‘Yan Majalisun Nijeriya: An Bar Jaki Ana Bugun Taiki!
Published: 7th, March 2025 GMT
Ya zama wajibi a tarihance cewa, a duk sa’adda aka tasamma furta asalin samuwar kunshin “yan majalisun taraiya a wannan kasa, a faro daga Jihar Legas, wadda ake yi wa take da “cunkus dakin tsumma, makarinki sai an dawo”. Kasantuwar, daga can ne suka samo asali.
Mai karatu ya fahimta cewa, wannan rubutu da alama zai ja zarensa ne har zuwa wani lokaci, cikin gabatar da mabanbantan bayanai game da “yan majalisunmu na Kasa, hada da na jihohi.
Cikin wannan rubutu, akwai yunkurin fakakar da al’umar kasa muhimmancin titse “yan majalisun, tare da neman suma, su titse gwamna da shugaban kasa, don rayuwar jama’ar mazabunsu su kyautata. Sabanin haka kuwa, zaben da suka yi musu, kwata-kwata bai yi wata rana ba. A rubutun, ana iya gabatar da wasu daga zakwakuran “yan majalisun (sai dai tsirari ne ainun), wadanda a aikace da baki, sun damu da ci gaban mutanensu, tare da yaba musu. Yabon da ya dace, ba yabo irin na banbadanci ba!!!.
Daga Tarihin Lagos Da Samuwar “Yan Majalisun Kasa, 1874 – 1886 – 1914
Tarihi ya tabbatar da cewa, cikin Shekarar 1861 ce yankin Lagos ya fada karkashin ikon Sarauniyar Ingila, ko ace Masarautar Birtaniya. Haka lamura suka ci gaba da gudana har zuwa tsakanin Shekarun 1874 zuwa 1886, inda aka nada gwamna, wanda shi ke da ikon tafiyar da harkokin mulki, a wuraren dake karkashin mulkin Turawan Birtaniya a kafatanin kasashen yammacin Afurka. Sai dai wannan gwamna, na zaune ne a can yankin kasar da a yanzu ake kiranta da Sierra Leone. Kasar da akasarinmu ke kira da Salo.
Kamar yadda aka fara 6incinawa, a Shekarar da aka hade yankin Kudanci da na Arewacin wannan kasa (1914) ne, Turawan Birtaniya suka kyankyashe wasu dokoki guda uku (3), wadanda guda daga dokokin ne ta tabbatar da ikon kirkirar kunshin “yan majalisu na farko a tarihin siyasar Nijeriyar da take amsa sunanta na Nijeriya a jiya da yau. Ga kunshin wadancan dokoki uku kamar haka;
i- “The Nigeria Council Order-in-Council (1910)”.
ii- “The Letters Patent (1913)”, sannan
iii- “The Nigeria Protectorate Order-in-Council (1913)” (Constitutional Conference Report, 1995: 43). Kunshin doka ta biyu, wato” The Nigeria Council Order-in-Council (1910)” ita ce ta samar da “yan majalisun farko a wannan kasa tamu. Sannu a hankali, za a faiyacewa mai karatu irin karfin iko ko akasinsa, da wannan zaure na “yan majalisun ke da shi, a jiya da yau.
Dalilan Kirkirar “Yan Majalisun
Kamar yadda a baya aka fadi cewa, a farkon lamari, yankin gundumar Lagos ne kadai ke da kunshin “yan majalisu, gabanin hade kudanci da arewacin kasar, tare da rada masa sunan Nijeriya. Yayin da aka hade Kasar zuwa ga wani abu guda, ta tabbata a zahiri cewa, wancan kunshin tsaffin “yan majalisun Lagos na farko, taraiyar kasar sun yi musu dangangan, ko ace girma, wajen iya tafiyar da lamuranta baki daya. Wannan dalili, ya jaza kirkirar kunshin “yan majalisun, wadanda wakilcinsu zai ratsa ne zuwa ga sasannin kudanci da kuma na arewacin kasar. Dalili na biyu da ya bukatar da kafa “yan majalisun shi ne, ta tabbata cewa, muddin gwamna da gwamnatin Birtaniya ta samar da shi, karkashin kunshin dokar “The Letters Patent (1913)” na da muradin jin ra’ayoyin jama’ar kudanci da na arewacin Kasar da aka hade waje guda baki daya, to fa babu makawa, sai an samar da gungun “yan majalisun a duka bangarori biyu na kasar. A karkashin doka ta bai daya a kasa da aka samar, wadannan ne “yan majalisa na farko, wanda adadinsu ya riski mutum talatin da shida ne cifcif (36). Sai dai, shida (6) kacal daga cikinsu ne jama’ar Nijeriya ke da ikon zabowa, don wakiltar bangarorinsu (Fagge & Alabi, 2007: 53-54).
