Leadership News Hausa:
2025-11-03@08:56:20 GMT

‘Yan Majalisun Nijeriya: An Bar Jaki Ana Bugun Taiki!

Published: 7th, March 2025 GMT

‘Yan Majalisun Nijeriya: An Bar Jaki Ana Bugun Taiki!

Ya zama wajibi a tarihance cewa, a duk sa’adda aka tasamma furta asalin samuwar kunshin “yan majalisun taraiya a wannan kasa, a faro daga Jihar Legas, wadda ake yi wa take da “cunkus dakin tsumma, makarinki sai an dawo”. Kasantuwar, daga can ne suka samo asali.

Mai karatu ya fahimta cewa, wannan rubutu da alama zai ja zarensa ne har zuwa wani lokaci, cikin gabatar da mabanbantan bayanai game da “yan majalisunmu na Kasa, hada da na jihohi.

Fede irin karfin iko da tsarin mulkin Kasa ya ba su, tare da yin jinjina ga wasu cikin cokali daga cikinsu, sai kuma fyadar “ya”yan kadanya ga asarinsu, duba da irin burus da suka yi da kwamacalar shugabanni (shugaban kasa da gwamnoni) a kasa, duk da irin mummunan yanayi na tabarbarewar daukacin lamuran rayuwa da aka samu, musamman ga asarin jama’ar kasa da suke talakawa raunana!!!.

Cikin wannan rubutu, akwai yunkurin fakakar da al’umar kasa muhimmancin titse “yan majalisun, tare da neman suma, su titse gwamna da shugaban kasa, don rayuwar jama’ar mazabunsu su kyautata. Sabanin haka kuwa, zaben da suka yi musu, kwata-kwata bai yi wata rana ba. A rubutun, ana iya gabatar da wasu daga zakwakuran “yan majalisun (sai dai tsirari ne ainun), wadanda a aikace da baki, sun damu da ci gaban mutanensu, tare da yaba musu. Yabon da ya dace, ba yabo irin na banbadanci ba!!!.

 

Daga Tarihin Lagos Da Samuwar “Yan Majalisun Kasa, 1874 – 1886 – 1914

Tarihi ya tabbatar da cewa, cikin Shekarar 1861 ce yankin Lagos ya fada karkashin ikon Sarauniyar Ingila, ko ace Masarautar Birtaniya. Haka lamura suka ci gaba da gudana har zuwa tsakanin Shekarun 1874 zuwa 1886, inda aka nada gwamna, wanda shi ke da ikon tafiyar da harkokin mulki, a wuraren dake karkashin mulkin Turawan Birtaniya a kafatanin kasashen yammacin Afurka. Sai dai wannan gwamna, na zaune ne a can yankin kasar da a yanzu ake kiranta da Sierra Leone. Kasar da akasarinmu ke kira da Salo.

Kamar yadda aka fara 6incinawa, a Shekarar da aka hade yankin Kudanci da na Arewacin wannan kasa (1914) ne, Turawan Birtaniya suka kyankyashe wasu dokoki guda uku (3), wadanda guda daga dokokin ne ta tabbatar da ikon kirkirar kunshin “yan majalisu na farko a tarihin siyasar Nijeriyar da take amsa sunanta na Nijeriya a jiya da yau. Ga kunshin wadancan dokoki uku kamar haka;

i- “The Nigeria Council Order-in-Council (1910)”.

ii- “The Letters Patent (1913)”, sannan

iii- “The Nigeria Protectorate Order-in-Council (1913)” (Constitutional Conference Report, 1995: 43). Kunshin doka ta biyu, wato” The Nigeria Council Order-in-Council (1910)” ita ce ta samar da “yan majalisun farko a wannan kasa tamu. Sannu a hankali, za a faiyacewa mai karatu irin karfin iko ko akasinsa, da wannan zaure na “yan majalisun ke da shi, a jiya da yau.

