Peter Obi ya kusa dawowa APC — Hadimin Tinubu
Published: 13th, March 2025 GMT
Mai Bai Wa Shugaba Bola Tinubu Shawara Kan Harkokin Yaɗa Labarai, Daniel Bwala, ya ce akwai yiwuwar ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi, ya koma jam’iyyar APC mai mulki.
Bwala ya bayyana haka ne a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na TVC, inda ya ce babban aminin Obi, Valentine Ozigbo, ya koma jam’iyyar APC domin yin takarar gwamna.
“Kun san muna rage ƙarfin jam’iyyar LP kuwa?” in ji Bwala.
“Valentine Ozigbo ya shigo jam’iyyarmu, Balami ma haka, Peter Obi ma zai zo. Idan har Ozigbo ya shigo jam’iyyar – wanda ke da kusanci da Obi – to na tabbata Obi ma zai biyo bayansa.”
Sai dai Obi bai mayar da martani kan wannan iƙirari ba.
A baya, ya sha musanta jita-jitar cewa zai bar jam’iyyar Labour Party.
Kakakin jam’iyyar, Obiora Ifoh, ya yi watsi da wannan magana, inda ya bayyana cewar wasu ’yan siyasa ne ke ƙoƙarin lalata jam’iyyar.
“Abin mamaki ne ganin yadda wasu ke ƙoƙarin haddasa matsala tsakanin jam’iyyar da shugabanninta,” in ji Ifoh.
“Peter Obi ya sha nanata cewa zai yi Labour Party cikakkiyar biyayya saboda manufofinta a kan al’umma sun dace da burinsa. Ba zai taɓa komawa wata jam’iyyar da ke kare muradun attajirai ba.”
Wasu masana siyasa na ganin cewa Obi ba zai bar Labour Party ba, domin ya samu karɓuwa sosai tun bayan zaɓen 2023.
Wasu kuwa na ganin rikice-rikicen cikin gida a jam’iyyar na iya tilasta masa neman wata mafaka.
Yayin da zaɓen 2027 ke ƙaratowa, makomar Obi a siyasa na ci gaba da zama abin tattaunawa.
Ko zai ci gaba da kasancewa a Labour Party ko kuma zai yanke shawarar komawa wata jam’iyya, wannan mataki nasa zai taka muhimmiyar rawa a siyasar Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Daniel Bwala jam iyya Siyasa Labour Party a jam iyyar
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Duk wani harin wuce gona da iri kan Iran zai fuskanci mayar da martani daidai da shi cikin gaggawa
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya tabbatar da cewa Iran na da kwarin gwiwa kan iya dakile duk wani yunkuri da wasu bangarorin ke yi na kawo cikas ga manufofinta na ketare.
Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araqchi ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa: Rudun gwamnatin yahudawan sahayoniyya, wadda take ganin za ta iya gindaya wa Iran abin da ya kamata ko kuma bai kamata ba, rudun tunani ne da ya yi nesa da hakikanin gaskiya, ta yadda bai cancanci mayar da martani ba.
Araqchi ya kara da cewa: “Duk da haka, jajircewar Netanyahu wani abin lura ne, a yayin da yake kokarin neman bayyana wa Shugaba Trump abin da zai iya ko kuma ba zai iya yi a diflomasiyyarsa da Iran ba!”
Ministan harkokin wajen ya yi nuni da cewa: “Abokanan Netanyahu a cikin tawagar Biden da ta gaza – wadanda suka kitsa makarkashiyar hana cimma yarjejeniya da Iran – suna kokarin nuna zaman tattaunawar da ake yi ba na kai tsaye ba da gwamnatin Trump a matsayin wani kuskure ne kuma tamkar hoton sauran yarjejeniyar nukiliya ce da aka gudanar.”