Yana da kyau mai karatu ya sani cewa, an mirgina matakai da yanayai iri daban-daban, gabanin “yan majalisun na jihohi da na tarayya musamman, su sami kaiwa ga mamakon ikon da suka riska a yau. Sai dai, shin, riskar ikon nasu a yau, yana yin tasiri mai kyau ga ci gaban jama’ar kasa ne koko a’a?. Cikin bayanai da za a kutsa can gaba, duk dan Nijeriya akili kuma managarci, zai kai ga fahimtar cikakkiyar amsar wannan tambaya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: yan majalisun
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
Hukumar Fensho ta Jihar Jigawa da Kananan Hukumomin jihar ta shirya fara aikin tantance ‘yan fansho da ke cikin tsarin.
Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, Alhaji Muhammad K. Dagaceri ne ya bayyana haka yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Gidan Fansho, inda shugabannin kungiyar ‘Yan Fansho ta Najeriya reshen Jigawa suka halarta.
A cewarsa, an shirya fara aikin tantancewar ne daga ranar Litinin, 5 ga Mayu, 2025.
Alhaji Dagaceri ya bayyana cewa, an shirya hakan ne da nufin sabunta tsarin biyan fansho tare da tabbatar da ingancin bayanai.
Ya ce, aikin tantancewar zai gyara wasu ‘yan kura-kurai da suka kunno kai a cikin shekaru uku da suka gabata, da kuma tabbatar da ingantattun bayanai a jadawalin biyan fansho.
Ya kara da cewa, wannan yunkuri ya yi daidai da kudirin jihar gwamnati na tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkokin mulki, tare da bai wa ‘yan fansho dama su gyara duk wani bayanin da bai cika ba a takardunsu.
Shi ma da ya ke jawabi, Akanta Janar na Jihar, Alhaji Abdullahi S.G. Shehu, ya jaddada cewa aikin tantancewar zai bai wa ‘yan fansho damar sabunta bayanansu da suka bace ko suka canza a takardunsu.
Saboda haka, ya bukaci dukkan ‘yan fansho daga ma’aikatun gwamnati, sassan hukumomi, kananan hukumomi da kuma hukumomin ilimi na kananan hukumomi da su halarci tantancewar a ranar da aka tsara kamar yadda yake cikin jadawalin aikin.
A jawabinsa, Shugaban kungiyar kananan hukumomi ALGON ta Jihar Jigawa, Farfesa Salim Abdurrahman, ya tabbatar da cikakken goyon baya daga shugabannin kananan hukumomi 27 domin cimma burin aikin.
Shugaban na ALGON wanda shugaban karamar hukumar Malam Madori, Alhaji Salisu Sani ya wakilta, ya bukaci ‘yan fanshon da su ba da cikakken haɗin kai don samun nasarar shirin.
Shi ma Shugaban hukumar, Dr. Bilyaminu Shitu Aminu, ya bukaci ‘yan fansho daga sassa daban-daban da su ba da hadin kai domin cimma burin da aka sanya, tare da jaddada cewa su ziyarci sakatariyar kananan hukumominsu domin a tantance su.
Shugaban Kungiyar ‘Yan Fansho ta Najeriya reshen Jihar Jigawa, Alhaji Umar Sani Babura, ya yi alkawarin cewa kungiyar za ta bada cikakken goyon baya domin nasarar wannan shiri.
Dukkan ‘yan fansho daga Ma’aikatun Gwamnati, Kananan Hukumomi, da Hukumomin Ilimi na Kananan Hukumomi da ke cikin tsarin fanshon, ya zama wajibi su halarci wannan tantancewa a ranakun da aka tsara a jadawalin aikin.
Usman Muhammad Zaria