 

Dalilan Kirkirar “Yan Majalisun

Kamar yadda a baya aka fadi cewa, a farkon lamari, yankin gundumar Lagos ne kadai ke da kunshin “yan majalisu, gabanin hade kudanci da arewacin kasar, tare da rada masa sunan Nijeriya. Yayin da aka hade Kasar zuwa ga wani abu guda, ta tabbata a zahiri cewa, wancan kunshin tsaffin “yan majalisun Lagos na farko, taraiyar kasar sun yi musu dangangan, ko ace girma, wajen iya tafiyar da lamuranta baki daya. Wannan dalili, ya jaza kirkirar kunshin “yan majalisun, wadanda wakilcinsu zai ratsa ne zuwa ga sasannin kudanci da kuma na arewacin kasar. Dalili na biyu da ya bukatar da kafa “yan majalisun shi ne, ta tabbata cewa, muddin gwamna da gwamnatin Birtaniya ta samar da shi, karkashin kunshin dokar “The Letters Patent (1913)” na da muradin jin ra’ayoyin jama’ar kudanci da na arewacin Kasar da aka hade waje guda baki daya, to fa babu makawa, sai an samar da gungun “yan majalisun a duka bangarori biyu na kasar. A karkashin doka ta bai daya a kasa da aka samar, wadannan ne “yan majalisa na farko, wanda adadinsu ya riski mutum talatin da shida ne cifcif (36). Sai dai, shida (6) kacal daga cikinsu ne jama’ar Nijeriya ke da ikon zabowa, don wakiltar bangarorinsu (Fagge & Alabi, 2007: 53-54).

Yana da kyau mai karatu ya sani cewa, an mirgina matakai da yanayai iri daban-daban, gabanin “yan majalisun na jihohi da na tarayya musamman, su sami kaiwa ga mamakon ikon da suka riska a yau. Sai dai, shin, riskar ikon nasu a yau, yana yin tasiri mai kyau ga ci gaban jama’ar kasa ne koko a’a?. Cikin bayanai da za a kutsa can gaba, duk dan Nijeriya akili kuma managarci, zai kai ga fahimtar cikakkiyar amsar wannan tambaya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: yan majalisun

এছাড়াও পড়ুন:

Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai

Idan ka duba tarihin duniya gabadaya da tarihin annabawa, tarihi ne na wayewar duniya tun daga Annabi Nuhu (S.A.) har zuwa Manzon Allah (S.A.W.) kamar duniya tana ‘yar makaranta ce ta fara da Nazare, ta zo Firamare zuwa Sakandire har zuwa Jami’a, sannan aka yaye ta, yanzu da zuwan Manzon Allah an yaye duniya, yanzu duniya ba ta bukatar sai an aiko annabi, ba ta bukata sai an aiko ma’aiki, a’a wanna abu da Manzon Allah ya zo da shi za mu iya kafa dalili da shi mu shirya kanmu ba sai da annabi ba.

Wannan abu da Manzon Allah ya zo da shi yanzu ya kafa dalili da shi, da shi muka karantar da kanmu ba sai da Annabi ba, wannan abu da ya zo da shi za mu iya aiki da shi mu zauna lafiya, mu haramta abin da Allah Ya haramta. Yanzu kamar an yaye mu ne daga Jami’a tun daga jami’a tun daga zamanin Annabi Nuhu (A.S.) har ya zuwa Annabi Muhammadu (S.A.W.). idan ka faro duniya daga farkon ma’aika, duniya ta faro ne daga sanin wuta wato yadda za a yi amfani da wuta. Dan adam na farko ya ji tsoron wuta wasu sun tafi a kan cewa farkon abin da Dan Adam ya fara bautawa shine wuta, wanda ita ta fara ba shi tsoro ba wai ya iya kunnawa ba amma ya ga daki ya kama da wuta, dubi irin zamanin nan duk da motocin kashe gobara haka daji zai kama da wuta ta gagare su balle ka koma zamani da shekara miliyan kaza wanda dan Adam bai ma santa ba sai dai ya ga daki ya kama da wuta (wata ay ana cewa) “Allahn da ya sa muku wuta a ciki koren ganye ko koriyar bishiya”, malamai na cewa bishiya mai yado wanda ake kunna wuta, toh wannan abu ne ya sa idan wuta ta kama aka kasa shawo kanta sai mutane su tsorata su ce wai meye wannan, meye ya kunna wannan wutar? Suka ga to lallai wannan duniyar da suke ciki akwai wani abu a boye, gwara su bauta wa abin nan na boye fa, don ya kiyaye su daga wanna wutar har suka fara bauta mata da yanka dabbbobi don ta kiyaye su, gaba daya dai har ta soma gasa wasu abubuwa na dabbobi, idan wutar ta mutu suka zo wurin su ji kamshin ya bambanta, idan sun sa a baki su ji dadinsu ya banbanta. Toh tana daya daga cikin abin da ta koya wa dan Adam wayewa.

