Leadership News Hausa:
2025-08-01@15:19:08 GMT

‘Yan Majalisun Nijeriya: An Bar Jaki Ana Bugun Taiki!

Published: 7th, March 2025 GMT

‘Yan Majalisun Nijeriya: An Bar Jaki Ana Bugun Taiki!

Ya zama wajibi a tarihance cewa, a duk sa’adda aka tasamma furta asalin samuwar kunshin “yan majalisun taraiya a wannan kasa, a faro daga Jihar Legas, wadda ake yi wa take da “cunkus dakin tsumma, makarinki sai an dawo”. Kasantuwar, daga can ne suka samo asali.

Mai karatu ya fahimta cewa, wannan rubutu da alama zai ja zarensa ne har zuwa wani lokaci, cikin gabatar da mabanbantan bayanai game da “yan majalisunmu na Kasa, hada da na jihohi.

Fede irin karfin iko da tsarin mulkin Kasa ya ba su, tare da yin jinjina ga wasu cikin cokali daga cikinsu, sai kuma fyadar “ya”yan kadanya ga asarinsu, duba da irin burus da suka yi da kwamacalar shugabanni (shugaban kasa da gwamnoni) a kasa, duk da irin mummunan yanayi na tabarbarewar daukacin lamuran rayuwa da aka samu, musamman ga asarin jama’ar kasa da suke talakawa raunana!!!.

Cikin wannan rubutu, akwai yunkurin fakakar da al’umar kasa muhimmancin titse “yan majalisun, tare da neman suma, su titse gwamna da shugaban kasa, don rayuwar jama’ar mazabunsu su kyautata. Sabanin haka kuwa, zaben da suka yi musu, kwata-kwata bai yi wata rana ba. A rubutun, ana iya gabatar da wasu daga zakwakuran “yan majalisun (sai dai tsirari ne ainun), wadanda a aikace da baki, sun damu da ci gaban mutanensu, tare da yaba musu. Yabon da ya dace, ba yabo irin na banbadanci ba!!!.

 

Daga Tarihin Lagos Da Samuwar “Yan Majalisun Kasa, 1874 – 1886 – 1914

Tarihi ya tabbatar da cewa, cikin Shekarar 1861 ce yankin Lagos ya fada karkashin ikon Sarauniyar Ingila, ko ace Masarautar Birtaniya. Haka lamura suka ci gaba da gudana har zuwa tsakanin Shekarun 1874 zuwa 1886, inda aka nada gwamna, wanda shi ke da ikon tafiyar da harkokin mulki, a wuraren dake karkashin mulkin Turawan Birtaniya a kafatanin kasashen yammacin Afurka. Sai dai wannan gwamna, na zaune ne a can yankin kasar da a yanzu ake kiranta da Sierra Leone. Kasar da akasarinmu ke kira da Salo.

Kamar yadda aka fara 6incinawa, a Shekarar da aka hade yankin Kudanci da na Arewacin wannan kasa (1914) ne, Turawan Birtaniya suka kyankyashe wasu dokoki guda uku (3), wadanda guda daga dokokin ne ta tabbatar da ikon kirkirar kunshin “yan majalisu na farko a tarihin siyasar Nijeriyar da take amsa sunanta na Nijeriya a jiya da yau. Ga kunshin wadancan dokoki uku kamar haka;

i- “The Nigeria Council Order-in-Council (1910)”.

ii- “The Letters Patent (1913)”, sannan

iii- “The Nigeria Protectorate Order-in-Council (1913)” (Constitutional Conference Report, 1995: 43). Kunshin doka ta biyu, wato” The Nigeria Council Order-in-Council (1910)” ita ce ta samar da “yan majalisun farko a wannan kasa tamu. Sannu a hankali, za a faiyacewa mai karatu irin karfin iko ko akasinsa, da wannan zaure na “yan majalisun ke da shi, a jiya da yau.

 

Dalilan Kirkirar “Yan Majalisun

Kamar yadda a baya aka fadi cewa, a farkon lamari, yankin gundumar Lagos ne kadai ke da kunshin “yan majalisu, gabanin hade kudanci da arewacin kasar, tare da rada masa sunan Nijeriya. Yayin da aka hade Kasar zuwa ga wani abu guda, ta tabbata a zahiri cewa, wancan kunshin tsaffin “yan majalisun Lagos na farko, taraiyar kasar sun yi musu dangangan, ko ace girma, wajen iya tafiyar da lamuranta baki daya. Wannan dalili, ya jaza kirkirar kunshin “yan majalisun, wadanda wakilcinsu zai ratsa ne zuwa ga sasannin kudanci da kuma na arewacin kasar. Dalili na biyu da ya bukatar da kafa “yan majalisun shi ne, ta tabbata cewa, muddin gwamna da gwamnatin Birtaniya ta samar da shi, karkashin kunshin dokar “The Letters Patent (1913)” na da muradin jin ra’ayoyin jama’ar kudanci da na arewacin Kasar da aka hade waje guda baki daya, to fa babu makawa, sai an samar da gungun “yan majalisun a duka bangarori biyu na kasar. A karkashin doka ta bai daya a kasa da aka samar, wadannan ne “yan majalisa na farko, wanda adadinsu ya riski mutum talatin da shida ne cifcif (36). Sai dai, shida (6) kacal daga cikinsu ne jama’ar Nijeriya ke da ikon zabowa, don wakiltar bangarorinsu (Fagge & Alabi, 2007: 53-54).

Yana da kyau mai karatu ya sani cewa, an mirgina matakai da yanayai iri daban-daban, gabanin “yan majalisun na jihohi da na tarayya musamman, su sami kaiwa ga mamakon ikon da suka riska a yau. Sai dai, shin, riskar ikon nasu a yau, yana yin tasiri mai kyau ga ci gaban jama’ar kasa ne koko a’a?. Cikin bayanai da za a kutsa can gaba, duk dan Nijeriya akili kuma managarci, zai kai ga fahimtar cikakkiyar amsar wannan tambaya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: yan majalisun

এছাড়াও পড়ুন:

2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC

Abdullahi ya ce tun kafin a kafa haɗakar, wasu sun riga sun fara yaɗa cewa an shirya ta ne domin Atiku.

Ya ƙara da cewa: “Ni ina da shekara 56, wa ya ce ba zan iya tsayawa takarar shugaban ƙasa ba?”

Da aka tambaye shi game da Peter Obi, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP, Abdullahi ya ce Obi na cikin haɗakar har yanzu.

Amma ya ce bai zama cikakken ɗan jam’iyyar ADC ba har yanzu.

Ya bayyana cewa jam’iyyar ADC ta bai wa Obi da kuma tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, dama su fice daga jam’iyyunsu na yanzu wato LP da SDP.

Ya kuma ce Obi ba zai koma jam’iyyar PDP ba, duk da cewa jam’iyyar tana ƙoƙarin jawo ‘yan siyasa domin dawo da ƙarfinta.

Da aka tambaye shi dalilin da ya sa ‘yan Nijeriya za su yadda da jam’iyyarsu, Abdullahi ya ce jam’iyyar APC da ke mulki ta yi alƙawarin kawo sauyi amma ta gaza.

Don haka, ya ce lokaci ya yi da ‘yan Nijeriya za su gwada wata sabuwar tafiyar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ya Kamata A Sake Yi Wa Tsarin Ɗaukar Kuratan Ƴansanda Garanbawul
  • NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi?
  • 2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC
  • Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila
  • Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang