Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-27@16:08:50 GMT

An Bukaci ‘Yan Su Matsa Kaimi Har Sai Anbiya su Hakokinsu

Published: 7th, March 2025 GMT

An Bukaci ‘Yan Su Matsa Kaimi Har Sai Anbiya su Hakokinsu

An Bukaci ‘yan fansho suyi gangami ganin jinkirin da ake samu wajen biyan su kudaden su.

An shawarci kungiyar ’yan fansho ta tarayya da ta zaburar da mambobinta kan jinkirin rage basussukan da gwamnatin tarayya ta amince da su.

Jami’in hulda da jama’a na kungiyar ’yan fansho na Jami’ar Ahmadu Bello Zariya, Alhaji Muhammad Mamman, ya bayar da wannan shawarar a matsayin martani ga rahotannin da ke cewa an dakatar da zanga-zangar da ake shirin yi kan lamarin, biyo bayan rokon da PTAD ta yi na a ba da damar tattaunawa.

Alhaji Muhammad Mamman wanda ya bayyana goyon bayansa ga tattaunawa da wa’adin makonni hudu da hukumar NIPOST reshen kungiyar ‘yan fansho ta kasa ta bayar ya ba da shawarar fadada taron kungiyoyin domin ganin an warware matsalolin da aka samu wajen biyan basussukan da ake bin su.

Ya ji takaicin yadda duk da alkawuran da hukumar ta yi na biyan kudaden alawus-alawus din, har yanzu wadanda suka yi ritaya ba su samu kudaden da kungiyoyin da abin ya shafa suka amince da su ba.

Alhaji Muhammad Mamman ya jaddada bukatar kungiyoyin su kai kara ga Majalisar Dokoki ta kasa, EFCC da ICPC idan har aka kasa cimma matsayar tattaunawa kan lamarin duba da yadda ake zargin karkatar da kudaden fansho a baya ba tare da isassun hukumcin da zai kawo gyara ga lamarin ba.

COV/ SULEIMAN KAURA

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kashe ‘yan fashi da ƙwato makamai a Kaduna

An harbe wasu mutum biyu da ake zargin ’yan fashi da makami ne a ranar Talata a yayin wani artabu da jami’an tsaro suka yi a unguwar Makera da ke Kakuri a Jihar Kaduna.

Rundunar ta kuma kama wasu mutane biyu da ake zargin tare da ƙwato tarin makamai da kayayyaki masu daraja da aka sace daga mazauna garin.

An tallafawa iyalan ’yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno Yadda aka kama mai garkuwa da mutane yana tsaka da cin kasuwar shanu a Neja

A cewar kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, lamarin ya fara ne da misalin ƙarfe 3:10 na tsakar dare, inda wasu ’yan bindiga 8 suka kai hari a rukunin gidaje na Estate Gashash da ke Barnawa.

Rahotanni sun bayyana cewa, waɗanda ake zargin ɗauke da bindiga ƙirar gida da kuma wasu muggan makamai, an yi zargin sun yi wa mazauna yankin fashin wayoyin salula da kwamfutar tafi-da-gidanka, da agogunan hannu da na’urorin wasanni da sarƙoƙin masu daraja.

Da aka samu kiran gaggawar, babban jami’in ’yan sanda na Barnawa (DPO), tare da haɗin gwiwar DPO na sashen Kakuri da Sabon Tasha, da kuma jami’an runduna ta 312 na Artillery Regiment Kalapanzi, suka garzaya wurin da lamarin ya faru cikin gaggawa.

Daga baya an bi sawun waɗanda ake zargin har zuwa hanyar Makera, inda aka yi artabu da muggan makamai.

“A fafatawar ne aka kashe biyu daga cikin ’yan fashi da makami, yayin da aka kama wasu biyu,” in ji DSP Hassan.

Ya ce, ana ci gaba da ƙoƙarin kamo sauran ’yan fashin da suka tsere daga yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
  • Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP
  • Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji
  • ’Yan sanda sun kashe ‘yan fashi da ƙwato makamai a Kaduna
  • An tallafawa iyalan ‘yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno
  • ’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe
  • Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya
  • Gwamnatin Gombe za ta biya ’yan fansho Naira biliyan 6.6 kuɗin ritaya
  • Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa
  • Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — Trump