Da dan Adam ya waye, wuta tana daya daga cikin abin da ya wayar da dan Adam kuma idan ka lura yau wuta ita ke biye da mu duk wasu kere-kere za ka ga daga wuta ne, abin da muke tsoro kuma shi ne babban abin amfani, toh a haka dai dan Adam har ya iya kera wutar da kansa. Kamar yadda Allah ya fada mana cikin ‘ya’yan Adam da daya ya kashe daya ya rasa yadda zai yi, a haka ne har dan Adam ya san yadda zai binne dan’uwansa har zuwa zamanin Annabi Idirisu sama ta soma magana da kasa, Allah ya soma aiko ma dan Adam da mala’ika, su ne wadannan mutane da muke cewa ko akwai su a duniyar wata ko mutanen sama, Turawa duk sun rubuta wannan abu, sun zana wannan abu sai ga shi irin wannan jirage ne wanda ake cewa na duniyar sama, daya daga ciki Annabi Sha’ayahu yake cewa ga wani abu ya sauko kasa mai kara iri kaza.

Tun daga zamanin Annabi Idris mala’iku ne suka kawo sako suke yin magana da mutanen kasa, su ake cewa tatsuniyoyi na duk al’umma, tatsuniya ne a wajenmu amma su gaske ne a wajensu, su ce mutane sun sauko musu daga sama, har aka zo zamanin Annabi Nuhu ya tabbatar, da ya zo ya fada wa mutane suka ce ba su yarda ba, ba mu ji wannan wajen iyayenmu ba, haka aka ci gaba har zuwa zamanin Annabi Hudu dan Adam ya fara hore dabbobi, dabbar da dan Adam ya fara horewa shi ne kare, kuma ya hore dabbobin da zai ci, zai iya gane wannan dabbar ba zai ci ba wannan zai ci, wannan zai iya zama da ita lafiya, wannan ba zai iya zama da ita ba, daga nan dan Adam ya fara gini, ya dan kwakule kasa ya yi kogo ya shiga.

Har ya zuwa Annabi Salihu, har dan Adam ya fara fahimtar wannan kwayar da take fitowa a kasa, wannan zan iya ci in rayu, wannan kwayar kuma ba a cin ta, har ya soma tunanin toh wannan kwayar ya zan ajiye ta zuwa nan gaba in sake shuka ta, haka dan Adam har ya soma yin noma a aikace don ya rayu. Allah ya gaya mana wannan yana daga cikin ayoyin Allah (kamar yadda ya zo a aya) “arziki yana daga cikin kasa da abin da kasa take tsirarwa da abin da hannunka yake aikatawa” kamar sana’a ko noma ko nema. Toh ka ga a nan babu zancen ka ce ba za ka yi nema ba, duk abin da kake nema idan ka juya kasa za ka same shi, duka kasar da ta rike noma da sana’a za ku ga sun fi arziki, Allah ga shi ya gaya mana idan kafiri ya fi ka arziki sai dai ka nema a wajensa, don haka mu dogara da Allah shi ke azurtawa, ga ka’idoji nan ya fada mana, nema, kiwo abubuwa duk gabaki daya.

Za mu ci gaba a mako mai zuwa in sha Allahu.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP October 31, 2025 Manyan Labarai Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta October 31, 2025 Manyan Labarai Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi? October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai