An Bukaci ‘Yan Su Matsa Kaimi Har Sai Anbiya su Hakokinsu
Published: 7th, March 2025 GMT
An Bukaci ‘yan fansho suyi gangami ganin jinkirin da ake samu wajen biyan su kudaden su.
An shawarci kungiyar ’yan fansho ta tarayya da ta zaburar da mambobinta kan jinkirin rage basussukan da gwamnatin tarayya ta amince da su.
Jami’in hulda da jama’a na kungiyar ’yan fansho na Jami’ar Ahmadu Bello Zariya, Alhaji Muhammad Mamman, ya bayar da wannan shawarar a matsayin martani ga rahotannin da ke cewa an dakatar da zanga-zangar da ake shirin yi kan lamarin, biyo bayan rokon da PTAD ta yi na a ba da damar tattaunawa.
Alhaji Muhammad Mamman wanda ya bayyana goyon bayansa ga tattaunawa da wa’adin makonni hudu da hukumar NIPOST reshen kungiyar ‘yan fansho ta kasa ta bayar ya ba da shawarar fadada taron kungiyoyin domin ganin an warware matsalolin da aka samu wajen biyan basussukan da ake bin su.
Ya ji takaicin yadda duk da alkawuran da hukumar ta yi na biyan kudaden alawus-alawus din, har yanzu wadanda suka yi ritaya ba su samu kudaden da kungiyoyin da abin ya shafa suka amince da su ba.
Alhaji Muhammad Mamman ya jaddada bukatar kungiyoyin su kai kara ga Majalisar Dokoki ta kasa, EFCC da ICPC idan har aka kasa cimma matsayar tattaunawa kan lamarin duba da yadda ake zargin karkatar da kudaden fansho a baya ba tare da isassun hukumcin da zai kawo gyara ga lamarin ba.
COV/ SULEIMAN KAURA
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa
dimokuradiyya ta hanyar ba da umarni ga manyan wadanda ya nada na arewa su halarci taron.
“Wannan aiki daya na sadaukarwar da shugaban kasa ya yi don tattaunawa da mutane
Yana ishara da cewa, ba wai isa ce kadai a kan iya siyasa ba har ma da isa matuka wajen mutunta ka’idojin dimokuradiyya.
Mahalarta taron sun hada da; Sakataren Gwamnati na Tarayya, Sanata George Akume, Mai Ba Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Tsaro Malam Nuhu Ribadu, Babban Hafsan Hafsoshin Tsaro Janar Christopher Musa, Hafsan Hafsan Sojin Sama Hassan Bala, Kwamanda Janar na NSCDC Dr. Ahmed Abubakar Audi, Shugaban Gwamnonin Arewa, Mai Girma Gwamna Inuwa Yahaya, Mai Girma Gwamnan Jihar Kwara Da Shugaban Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Hon. Abdulrazak Abdulrahman, Wanda Ya Wakilci Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu GCFR duk hallara a wurin taron. Sauran sun hada da Mashawarciya ta Musamman ga shugaban kasa akan harkokin siyasa, Hadiza Bala Usman, da sauran shugabani da hukumomi daga yankin.
Cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kodinentan UADD Kwamared Jamil Bala Muhammad, ta ce, zaman tattaunawa ya bai wa Arewa damar yin tunani akan ayyukan gwamnatin Tinubu da kuma gabatar da ra’ayoyi na gaskiya.
Kazalika, UADD ta yaba wa Babban Darakta Janar na tunawa da Sir Ahmadu Bello Foundation, Engr. Abubakar Gambo Umar bisa hangen nesa da jajircewar sa. In ji sanarwar.
Manyan abubuwan da aka mayar da hankali kansu sun hada da yabon gwamnatin Tinubu kan nasarori da kokarin da ta yi a bayyane don cika alkawuran da aka dauka yayin yakin nenam zave, musamman a harkokin tsaro da sake fasalin tattalin arziki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp