An Bukaci Jama’a Su Rika Binciken Lafiyarsu Don Kare Kai Daga Cutar Koda
Published: 13th, March 2025 GMT
Babban Rajistara na Sashen kula da lafiyar Koda a Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Gombe (FTHG), Dr. Fidelis Linga, ya yi kira ga jama’a da su kula da lafiyarsu domin kaucewa kamuwa da cututtukan koda.
Ya bayyana hakan ga manema labarai a Gombe yayin bikin Ranar Koda ta Duniya.
Dr. Fidelis Linga ya jaddada cewa wasu munanan dabi’u kamar shan barasa, da taba, da cin abinci mara kyau, da zama babu motsa jiki na daga cikin dalilan da ke haddasa karuwar cututtukan da suka shafi Koda.
Ya yi nuni da mahimmancin yin gwaje-gwaje a asibiti akai-akai, da cin abinci mai kyau, da motsa jiki domin hana cutar koda.
Ya bayyana cewa, a duniya gaba ɗaya, mutane miliyan 850 na fama da cututtukan Koda, kuma daga cikinsu, mutane miliyan 11 ke mutuwa kowace shekara. Ya bayyana wannan matsala a matsayin abin damuwa.
Dr. Fidelis Linga ya ce Asibitin FTH Gombe na kokarin samar da karin na’urorin wanke koda da kuma ƙarin ma’aikatan lafiya domin kula da yawan marasa lafiya da ke zuwa asibitin don wanke Koda.
Ya ce wannan yunƙuri na da nufin inganta samun damar wanke Koda ga marasa lafiya da ke fama da cututtukan koda.
HUDU SHEHU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Cutar Koda
এছাড়াও পড়ুন:
Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko Da ‘Yan Ta’adda
Kwamandan sojan kasar Pakitsan Asim Munir ya ce; Dole ne Taliban ta zabi wanda za ta yi mu’amala da hulda da su, ko dai gwamnatin Pakistan din, ko kuma ‘yan ta’adda.
Asim Munir wanda a makon da ya shude aka sake tabbatar da shi akan mukaminsa na shugaban sojojin kasar, ya kara da cewa sun isar da wannan sakon zuwa ga gwamnatin Taliban ta Afghanistan.
Haka nan kuma ya ce; Pakistan kasa ce mai son zaman lafiya,amma kuma a lokaci daya ba a shirye take ba, ta bari a tsokane ta akan abinda ta shafi zaman lafiya da kare hurumin kasarta.
A gefe daya, Asim Munir ya kuma gargadi makwabtansu na gabas, wato India yana mai cewa s fito daga cikin rudani, domin anan gaba idan wani abu ya faru, to martanin da Pakistan za ta mayar zai zama cikin sauri kuma da tsanani fiye da baya.
Ministan tsaron na Pakistan ya kuma ce, sojojin kasar sun sami gagarumin ci gaba wajen bunkasa ayyukansu, da kara zama cikin shiri, da kuma hanyoyin aiki tare a tsakanin dukkanin bangarorin tsaro.
A cikin watannin bayan nan dai an sami rashin jituwa a tsakanin kasashen Pakitsan da Afghanistan wanda ya kai ga musayar wuta na kwanani masu yawa. Kasashen Turkiya da Katar ne su ka shiga tsakani da ya kai ga tsagaita wutar yaki.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha December 9, 2025 An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa” December 9, 2025 Talauci Yana Karuwa A “Isra’ila” Bayan 7 Ga Watan Oktoba December 9, 2025 AU Ta yi Tir Da Harin RSF A Makarantar Kananan Yara Da Ya Kashe Mutane 80 December 8, 2025 MِِِِDD: Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya December 8, 2025 Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Matsaloli December 8, 2025 Iran Da Kasashen Afrika Sun Daura Dammarar Karfafa Alakar Kimiyya Tsakaninsu December 8, 2025 Ecowas Ta Tura Sojoji Zuwa Jamhuriyar Benin Don Dakile Juyin Mulki December 8, 2025 IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12 December 8, 2025 Najeriya: Gwamnatin Tarayya Ta Bada Sanarwan Kubutar Da Yan Makaranta 100 Da Aka Sace December 8, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci