An Bukaci Jama’a Su Rika Binciken Lafiyarsu Don Kare Kai Daga Cutar Koda
Published: 13th, March 2025 GMT
Babban Rajistara na Sashen kula da lafiyar Koda a Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Gombe (FTHG), Dr. Fidelis Linga, ya yi kira ga jama’a da su kula da lafiyarsu domin kaucewa kamuwa da cututtukan koda.
Ya bayyana hakan ga manema labarai a Gombe yayin bikin Ranar Koda ta Duniya.
Dr. Fidelis Linga ya jaddada cewa wasu munanan dabi’u kamar shan barasa, da taba, da cin abinci mara kyau, da zama babu motsa jiki na daga cikin dalilan da ke haddasa karuwar cututtukan da suka shafi Koda.
Ya yi nuni da mahimmancin yin gwaje-gwaje a asibiti akai-akai, da cin abinci mai kyau, da motsa jiki domin hana cutar koda.
Ya bayyana cewa, a duniya gaba ɗaya, mutane miliyan 850 na fama da cututtukan Koda, kuma daga cikinsu, mutane miliyan 11 ke mutuwa kowace shekara. Ya bayyana wannan matsala a matsayin abin damuwa.
Dr. Fidelis Linga ya ce Asibitin FTH Gombe na kokarin samar da karin na’urorin wanke koda da kuma ƙarin ma’aikatan lafiya domin kula da yawan marasa lafiya da ke zuwa asibitin don wanke Koda.
Ya ce wannan yunƙuri na da nufin inganta samun damar wanke Koda ga marasa lafiya da ke fama da cututtukan koda.
HUDU SHEHU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Cutar Koda
এছাড়াও পড়ুন:
Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Bayan an mika damar karbar bakuncin taron kungiyar APEC, kasashen duniya sun soma zura ido kan kasar Sin. Ana sa ran cewa, taron APEC da za a gudanar a Shenzhen, zai kara habaka hadin gwiwa, da samun ci gaba, da wadata tare a shiyyar, kana zai shaida yadda kasar Sin ke kara samar da sabbin damammaki ga yankin Asiya da Pasifik, bisa ga sabbin nasarorin da take samu ta hanyar zamanantarwa irin ta kasar Sin. (Mai fassara Bilkisu Xin)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA