Peter Obi na ganawar sirri da gwamnan Bauchi
Published: 13th, March 2025 GMT
Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, na ganawar sirri da Gwamna Bala Mohammed na Jihar Bauchi.
Taron na gudana ne a Ramat House da ke Bauchi, amma ba a bayyana manufarsa ba tukuna.
Da amincewar Buhari na fice daga jam’iyyar APC — El-Rufai ’Yan sanda sun hallaka hatsabibin ɗan bindiga a AbujaObi ya isa Filin Jirgin Sama na Abubakar Tafawa Balewa da misalin ƙarfe 10 na safiyar ranar Alhamis, inda Mataimakin Gwamnan Jihar Bauchi, Auwal Mohammed Jatau, ya tarbe shi.
Rahotanni sun nuna cewa Obi da Gwamna Mohammed za su yi magana da ’yan jarida bayan kammala ganawar tasu.
Wannan ganawa na faruwa ne a daidai lokacin da ’yan siyasa ke shirye-shiryen tunkarar zaɓen 2027.
Obi ya zo na uku a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, wanda tsohon gwamnan Jihar Legas, Bola Tinubu na jam’iyyar APC, ya lashe.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
An ceto mutane 3 da aka yi garkuwa da kama wasu a Bauchi
Rundunar ’yan sandan Jihar Bauchi ta ceto wasu mutane uku da aka yi garkuwa da su tare da kama wasu mutane shida da ake zargi da hannu wajen yin garkuwa da su a ƙauyen Euga da ke Ƙaramar hukumar Toro a jihar.
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, Ahmed Wakil ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da majiyar PUNCH Metro ta ruwaito ranar Laraba.
Majalisar Dattawa ta amince da Amupitan Shugaban INEC Za a kafa kamfanin ƙera kayan sola a KanoA cewar sanarwar, aikin ceton waɗanda aka kuɓutar ya biyo bayan kiran gaggawa da wani ɗan unguwar ya yi ga hukumar ne.
Wakil ya ce, “A ranar 29 ga Satumba, 2025 da misalin ƙarfe 12:01 na tsakar dare rundunar ’yan sandan Jihar Bauchi ta samu kiran gaggawa daga wani ɗan banga na unguwar, inda ya ba da rahoton harin da wasu da ba a san ko su wanene ba suka kai ga sace wasu maza uku daga ƙauyen Euga, a Ƙaramar hukumar Toro da suka haɗa da: Idi Umar da Idi Lawan da Musa Lawal.”
Ya ƙara da cewa, rundunar ’yan sandan ta yi gaggawar tattara jami’an rundunar ’yan sandan yankin Toro, na babban ofishin jami’an Toro da na ofishin Nabordo, tare da jami’an tsaro na yankin domin kai ɗauki ga lamarin.
“Rundunar haɗin gwiwa ta yi nasarar bin diddigin waɗanda ake zargin zuwa wajen ƙauyen tare da gudanar da aikin ƙwararru wanda ya kai ga ceto waɗanda lamarin ya rutsa da su.
Wakil ya ƙara da cewa, an kama wasu mutane shida da ake zargi da hannu a wannan lamarin.”
Waɗanda ake zargin sun haɗa da: Abubakar Usman da Adamu Alo da Abubakar Aliyu da Umar Habu da Abubakar Mamman Abubakar da kuma Shehu Samb.