Nijeriya Ta Samu Damar Karɓar Baƙuncin Taron Hulɗa Da Jama’a Na Duniya Na 2026
Published: 8th, March 2025 GMT
Ya bayyana cewa samun damar karɓar baƙuncin wannan babban taro wata gagarumar nasara ce ga Nijeriya, kasancewar ita ce ƙasar Afirka ta biyu da za ta karɓi baƙuncin taron.
Ya ce: “Wannan babban cigaba ne ga Nijeriya kuma yana da alaƙa da manufofin gwamnatin mu na inganta martabar ƙasar a idon duniya.
“Gwamnati za ta bayar da cikakken goyon baya don tabbatar da nasarar wannan taro.”
Ya kuma bayyana wata muhimmiyar nasara, inda ya ce Nijeriya ta samu damar karɓar baƙuncin Cibiyar UNESCO ta Mataki na Biyu kan Ilimin Kafofin Watsa Labarai da Bayani (MIL), wadda ita ce irin ta ta farko a Afrika.
Ya ce wannan matakin yana nuna irin girman tasirin da Nijeriya take samu a duniya.
Ya ce: “Hulɗa da jama’a tana da muhimmiyar rawa wajen gina ƙasa, bunƙasa dimokiraɗiyya, da inganta martabar Nijeriya a duniya.
“Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai tana da ecikakken niyyar yin aiki tare da duk masu ruwa da tsaki domin cimma wannan buri da kuma ba Nijeriya matsayi na jagora a fagen sadarwa na duniya.”
A nasa jawabin, Shugaban NIPR, Dakta Ike Neliaku, ya yaba wa ministan bisa ƙwazon da yake yi wajen inganta sarrafa bayanai da hulɗa da jama’a a ƙasar.
Ya ce: “Yanzu muna kallon sarrafa bayanai a matsayin hanyar sadarwa ta ɓangarori biyu, wato inda muke karɓar ra’ayoyi daga jama’a don su taimaka mana wajen tsara matakai na gaba.”
Dakta Neliaku ya kuma ba da sanarwar cewa Nijeriya za ta karɓi baƙuncin bikin cika shekaru 25 na ƙungiyar Global Alliance a shekarar 2026, wanda hakan zai ƙara tabbatar da matsayin ƙasar a matsayin jagaba a fagen hulɗa da jama’a a duniya.
Bugu da ƙari, ya sanar da ministan manyan shirye-shiryen da NIPR ta tsara na shekarar 2025, wanda suka haɗa da Makon Hulɗa da Jama’a na Nijeriya (NPR Week), Taron Ƙasa na Masu Magana da Yawu, da Taron Ƙasa kan Sarrafa Sunan Nijeriya.
Tawagar shugabannin NIPR ɗin ta haɗa da Mataimakin Shugaba, Farfesa Emmanuel Dandaura, da wasu manyan jami’ai, ciki har da Cif Yomi Badejo-Okusanya, Mohammed Kudu Abubakar, da Cif Uzoma Onyegbadue.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: karɓar baƙuncin
এছাড়াও পড়ুন:
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
Taron dandalin tattaunawa kan tattalin arzikin duniya na lokacin zafi na Davos, wanda aka gudana a tsakanin ranar 24 zuwa ranar 26 ga watan nan da muka ciki, a birnin Tianjin na kasar Sin, ya samu halartar wakilai kimanin 1800 daga kasashe da yankuna sama da 90, adadin da ya kai koli cikin tarihi. Kamar yadda babban daraktan dandalin Davos Borge Brende ya bayyana, “in muka duba yanayin kasashen duniya, za a gane cewa, wakilai a fannonin masana’antu da kasuwanci na kasashe da dama, suna fatan zuba jari a kasar Sin, tare da zurfafa hadin gwiwar cinikayya dake tsakaninsu da kasar Sin.”
A halin yanzu, kasuwannnin kasar Sin suna ci gaba da samun kyautatuwa da karuwa, lamarin da ya samar da damammaki ga bunkasar hadin gwiwar cinikayya a tsakanin kasa da kasa. Ci gaba da yin kirkire-kirkire a kasar Sin, ya samar da sabon karfi na neman samun bunkasa. A ciki kuma, bunkasar fasahar kwaikwayon tunanin dan Adam ta AI ta janyo hankulan jama’a cikin taron Davos. Masana na ganin cewa, idan muka yi amfani da fasahohin da abin ya shafa kan aikin nazarin sabbin kayayyaki, zai ninka saurin gudana da ayyukanmu sau 100 har ma zuwa sau 1000. Kuma kasar Sin za ta taka muhimmiyar rawa cikin wannan babban sauyi.
Haka kuma, cikin farkon watanni 5 na bana, an kafa sabbin kamfanoni masu jarin waje guda 24,018 a cikin kasar Sin, adadin da ya karu da kaso 10.4 bisa dari idan aka kwatanta da na makamancin lokacin bara. Kamfanonin kasashen duniya sun nuna fatansu na hada kai da kasar Sin. Kamar yadda tsohon firaministan kasar Burtaniya Tony Blair ya bayyana a yayin taron Davos cewa, “ya kamata a ci gaba da tuntubar kasar Sin a kai a kai.” (Mai Fassara: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp