Babban Rajistara na Sashen kula da lafiyar Koda a Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Gombe (FTHG), Dr. Fidelis Linga, ya yi kira ga jama’a da su kula da lafiyarsu domin kaucewa kamuwa da cututtukan koda.

Ya bayyana hakan ga manema labarai a Gombe yayin bikin Ranar Koda ta Duniya.

Dr. Fidelis Linga ya jaddada cewa wasu munanan dabi’u kamar shan barasa, da taba, da cin abinci mara kyau, da zama babu motsa jiki na daga cikin dalilan da ke haddasa karuwar cututtukan da suka shafi Koda.

Ya yi nuni da mahimmancin yin gwaje-gwaje a asibiti akai-akai, da cin abinci mai kyau, da  motsa jiki domin hana cutar koda.

Ya bayyana cewa, a duniya gaba ɗaya, mutane miliyan 850 na fama da cututtukan Koda, kuma daga cikinsu, mutane miliyan 11 ke mutuwa kowace shekara. Ya bayyana wannan matsala a matsayin abin damuwa.

Dr. Fidelis Linga ya ce Asibitin FTH Gombe na kokarin samar da karin na’urorin wanke koda da kuma ƙarin ma’aikatan lafiya domin kula da yawan marasa lafiya da ke zuwa asibitin don wanke Koda.

Ya ce wannan yunƙuri na da nufin inganta samun damar wanke Koda ga marasa lafiya da ke fama da cututtukan koda.

HUDU SHEHU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Cutar Koda

এছাড়াও পড়ুন:

An kama mutum 3 kan zargin sata da ƙone gidan bature a Gombe

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta kama wasu mutum uku da ake zargi da laifin sata da kuma ƙone gidan wani Bature a unguwar G.R.A, kusa da gidajen ’yan majalisa a jihar.

Waɗanda aka kama sun haɗa da Hannatu Ibrahim mai shekaru 28 daga Kumo, Ahmed Adamu mai shekaru 20, da Abubakar Ibrahim mai shekaru 28.

Mutum 2 sun rasu, wani ya ji rauni a hatsarin mota a Kano Majalisa ta amince da karatu na biyu kan ƙirƙirar sabbin Jihohi 4

A cewar kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, lamarin ya faru ne ranar 22 ga watan Maris, 2025 da misalin ƙarfe 8 na dare.

Sanarwar ta bayyana cewa Hannatu Ibrahim, wacce ke aiki a matsayin mai girki ga Mohammed Jurdi, wanda ɗan kasar Siriya da ke aiki da kamfanin Triacta Nigeria Limited, ta sace dala 35,000 (kimanin Naira miliyan 53.5) tare da banka wa gidan wuta.

Bayan samun rahoton, ‘yan sanda sun garzaya wajen, inda suka kama ta tare da gano dala 7,100 a wajenta.

A yayin bincike, ta ce Ahmed Adamu ne, mutum na farko da ta tuntuɓa bayan aikata laifin.

An samu dala 100 a cikin sakar hannunsu.

An kuma kama Abubakar Ibrahim, mai gadin gidan da aka yi satar, wanda ake zargi da taimaka musu wajen aikata laifin.

DSP Abdullahi, ya ce suna ci gaba da bincike, kuma suna shirin gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban kotu.

Ya kuma tabbatar wa jama’a cewa rundunar za ta ci gaba da yaƙi da laifuka tare da tabbatar da adalci a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cutar sanƙarau ta yi ajalin mutum 3 a Gombe
  • Kwara Ta Gargadi Jama’a Akan Gine-Gine Akan Bututun Ruwa
  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata a matsayin hutun sallaGwamnati Ta Ayyana 31 Ga Maris Da 1 Ga Afrilu A Matsayin Ranakun Hutu Don Bukin Eid-el-Fitr Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 31 ga Maris, da Talata, 1 ga Afrilu, a matsayin ranakun hu
  • An kama mutum 3 kan zargin sata da ƙone gidan bature a Gombe
  • Majalisa ta amince da karatu na biyu kan ƙirƙirar sabbin Jihohi 4
  • Yadda Binciken Kayan Tarihi Ke Zakulo Asalin Magabata Da Wayewar Kansu A Kasar Sin
  • Ministan tsaro ya yi alƙawarin kawo sauyi a cibiyar horar da sojoji
  • ‘Yan ta’adda Sun Kai Hari Sansanin Sojoji, Sun Kashe Uku A Borno
  • Za mu ɗauko hayar sojojin ƙetare domin horas da dakarun Nijeriya — Badaru
  • Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi