su ci gaba da yin gogayya a da ire iren su a duniya.

 

Keyamo ya tabbatar da cewa an inganta tashoshin jiragen Hajj don kyautata tsarin aikin hajji.

 

A halin yanzu, Jami’ar Kimiyya da Fasahar Jiragen Sama ta Afirka ta fara aiki gaba ɗaya, kuma Najeriya ta rattaba hannu kan yarjejeniya da Boeing domin inganta sayan jirage da matakan tsaro.

 

A fannin amincewar kasa da kasa, tashoshin jirgin saman Port Harcourt da Abuja sun samu matsayi mafi kyau a Afirka dangane da tsaron fasinjoji da shirin gaggawa, a cewar Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama ta Duniya (ACI) a Afirka ta Kudu.

 

Radio Nigeria/Adamu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Arziki Gwamnati Farashin Kayan Abinci Ingantuwa Raguwa

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya za ta buga wasan sada zumunta da Masar kafin fara gasar AFCON ta 2025

Tawagar Super Eagles ta Najeriya za ta buga wasan sada zumunta da ƙasar Masar kafin fara gasar Kofin Afrika da za a yi a Maroko.

Wasan zai gudana ne a ranar 11 ga wata. Disamba, da misalin ƙarfe 7 na dare, a filin wasa na Cairo da ke Masar.

EFCC ta tsare Malami kan binciken kuɗaɗen Abacha Real Madrid  za ta ɓarje gumi da Manchester City a Santiago

Za a yi wasan ne kwana shida kafin a fara gasar da ƙasashe 24 za su fafata a cikinta.

Najeriya za ta fara wasanta na farko a ranar 23 ga watan Disamba da Tanzania.

Ita kuwa Masar za ta buga wasanta na farko da Zimbabwe a ranar 22 ga watan Disamba.

A tarihi, Masar ce tafi lashe Kofin Afrika inda ta lashe gasar sau bakwai, yayin da Najeriya ta lashe sau uku.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”
  • Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa
  • Shugabannin Sin Sun Yi Taron Koli Na Tattauna Aikin Raya Tattalin Arziki Don Tsara Abubuwan Da Za A Aiwatar A 2026
  • ‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’
  • Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu  
  • NAJERIYA A YAU: Alfanu Da Kalubalen Sabon Jadawalin Karatun Makarantu Da Gwamnati Ta Bijiro Dashi
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC
  • Najeriya za ta buga wasan sada zumunta da Masar kafin fara gasar AFCON ta 2025