Babban Rajistara na Sashen kula da lafiyar Koda a Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Gombe (FTHG), Dr. Fidelis Linga, ya yi kira ga jama’a da su kula da lafiyarsu domin kaucewa kamuwa da cututtukan koda.

Ya bayyana hakan ga manema labarai a Gombe yayin bikin Ranar Koda ta Duniya.

Dr. Fidelis Linga ya jaddada cewa wasu munanan dabi’u kamar shan barasa, da taba, da cin abinci mara kyau, da zama babu motsa jiki na daga cikin dalilan da ke haddasa karuwar cututtukan da suka shafi Koda.

Ya yi nuni da mahimmancin yin gwaje-gwaje a asibiti akai-akai, da cin abinci mai kyau, da  motsa jiki domin hana cutar koda.

Ya bayyana cewa, a duniya gaba ɗaya, mutane miliyan 850 na fama da cututtukan Koda, kuma daga cikinsu, mutane miliyan 11 ke mutuwa kowace shekara. Ya bayyana wannan matsala a matsayin abin damuwa.

Dr. Fidelis Linga ya ce Asibitin FTH Gombe na kokarin samar da karin na’urorin wanke koda da kuma ƙarin ma’aikatan lafiya domin kula da yawan marasa lafiya da ke zuwa asibitin don wanke Koda.

Ya ce wannan yunƙuri na da nufin inganta samun damar wanke Koda ga marasa lafiya da ke fama da cututtukan koda.

HUDU SHEHU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Cutar Koda

এছাড়াও পড়ুন:

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

Ya ƙara da cewa yana cikin farin ciki ganin yadda Gwamna Douye Diri ya fice  daga jam’iyyar, inda ya ce, “Shi da Makinde sun taɓa cewa ba za su bari a lalata PDP ba ko a jawo ta ƙasa, amma ga su yanzu; su ne suka faɗi ƙasa.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi  November 4, 2025 Manyan Labarai Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja  November 4, 2025 Manyan Labarai Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo November 4, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamitin Tsaron Ya Ce: Amurka Ta Bukaci Duba Kudurin Neman Kafa Rundunar Kasa Da Kasa A Gaza
  • Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir
  • Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano
  • Likitoci sun wayar da kan mata kan cutar Sankara a Gombe
  • Matan 500 Za Su Amfana da Gwajin Cutuka Kyauta a Jihar Gombe
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Farmaki Ga Wani Dan Majalisa A Jihar Niger
  • Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike
  • Karuwanci da zubar da cikin ’yan mata ’yan gudun hijira ya karu a Maiduguri
  • Uba Sani Ya Kaddamar Da Gidaje 100 Ga Waɗanda Rikici Ya Shafa A Jihar