Babban Rajistara na Sashen kula da lafiyar Koda a Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Gombe (FTHG), Dr. Fidelis Linga, ya yi kira ga jama’a da su kula da lafiyarsu domin kaucewa kamuwa da cututtukan koda.

Ya bayyana hakan ga manema labarai a Gombe yayin bikin Ranar Koda ta Duniya.

Dr. Fidelis Linga ya jaddada cewa wasu munanan dabi’u kamar shan barasa, da taba, da cin abinci mara kyau, da zama babu motsa jiki na daga cikin dalilan da ke haddasa karuwar cututtukan da suka shafi Koda.

Ya yi nuni da mahimmancin yin gwaje-gwaje a asibiti akai-akai, da cin abinci mai kyau, da  motsa jiki domin hana cutar koda.

Ya bayyana cewa, a duniya gaba ɗaya, mutane miliyan 850 na fama da cututtukan Koda, kuma daga cikinsu, mutane miliyan 11 ke mutuwa kowace shekara. Ya bayyana wannan matsala a matsayin abin damuwa.

Dr. Fidelis Linga ya ce Asibitin FTH Gombe na kokarin samar da karin na’urorin wanke koda da kuma ƙarin ma’aikatan lafiya domin kula da yawan marasa lafiya da ke zuwa asibitin don wanke Koda.

Ya ce wannan yunƙuri na da nufin inganta samun damar wanke Koda ga marasa lafiya da ke fama da cututtukan koda.

HUDU SHEHU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Cutar Koda

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Cutar kansar mama na ɗaya daga cikin manyan cututtukan da ke addabar mata a Najeriya da ma duniya baki ɗaya.

 

An kiyasta cewa mata sama da dubu ɗari biyu na kamuwa da cutar a kowace shekara a Najeriya, yayin da miliyoyin mata a duniya ke fama da wannan cuta. Abin damuwa shi ne cewa yawancin lokuta ana gano cutar ne a kurarren lokaci, wanda hakan ke sa magani ya yi wahala kuma ya rage yiwuwar ceto rayuwar wanda ya kamu da shi.

NAJERIYA A YAU: Halayen Da Ambasadoji Ya Kamata Su Mallaka Kafin Tura Su Wasu Kasashe DAGA LARABA: Shin Ya Kamata A Biya Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane?

Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi
  • Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100%
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a
  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
  • Shugaban venuzuwela Ya Gargadi Amurka Game Da Kokarin Da Take yi Na Karbe Ikon Kula Da Rijiyoyin Mai Na Kasar
  • Hizbullah Ta Bukaci Shugaban Cocin Katolika Na Duniya Yayi Tir Da Hare-haren Isra’ila
  • MDD Ta Bukaci Isra’ila Da ta Kawo Karshen Mamayar Da Tayi wa Yankunan Falasdinawa
  • Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo
  • Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe